← Book details Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 118 OF 145

Sashe 118

Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Sauke ajiyar zuciya Makiyyah tai tana cewa ",humm kefa Khaldiyyah kukan dad'i kike gara ke da sau'ki zaki iya tunkararsa kai tsaye batare dajin tsoro ba amma nifa wallahi Asad idan na ganshi gabana har fad'uwa yake tsabar kwarjininsa kuka wallahi Nima shine za'bina".

Ta'be baki Khimiyyah tai tana kad'a kai domin ita kam yanzu babu komai tsakaninta da Asad sai d'aukar fansa ko sauraren maganar bata yi iya su kad'ai suke tattaunawa a junansu.

Da sallama Asad ya shiga fadar mai martaba ya tarar mai girma Alhussain yana can ga Mami sannan kuma shima gasu shida Ajeeb zama yai yana gaidasu tare da yi musu barka da dare amsawa mai martaba yai yana kallonsa kafin ya mayar da hankalin sa kan Ajeeb wanda yai shiri yana kallon Asad kamar mai tunani gyara zama Mai Martaba yayi sosai yana fuskantar Asad yace.

"Asad ka saurare ni da kyau cikin nutsuwa kaji abinda zan fad'a maka kasan cewa Allah ne keyin abu da ayi ko duk dabarar mutum bai isa yayi maka wani abu wanda Allah bai nufa ba Asad Ajeeb d'an uwanka ne uwarku d'aya sannan ubanku d'aya yaga ya isa dakai yana da iko dakai zai iya yai maka abu kansa tsaye batare daya nemi yardarka ko shawararka ba shiyasa lokaci mai d'an tsawo yazo min da wata magana yaga yarinya mai nutsuwa wacce yaga ta dace dakai zai wakilceka ya aura maka ita amma ya rokeni alfarmar kada na sanar dakai sai ranar da aka d'aura auren saboda gudun fitinarka Asad Ajeeb baiyi maka haka dan ya bata maka raiba a'a yayi haka domin samun farin ciki da walwalarka dan Allah Asad kada ka tada hankalin ka akan wannan al'amarin ka d'auka kaddara ce ka kar'bi auren nan da hannu biyu kayiwa Ajeeb godiya".

Zabura Asad yai yana cewa "Abba dawa aka d'aura aure dani fa? Haba wannan zance ne".

Da mamaki Mai Martaba yace "Asad nine zan fad'i magana kace zance ne"?.

Da sauri Asad ya d'an daidaita nutsuwarshi yana cewa "kayi hakuri abba abunne yazo min a bazata amma dai dan Allah Abba kace min da wasa kake taya Ajeeb zaiyi min aure"?.

Kai mae Martaba ya girgiza ''a'a Asad bada wasa bane da gaske ne dakai aka d'aura aure ba Ajeeb ba duk wani abu da kaga Ajeeb yana yi domin kane ni na amince masa domin bada ka yayi maka hakan ba saida ya nemi shawarata data d'an uwana sannan aka aura maka ita"....

Cafff mai martaba yana rufe baki Asad ya mi'ke tsaye a fusace yana kallon Ajeeb yace "dama nace maka kayi min aure ne nace maka Ina bu'katar aurene"?.

Wata uwar harara Ajeeb ya sakar masa yana cewa "dama saika bu'kata da nayi maka isa nai dakai shiyasa na nuna maka isar tawa a aikace ka gane"?.

Ajeeb na rufe baki Asad ya dam'keshi da dambe ransa a mugun 'bace idonsa ya gama rufewa har wata jijjiga da saiwa yake kamar wanda tsumunsa ya tashi mai martaba yana zaune yana kallon su ko kad'an baiyi motsi ba balle yayi magana mai girma Alhussain ke tayi da bakinsa amma ko jinsa basayi haka Asad ya shakewa Ajeeb wuya yana cewa.

"Ka bani amsar dana tambaye ka nace maka kayi min aure ne''?.

Fisgewa Ajeeb yai shima ransa a had'e sosai yana cewa "kuma dama sai kace nayi maka isa nayi shiyasa nayi maka d'in kuma babu yadda zakai dani zama da matar ya zama dol.....................

