← Book details Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 74 OF 145

Sashe 74

Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

"Aaann gamaaa ku jiraniiiii" boka yana rufe baki ya soma juya 'kwala-'kwalan idanuwansa kamar yadda yake juya idonsa👀 haka 'kwaryar gabansa ma take juyi yana yi yana yayyafa wani abu ciki yana kiran sunan Malam Habu da Sadi zuwan can sai gani sukai faaaaa💥💥wuta ta kama a cikin 'kwaryar hhhhh hahaha hihihihih hhhhhhhhhhh haka boka ya cika musu kunne da 'kara zuwa wani lokaci yai shiru yana kallon su yace.

"Shikenannnn aikinnku yaaa kammalaaa saura biyaannn bukataaa kamarr yaddaa wannan 'kwarya ta 'kone hakaa arzikinn suu zaii 'konee ammaa badaa wutaa baa zann turaa aljanii Shahirgiii ya d'ebee kud'inn suu tashii basuu daa koo siisii dagaa suu saii kayann jikinsuu hakan yayi muku"?.

Kallon juna Tanko da Mudi sukai suna fashewa da dariyar mugunta Tanko daya kasa tsayawa yace "kwarai boka tabbas haka yayi wannan zai faranta min raina shakka babu boka na yarda da tsarin aikinka mai kyau ne shikenan zamu tafi boka saimun sake dawowa da babbar kyauta idan muka ga malam Habu ya dawo a firgice kuma a talauce kamar yadda ya tafi jiya iyau".

"Hhhh karrku damuuu kunn samuuu mazaaa a fitaaa daga nan da sauriii ku d'age 'kafa d'aya da tsalle babu waiwayeee idan kuka juyo abinda zai sameshi zai dawoo kankuu kujeee naceeeeeee🙊".

Ba arziki da sauri suka tashi jiki na rawa kowa ya d'age 'kafa d'aya suka bar gurin suna tafe suna tsalle kamar kwad'i sun ji'ke da gumi shir'bim sai sauke numfashi suke da'kyar suka karaso bakin wata 'yar siririyar hanya dake dajin sai a gurin dole suka zauna idan sun dawo daidai numfashin su ya tsirga sa tashi su tafi kallon gabas yamma kudu da arewa Tanko yai yana cewa.

"Kaii ah kaii sai yanzu naji dad'i d'an bala'i haba malam idan nabar malam Habu ya dawo da arzikin sa irin nada ai bazan iya rayuwa ba tsabar ba'kin ciki takaici ne zai kasheni saidai a wayi gari nayi bunga😂 wallahi"

Dariya Mudi yai yana cewa "balle kuma ni inaga nafi jin haushin sa akanka"?.

Zaro ido Tanko yai "inji ubanwa kafini tabbbbb kasan yadda nake son ganin karshen Malam Habu kuwa hummm abun bazai dad'i ba idan na tsaya yi maka bayani zai kaimu tsawon shekara guda ban gama fad'a maka ba so nake kafin ya mutu ya dandani azababbiyar azaba ya tagayyara ya zama abin tausayi da abin kwatance idan ya mutu babu wanda zaije kan gawarsa balle a samu wanda zaice aimai wanka har akaishi kabari inaaa wallahi bazan bari ba malam Habu! Malam Habu!! Hummm zaka ga tashin hankali da damuwa a gabanka talauci zaita bibiyar jininka har abada kuma nayi alkawari bazan ta'ba bari ko d'aya cikin 'ya'yanka tayi aure ba musamman ma wannan yarinyar" tsayawa yai yana kallon mudi yace "meye ma sunanta Mudi"?.

Dariya Mudi yai yana cewa "sunan gyatumarsa yasa Hauwa'u suke ce mata Amatullahi shi kuma yana ce mata mamarsa".

Tsaki Tanko yai "to ko uban mamarsa ce tunda yafi sonta itama saitaga bala'i iri iri sai na hanasu zaman lafiya" ya karasa maganar yana kallon Mudi wanda ya zuba masa ido kafin yace.

"Meye"?.

