Sashe 32
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Wani kallo yai masa na baka da hankali amma zan koya maka kafin yace "kace bakasan komai ba ko? Haka kace ko? Lallai yau saina bambance maka abinda ake kira da jaki sha duka" warto shi yai tare da d'uma shi da 'kasa yabi ya take ya hau jibgarsa da dukkan karfi sa ihu Mudi keyi yana neman agaji Sabi'u na tsaye da yake baida zafin rai kamar Habu amma bazai hana shi dukan nasu harsai sun amsa cewa eh.
Jin da Mudi yai idan ya sake za'ai bashi yasa cikin wahala da numfashi da'kyar yace "dan Allah Habu ka tsaya zan fad'a maka gaskiya wallahi zan fad'i gaskiya karka kashe ni zaka 'balla min 'kafa" jin haka yasa da gudu Sabi'u yaje yana 'bam'bare Habu daga ruwan cikin Mudi yai dauke shi yai gefe dashi.
Yana cewa "tsaya haka Habu yanzu zaiyi bayani" huci Habu keyi yana kallon Tanko dake kwance sharkaf kamar matacce a hasale yaje ya wanka masa wani irin gigitaccen mari me karfi sai ga Tanko ya mi'ke tsaye a firgice yana neman hanyar guduwa dam'ko shi Habu yai yana maka shi da 'kasa yace.
"Gidan uban wa zakaje"? Idan kaga na barka ka fita anan to saidai ka fad'a min amsar tambayar danai maka meyasa kaiwa Lami fayd'e"? Zaka fad'a ko saina fasa ma kai"?.
Ganin ya cakumo shi yana dunkule hannunsa zai kai masa naushi yasa jikin Tanko na rawa bakinsa na jini yace "zan fad'a dan Allah kamin hakuri wallahi zan fad'a maka gaskiya".
Sakin sa Habu yai yana kallon Sabi'u yace "kasan Allah yaya Sabi'u bazan 'kyale su fita nan cikin hayyacin su ba indai basu fad'i gaskiya ba saina dau fansar abinda sukai mata kamar yadda kai ka fad'a a kofar gidan mu dan na jika" ya karasa maganar yana kallon Tanko dake ta goge jinin da ya 'bata masa fuska.
'Durkusawa gaban sa Habu yai yana sha'kar wuyan rigarsa 'kara Tanko yana cewa "Habu zaka yanka min wuya dan Allah ka sake ni zan fad'a maka".
Habu bai sake shiba saidai ya sassauta ri'kon da yai masa fuskarsa a d'aure tamau yace "ina jinka".
Jikin Tanko na 'barin tsoro bakinsa na rawa ya fara magana "dan Allah Habu kuyi hakuri ku yafe min na aikata muku kuskure tabbas nine naiwa Lami fayd'e ranar amma dan girman Allah ku dube ni da idanun rahma ku yafe min"..........................
Takaici ne ya rufe Sabi'u yana kallon Tanko yace "kenan zargin mu ya tabbata kaine silar mutuwarta me tai maka zaka dau alhakin ta"?.
Muryar Tanko na rawa yace "babu abinda tai min kawai naji haushi ne saboda tace min bazata aure ni ba na makara shine abun ya 'kona min na tare ta a ranar na mata fayd'e ba da niyyar kasheta na mata haka ba wallahi da nasan zaka mutu bazan yi mata ba kawai ganin ta gane ni yasa na kasa barinta dan karta tona min asiri har saida naji bata motsi ku gafarce n.....................
Bai karasa ba Habu ya d'auke shi da mari yana hankad'a shi ya mi'ke ransa a 'bace ya goge hawayen fuskarsa yana kallon Sabi'u yace "wallahi tallahi bazamu yarda ba yaya sai munkai 'kararsu gaban hukuma dole ne a yanke musu hukuncin daya dace dasu".
Kai Sabi'u ya jinjina yana cewa "muje" fita sukai daga gidan yayin da Mudi ya tashi a guje yana zuwa gurin Tanko dake kwance yana numfashi ya d'ago shi yana mikar dashi tsaye yace "sannu abokina gaskiya habu ya cika 'kasurgumin mugu kaga yadda duk ya sauya ma kamanni Allah ne yai da sauran kwanan ka a gaba da yanzu ya kashe ka" shidai Tanko shiru yai ya kasa magana cikin azaba da'kyar yake jan kafa suka fita daga gidan.
Bayan fitar su Habu kai tsaye gida suka nufa a kofar gidan suka samu Baffah zaune yayi ba'ki dan haka basuyi masa magana bayan sun gaisa suka wuce zuwa ciki suna jiransa ba'a dad'e ba shima ya shigo tare da zama kan wani 'karamin dutsi dake kafe a wajen kofar d'akinsa yana kallon yadda yanayin ya sauya yasan ba kalau ba akwai matsala.
"Sabi'u Habubakar me ya faru nagan ku haka ko kun samu wani bayani ne".
Kai Sabi'u ya d'aga "eh Baffah samu ma na ha'ki'ka Habu ya baka labari".
Maida kallon kan Habu Baffah yai yana cewa "Habubakar meya faru ne na ganku cikin fushi musamman ma kai"?.
Zazzafan numfashi Habu ya sauke yana cewa "wallahi Baffah baza mu yarda ba sai munje kotu wai tsabar zalunci ashe wannan tsinannan ne Tanko ya mata fayd'en bamu sani ba gashi yanzu da yaji wahala ya fad'a da bakinsa harda dan kada takai labari yasa bai 'kyale taba saida ta daina motsi".
Runtse ido Baffah yai jin abinda Habu ke cewa basu ankara ba sai ganin hawaye sukai sharr yana zuba a idanun Baffah tabdijan tashin hankali wanda ba'a sa masa rana hawaye fa suke ganin a idanun Baffah a zabure cikin tsananin fushi habu ya mi'ke yana cewa "wallahi bazan kyale Tanko ba Baffah saina kashe shi tunda yai silar zubar hawaye a idonka abunda ban ta'ba gani tare dakai ba a rayuwa ta sai yau" juyawa yai zai fita muryar Baffah da alamun kuka yace.
"Habubakar dawo kada ka koma gurin su na barwa Allah shine ya halicce mu sannan shike da iko damu zai sakawa Lami bazai kyale shiba Tanko ya cuce bazan ta'ba yafe masa ba har ranar komawa ta ga ubangiji" ya karasa maganar kukan nasa na sake fitowa.
'Durkusawa gaban sa Habu yai yana kifa kanshi a jikin Baffah kawai shima ya fara kuka wanda Sabi'u da sauri ya rungume su shima yana zubda hawaye suna wannan hali sukaji sallama yaro.
"Wai Baffah yana nan yazo inji Isubu me gari yana nemansa".
'Dagowa Baffah yayi yana kallon yaron cikin ajiyar zuciya yace "kace masa gani nan ina zuwa" yaro na fita Baffah ya mi'ke yana daukar buta ya wanke fuskarsa.
Ran Habu a 'bace yace "wato 'kara suka kai gurin me gari? Aiko yau saina tabbatar basuyi kwanan gida ba wallahi saina d'ebo musu hukuma muje Baffah.
Baffah bai iya magana ba kawai yayi gaba ne suka bishi a baya har gaban me gari suka samu guri dam ya cika da jama'a ma'kil ana ta hayaniya sallama Baffah yai yana zama cikin mutunci suka gaisa da kowa.
Kallon sa me gari yai "Baffah kasan dalilin kiranka?.
Kai Baffah ya girgiza "a'a ina fata lafiya"?.
Cigaba me gari yai "eh lafiya ba lafiya malam Balah ne ya kawo 'kararka cewa Habu da Sabi'u sun daki d'ansa Tanko harda rauni sukayi masa ga sun zubar masa da ha'kora guda biyu haka ne"?.
Kallon su Sabi'u Baffah yai ganin basu musa ba yace "gasu nan me gari ka tambaye su ni ban sani ba".
Kafin me gari yai magana Balah yace "a 'kwarai ka turo suwa adamu dukan mutuwa sannan kace wai baka san komai ba wallahi bazan yarda ba sai munyi shari'a dakai" gun me gari ya juya yana cigaba "me gari nifa ba cewa nai a tambaye shiba kuma ba sasanto naso ba idan bazaka iya ba zan kai gaba a bimin kadin dukan da sukai masa".
Shiru Baffah yai yana kallon Balah cikin mamaki wato d'ansa ya aikata wannan mummunan zunubin amma tsabar tsaurin ido har ya samu bakin magana.
Hayaniyar da suka kaure tsakanin Habu da Balah ne ya dawo da Baffah daga tunanin da yake yana cewa "Habubakar kayi shiru wannan ba zancen ka bane"
Shiru yai Balah dake binsa da kallo yace "kai mara kunya ba dakai nake yi ba da ubanka nake magana ba hurumin ka bane" a harzu'ke Habu zai magana Baffah ya dakatar dashi, mi'kewa Habu yai yana fita a wajen Sabi'u yaso binsa amma ya 'kyale domin yana son jin rainin wayon da Tanko yaje ya shiryawa Balah suna zaune mutane na kallo sai shari'a ake bugawa Tanko na rantsuwar bashi yaiwa Lami fayd'e ba kawai sai jin jiniyar mota sukai tazo tayi parking a gurin Habu ya fito fuska a had'e.