Kai Mudi ya kad'a yana cewa "babu komai tashi mu tafi na gaji mubar dajin nan" mi'kewa Tanko yai yana cewa "muje to ai yanzu hankalina ya kwanta bani da matsala sai jiran yadda zanga Malam Habu ya dawo garin nan a gigice kamar an koro shi ranar zanyi dariya a majalisarmu na buga 'kafa nayi shewa inta kama na mi'ke na taka rawa kaidai humm a rufe da buzu wai matar Malam tayi cikin shege bari kawai muje dai" Mudi dai bai sake magana ba suka cigaba da tafiya iya muryar Tanko ce ke tashi a dajin wanda ya kasance shiru babu motsin komai koda ganyen bishiya.

CAMEROON
Cameroon Douala zaune su Malam Habu suke a kofar gate d'in kofar gidan Alhaji Idrisu suna zance dama kuma baya gari kamar daga sama suka ga motarsa ta nufi kofar gidan da sauri malam Habu ya tashi yana bud'e masa gate d'in yana karasowa ya tsaya yana kashe motar ya sauke glass d'an le'kowa yai da fara'a a fuskarsa yace.

"Sannunku da kokari yaya kuke"?.

Suma fuskarsu da annuri suka gaida shi kallonsu ya sakeyi yana cewa "ok Malam Habubakar fatan ba wata matsala"?.

Kai Malam Habu ya d'aga cikin yabawa da halayyar Alhaji Idrisu na kula da wanda yake karkashin sa yace "eh Alhaji babu wani abu muna lafiya" saidai mutane da dama sunzo nemanka d'azun ma wani mutum yabar nan".

"Ok bai fad'a muku sunansa ba"?.

"Eh bai fad'a ba kawai dai ya d'an dad'e sannan ya mi'ke ya tafi amma yace zuwa dare zai sake dawowa".

"Ok shikenan zan shiga gida idan ya dawo ka min magana".

"To Alhaji insha Allahu a fito lafiya".

Tada motar yai yana karasa wucewa ciki kafin Malam Habu yaja gate ya rufe yana zama tsaye simm yaga anzo anyi a kansa yana d'agowa yaga yaron Alhaji Idrisu ne malam komai da ruwanka da mamaki yace.

"Yadai bismillah zauna mana".

"Dama zama ya kawo ni"? Ya fad'a yana fiddowa Malam Habu girman idonsa waje.

Cikin son 'kular dashi Malam Habu yace "oh haka akai yi ha'kuri ba zama ya kawo kaba tsaiwa ce ashe ka hangoni a mota na dawo kanata sauri kazo mu gaisa ni kuma na shiga gida saboda yau bazan bari kayi ha'inci ba da kaina zan fito na raba kud'i wa al-umma na gaji da ragal din da ake min".

Zaro ido waje malam kamai da ruwanka yai yana cewa "kuturun ubancan ni kake fad'awa magana a kaikaice"?.

Wani kallo Malam Habu yai masa yace "a'a kaina nake fad'awa magana ba dakai nake ba kasanni akwai saurin tsarguwa musamman yanzu dana fahimci bani kad'ai ne yaron Alhaji ba akwai wasu idan banyi hattara ba asirina gaf yake da tonuwa ka gane dan haka kaja baki kai shiru"🤫.

A masife Malam komai da ruwanka yace "bazan ja bakin nai shirun ba wato saboda kaga gurin kwanana shine kake neman d'ora min hau🙆 ko? Na rantse da Allah kayi da d'an halak kuma zaga gani" yana gama fad'in haka yabar gurin a fusace da kallo suka bishi Sadi da baya son hayaniya yace.

"Amma daka 'kyale shi nifa inaga kamar mutumin nan yana da ta'bin 'kwa'kwalwata wasu lokatan yana abu babu kan gado kaga fa yadda yaxo yaima wani tserere aka kamar bishiya haba wannan abun ba tsari".

Ta'be baki malam Habu yai yana gyara zama yace "kai da Allah manta dashi wannan mutumin baisan me yake ba nafi yarda da abinda ka fad'a kila ya samu ta'bin 'kwa'kwalwar haka nake zato saidai duk wani gigi da hauka da yakeji dashi na damashi na shanye baisan waye ni ba ba'ai min hauka badan ruwa ya daki babban zakara🐓 ba ake masa kallon d'an tsako🐤 humm manta kawai Allah ya rufa asiri amma inaga kafin mubar garin nan saina saita masa zama".