Kowa zaro ido waje yai suna bisa da kallo kai tsaye yaje ya cakumo Tanko yana fito dashi wani d'an sanda dake tsaye yace.
"Barshi aikin mune" yana kallon Tanko yace "your under arrest 🙊 malam munzo kamen ka" ya karasa maganar yana d'ago ankwa, zaro ido Tanko yai jikin sa na kakkarwa Balah daya taso da gudu ya ce.
"Wallahi yalla'bai bazan bari ka tafi min da yaro ko'ina ba bayan sharri akai masa".
Wani kallo d'an sandan yai masa wanda yasa Balah matsawa da sauri ya koma gefe yana gani suka sa Tanko a mota shida Mudi habu da Sabi'u suka shiga mota tabar gurin da sharad'in kada wanda ya biyo a yau sai gobe.
Zage zage Balah keyi ko gaban sa baya gani ya tafi gida takalmansa a hannu yana shiga ya soma kwalla kira "Delu ke Delu kina ina fito ga ba'kar rana tazo mana yau bankad'a ta same mu".
Da sauri ta fito daga d'aki tana cewa "malam lafiya ya na ganka haka ina Tankon".
Zama Balah yai akan tabarma yana cewa "Tanko yau kwanan bayan kanta zaiyi d'an iskan yaron nan ne Habubakar ya d'ebo masa 'yan sanda sun tafi dashi da abokinsa d'an gidan marigayi malam Ya'u suna can".
'Dora hannu Delu tai aka "mun shiga uku wai me ya had'a sune"?.
"Yo me ya had'a su sharri sukai masa da yake basu gaji arziki ba".
"Sharri kuma malam wani abu ne ya faru"?.
"Eh wai yarinyar nan Lami data rasu cewa saboda anyi mata fayd'e kuma shi saurayin tane duk garin suka rasa wanda zasu la'kabawa sai shi wai shine ya mata".
Ido waje Delu "innalillahi sharrin da zasuyi masa kenan aiko wallahi basu isa ba baza mu yarda".
'Kwafa Balah yai "taya kuwa zamu yarda jira nake gari ya waye ai na tafi gurin yan sandan ayita ta 'kare duk wanda yakai 'kararka aiya gama tozarta ka".
Jin da Mudi yai idan ya sake za'ai bashi yasa cikin wahala da numfashi da'kyar yace "dan Allah Habu ka tsaya zan fad'a maka gaskiya wallahi zan fad'i gaskiya karka kashe ni zaka 'balla min 'kafa" jin haka yasa da gudu Sabi'u yaje yana 'bam'bare Habu daga ruwan cikin Mudi yai dauke shi yai gefe dashi.
Yana cewa "tsaya haka Habu yanzu zaiyi bayani" huci Habu keyi yana kallon Tanko dake kwance sharkaf kamar matacce a hasale yaje ya wanka masa wani irin gigitaccen mari me karfi sai ga Tanko ya mi'ke tsaye a firgice yana neman hanyar guduwa dam'ko shi Habu yai yana maka shi da 'kasa yace.
"Gidan uban wa zakaje"? Idan kaga na barka ka fita anan to saidai ka fad'a min amsar tambayar danai maka meyasa kaiwa Lami fayd'e"? Zaka fad'a ko saina fasa ma kai"?.
Ganin ya cakumo shi yana dunkule hannunsa zai kai masa naushi yasa jikin Tanko na rawa bakinsa na jini yace "zan fad'a dan Allah kamin hakuri wallahi zan fad'a maka gaskiya".
Sakin sa Habu yai yana kallon Sabi'u yace "kasan Allah yaya Sabi'u bazan 'kyale su fita nan cikin hayyacin su ba indai basu fad'i gaskiya ba saina dau fansar abinda sukai mata kamar yadda kai ka fad'a a kofar gidan mu dan na jika" ya karasa maganar yana kallon Tanko dake ta goge jinin da ya 'bata masa fuska.
'Durkusawa gaban sa Habu yai yana sha'kar wuyan rigarsa 'kara Tanko yana cewa "Habu zaka yanka min wuya dan Allah ka sake ni zan fad'a maka".
Habu bai sake shiba saidai ya sassauta ri'kon da yai masa fuskarsa a d'aure tamau yace "ina jinka".