Shidai Sadi shiru yai bai sake magana ba amma a ransa yana fargaba domin yaga take taken Malam komai da ruwanka ba mutumin arziki bane saidai Allah ya kiyaye karya 'kulla musu 'kulallaya suda ba kowa suka sani a garin ba fatan sa Allah ya rabasu lafiya.

'KAUYE🏕️
Kwana biyar tsakani Balarabe yana zaune a kofar d'aki sai gyangyad'i yake har kamar zai kifa sannan ya d'ago fitowar Asabe ta kalleshi tana cewa "inye duniya taka 'kwarai ma Balarabe wato saboda sangarta tai maka yawa shine kazo ka zauna anan harda samun damar barci ko akan na d'auke nayin gidan to daga yau na sauke gara ka tashi ka nema dama wanki ne tsinanniyar 'yar taka takeyi dashi nake cefane kaga yanxu tunda bata nan kaine zaka dawo dan wankau shara girki wanke wanke da dafa min kayan sayarwata duk ranta ta dawo ka huta".

Kallonta Balarabe yai yana cewa "nifa bada yawu na tabar gidan nan ba kinsani bansan ta fice ba laifin Dalah ne".

Katse shi Asabe tai "kai dalla gafara can dama tsari nace kamin ko kaji nace laifinka ne damuwata ka tashi yanzun nan ka fara min aiki ".

Su'kuri Balarabe yai yana kallon ta wata uwar ba'kar harara ta sakar masa tana cewa "oh ka tsaya kallo na bazaka tashi ba kenan"? Da sauri Balarabe ya mi'ke yana kad'e jiki ya nufi gurin wanke wanke tsaki taja tana cije yatsa tace.

"Bahijjah kina ina"?.

Daga d'aki Bahijjah tace "gani a kwance bacci zanyi yane😳"? .

"Au ni kike cewa yane dan ubanki"?.

Ta'be baki Bahijjah tai tana cewa "eh man dole nace yane me zan miki"?.

Asabe bata damu da tambayar rainin da bahijjah tai mata na cewa yane gani take hakan duk cikin fashion🤪 ne tace.

"Ba komai fito da kayanki wadanda sukai datti ki watsowa Balarabe zai wanke".

Daga d'aki Bahijjah tace "ni wallahi na riga na kwanta bazan tashi ba in kin matsu ya wanke min kizo ki d'ebe gasu nan a tsakar d'aki".

Cikin haushi Asabe tace "dan ubanki ni kike fad'awa haka Bahijjah"?.

A hantare Bahijjah tace "Toya kike so nayi nace na riga na kwanta bazan iya tashi ba dole ne wannan wacce irin jaraba ce? Haba da Allah mutsss aikin kawai dun abi a dameka da magana" ta karasa maganar tana gyara kwanciyar ta daidai Asabe ta shigo d'akin ganin zatai magana kawai ta juya mata baya tana jan bargo Asabe batai magana sai kayan data tattara tana fitowa waje dasu ta watsawa Balarabe aka tana cewa.

"Kayi sauri gashi nan yana jiranka bana son asaranci ace har yanzu baka wanke kwano yai goma ba duk da uban me kake kallo? Kaga Balarabe ka kiyaye ni ka fara isata a gidan nan fa zan 'bab'bama maka ransa" shidai Balarabe shiru yai yana sauraron jikinsa sai kikir kirir yake a gaban kwanuka tunda ba sabawa yaiba ba iyawa yaiba duk ya jike jikinsa da ruwa ga kayan wanki data tulo masa tayi zamanta a gefe tana kallonsa a rana sai gumi yake yana sharcewa harda dariyar mugunta take ita kad'ai ganin yadda yai faca-faca.

Humm duniya mai juyi juyi kwad'o a ruwan zafi Allah ya sauwake 😘MIJI😘 wanda kake sa ran da albarkacinsa🤨 zaka shiga ALJANNAH🌲 amma kuma shi ka mayar bawanka😳🙆 wannan ta'bewar har inaaaaa??? hummm gaba gaba dai Asabe🤫.
Chapter 74 · 0% Book details