Jikin Tanko na 'barin tsoro bakinsa na rawa ya fara magana "dan Allah Habu kuyi hakuri ku yafe min na aikata muku kuskure tabbas nine naiwa Lami fayd'e ranar amma dan girman Allah ku dube ni da idanun rahma ku yafe min"..........................
Takaici ne ya rufe Sabi'u yana kallon Tanko yace "kenan zargin mu ya tabbata kaine silar mutuwarta me tai maka zaka dau alhakin ta"?.
Muryar Tanko na rawa yace "babu abinda tai min kawai naji haushi ne saboda tace min bazata aure ni ba na makara shine abun ya 'kona min na tare ta a ranar na mata fayd'e ba da niyyar kasheta na mata haka ba wallahi da nasan zaka mutu bazan yi mata ba kawai ganin ta gane ni yasa na kasa barinta dan karta tona min asiri har saida naji bata motsi ku gafarce n.....................
Bai karasa ba Habu ya d'auke shi da mari yana hankad'a shi ya mi'ke ransa a 'bace ya goge hawayen fuskarsa yana kallon Sabi'u yace "wallahi tallahi bazamu yarda ba yaya sai munkai 'kararsu gaban hukuma dole ne a yanke musu hukuncin daya dace dasu".
Kai Sabi'u ya jinjina yana cewa "muje" fita sukai daga gidan yayin da Mudi ya tashi a guje yana zuwa gurin Tanko dake kwance yana numfashi ya d'ago shi yana mikar dashi tsaye yace "sannu abokina gaskiya habu ya cika 'kasurgumin mugu kaga yadda duk ya sauya ma kamanni Allah ne yai da sauran kwanan ka a gaba da yanzu ya kashe ka" shidai Tanko shiru yai ya kasa magana cikin azaba da'kyar yake jan kafa suka fita daga gidan.
Bayan fitar su Habu kai tsaye gida suka nufa a kofar gidan suka samu Baffah zaune yayi ba'ki dan haka basuyi masa magana bayan sun gaisa suka wuce zuwa ciki suna jiransa ba'a dad'e ba shima ya shigo tare da zama kan wani 'karamin dutsi dake kafe a wajen kofar d'akinsa yana kallon yadda yanayin ya sauya yasan ba kalau ba akwai matsala.
"Sabi'u Habubakar me ya faru nagan ku haka ko kun samu wani bayani ne".
Kai Sabi'u ya d'aga "eh Baffah samu ma na ha'ki'ka Habu ya baka labari".
Maida kallon kan Habu Baffah yai yana cewa "Habubakar meya faru ne na ganku cikin fushi musamman ma kai"?.
Zazzafan numfashi Habu ya sauke yana cewa "wallahi Baffah baza mu yarda ba sai munje kotu wai tsabar zalunci ashe wannan tsinannan ne Tanko ya mata fayd'en bamu sani ba gashi yanzu da yaji wahala ya fad'a da bakinsa harda dan kada takai labari yasa bai 'kyale taba saida ta daina motsi".
Runtse ido Baffah yai jin abinda Habu ke cewa basu ankara ba sai ganin hawaye sukai sharr yana zuba a idanun Baffah tabdijan tashin hankali wanda ba'a sa masa rana hawaye fa suke ganin a idanun Baffah a zabure cikin tsananin fushi habu ya mi'ke yana cewa "wallahi bazan kyale Tanko ba Baffah saina kashe shi tunda yai silar zubar hawaye a idonka abunda ban ta'ba gani tare dakai ba a rayuwa ta sai yau" juyawa yai zai fita muryar Baffah da alamun kuka yace.
"Habubakar dawo kada ka koma gurin su na barwa Allah shine ya halicce mu sannan shike da iko damu zai sakawa Lami bazai kyale shiba Tanko ya cuce bazan ta'ba yafe masa ba har ranar komawa ta ga ubangiji" ya karasa maganar kukan nasa na sake fitowa.
'Durkusawa gaban sa Habu yai yana kifa kanshi a jikin Baffah kawai shima ya fara kuka wanda Sabi'u da sauri ya rungume su shima yana zubda hawaye suna wannan hali sukaji sallama yaro.
"Wai Baffah yana nan yazo inji Isubu me gari yana nemansa".
'Dagowa Baffah yayi yana kallon yaron cikin ajiyar zuciya yace "kace masa gani nan ina zuwa" yaro na fita Baffah ya mi'ke yana daukar buta ya wanke fuskarsa.
Ran Habu a 'bace yace "wato 'kara suka kai gurin me gari? Aiko yau saina tabbatar basuyi kwanan gida ba wallahi saina d'ebo musu hukuma muje Baffah.
Baffah bai iya magana ba kawai yayi gaba ne suka bishi a baya har gaban me gari suka samu guri dam ya cika da jama'a ma'kil ana ta hayaniya sallama Baffah yai yana zama cikin mutunci suka gaisa da kowa.
Kallon sa me gari yai "Baffah kasan dalilin kiranka?.
Kai Baffah ya girgiza "a'a ina fata lafiya"?.
Cigaba me gari yai "eh lafiya ba lafiya malam Balah ne ya kawo 'kararka cewa Habu da Sabi'u sun daki d'ansa Tanko harda rauni sukayi masa ga sun zubar masa da ha'kora guda biyu haka ne"?.
Kallon su Sabi'u Baffah yai ganin basu musa ba yace "gasu nan me gari ka tambaye su ni ban sani ba".
Kafin me gari yai magana Balah yace "a 'kwarai ka turo suwa adamu dukan mutuwa sannan kace wai baka san komai ba wallahi bazan yarda ba sai munyi shari'a dakai" gun me gari ya juya yana cigaba "me gari nifa ba cewa nai a tambaye shiba kuma ba sasanto naso ba idan bazaka iya ba zan kai gaba a bimin kadin dukan da sukai masa".
Shiru Baffah yai yana kallon Balah cikin mamaki wato d'ansa ya aikata wannan mummunan zunubin amma tsabar tsaurin ido har ya samu bakin magana.
Hayaniyar da suka kaure tsakanin Habu da Balah ne ya dawo da Baffah daga tunanin da yake yana cewa "Habubakar kayi shiru wannan ba zancen ka bane"
Shiru yai Balah dake binsa da kallo yace "kai mara kunya ba dakai nake yi ba da ubanka nake magana ba hurumin ka bane" a harzu'ke Habu zai magana Baffah ya dakatar dashi, mi'kewa Habu yai yana fita a wajen Sabi'u yaso binsa amma ya 'kyale domin yana son jin rainin wayon da Tanko yaje ya shiryawa Balah suna zaune mutane na kallo sai shari'a ake bugawa Tanko na rantsuwar bashi yaiwa Lami fayd'e ba kawai sai jin jiniyar mota sukai tazo tayi parking a gurin Habu ya fito fuska a had'e.
Kowa zaro ido waje yai suna bisa da kallo kai tsaye yaje ya cakumo Tanko yana fito dashi wani d'an sanda dake tsaye yace.
"Barshi aikin mune" yana kallon Tanko yace "your under arrest 🙊 malam munzo kamen ka" ya karasa maganar yana d'ago ankwa, zaro ido Tanko yai jikin sa na kakkarwa Balah daya taso da gudu ya ce.
"Wallahi yalla'bai bazan bari ka tafi min da yaro ko'ina ba bayan sharri akai masa".
Wani kallo d'an sandan yai masa wanda yasa Balah matsawa da sauri ya koma gefe yana gani suka sa Tanko a mota shida Mudi habu da Sabi'u suka shiga mota tabar gurin da sharad'in kada wanda ya biyo a yau sai gobe.
Zage zage Balah keyi ko gaban sa baya gani ya tafi gida takalmansa a hannu yana shiga ya soma kwalla kira "Delu ke Delu kina ina fito ga ba'kar rana tazo mana yau bankad'a ta same mu".
Da sauri ta fito daga d'aki tana cewa "malam lafiya ya na ganka haka ina Tankon".
Zama Balah yai akan tabarma yana cewa "Tanko yau kwanan bayan kanta zaiyi d'an iskan yaron nan ne Habubakar ya d'ebo masa 'yan sanda sun tafi dashi da abokinsa d'an gidan marigayi malam Ya'u suna can".
'Dora hannu Delu tai aka "mun shiga uku wai me ya had'a sune"?.
"Yo me ya had'a su sharri sukai masa da yake basu gaji arziki ba".
"Sharri kuma malam wani abu ne ya faru"?.
"Eh wai yarinyar nan Lami data rasu cewa saboda anyi mata fayd'e kuma shi saurayin tane duk garin suka rasa wanda zasu la'kabawa sai shi wai shine ya mata".
Ido waje Delu "innalillahi sharrin da zasuyi masa kenan aiko wallahi basu isa ba baza mu yarda".
'Kwafa Balah yai "taya kuwa zamu yarda jira nake gari ya waye ai na tafi gurin yan sandan ayita ta 'kare duk wanda yakai 'kararka aiya gama tozarta ka".