Tsalle Asad yai ya sake sha'karsa sukaci gaba da dambe wanda in kaga yadda suke kaiwa juna duka sai kayi tunanin irin ri'kakkun abokan gaban nan ne duk sun hargitsa parlon har kujeru Saida suka san ba lafiya ba table na glass kuwa sun fasa kusan uku har show glass saida suka ruguzashi ganin abun nasu yad'au zafi yasa Mai martaba cewa.

"Ku saki junanku kafin ku 6ata min rai Asad wannan abun ya isa haka sake shi kaima Ajeeb ka sake shi kun haukace ne kome tsabar rashi hankali".

Sakin Ajeeb Asad yai yana turashi baya da karfi yai yuuu zai fad'i da sauri Mai girma Alhussain ya tareshi yana cewa "subahanallahi Asad me kake haka kada ka fasa masa kai da wannan fasassun glass d'in".

Wani irin huci Asad keyi ji yake kamar ya sake fisgo Ajeeb d'in ya dokashi da qasa yabi ya take jin zuciya taxo masa har wuya yasa da qarfi ya jawo rigar Ajeeb wanda mai martaba yace.

"Asad sake shi nace".

Runtse ido Asad yai da qarfi yana sakin rigar Ajeeb d'in kafin ya juya da sauri a fice daga gurin yana shiga part d'insa a gigice ya fara tattara kayansa a take bai sake minti biyar cikin masarautar ba ya fice zuwa airport ya koma Marshall islands.

Hankalin Mami in yayi dubu ya tashi bawai fad'an da sukai bama Abinda yafi d'aga mata hankali shine jin wai duk wannan fafutukar da jajircewar da Ajeeb keyi dama saboda ya aurawa Asad yarinyar ne bayan ya riga ya fad'a masa bazaiyi aure ba sai yayi retire kai innalillahi wa Inna ilaihi raji'un kallon Mai martaba tai tana cewa.

"U're highness nifa ban gane komai ba wai dama shi Ajeeb d'in kunyi dashi ba a kansa zaiyi aure ba Asad zaiyi wa kai Ajeeb miyasa kayi masa haka bayan ya riga ya fad'a maka bazai aure yanxu ba"?.

Sauke ajiyar zuciya Ajeeb yai yana kallon Mami kafin ya zauna yana cewa "Mami nifa banyi haka dan 'bata ran Asad ko wani daga cikinku ba nayi haka ne saboda ina son ganinsa cikin farin ciki Mami dan Asad murd'add'an mutum ne bazai iya bi a huce ya tsaya ya saurareni ba amma wallahi Amatullahi yarinyar hundred% ta dace dashi ita kad'ai ce zata iya dawo dashi hanya ta sanyaya zafin zuciyarsa".

Kai Mami ta jinjina tana cewa "tabdijan To kaima Ajeeb tunda a gabanka yayi maganar cewa saiyayi retire meyasa zakai masa haka dan kawai kasa hankalin mutane ya tashi kasan fa waye Asad ko"?.

Tun kafin Ajeeb yayi magana mai Martaba yace "Kuma dan yace sai yayi retire tsabar rashin hankali dama mu irinsa ne koda ace Ajeeb baiyi masa ba ni da zanyi masa aidai ni bazai kamani da kokawa ba abinda Ajeeb yayi shine daidai Allah yayi maka albarka sannan kayi zamanka ka kwana anan bazaka fita daga part d'in nan ayau ba saboda Asad yad'au fushi da yawa idan kuka had'u akwai matsala mai girma kuma koda gobe ne karka je inda yake".

Kai Ajeeb ya d'aga "to Abba nagode da kuka fahimce ni".

Sauke ajiyar zuciya Mami tai bata sake magana ba saidai ranta fal yake da tarin tunanin yanzu da Asad ya fita a haka Ina yayi me yake yi a wanne hali yake karfa ace............. Da sauri ta d'ago tana kallon Mai Martaba da suke magana da Mai girma Alhussain tace.

"Allah ya baka nasara bari naje kar ba'ki masu kawo amarya suzo Ina nan" ta fad'a tana mi'kewa sannan ta kalli Sultana Fatima wacce itama ta mi'ke tace "yauwa Fatima muje dan Allah kinsan ga Shaukiyyah ma bamuje mun kaita part d'in Ameer ba abubuwa sunyi yawa musamman wannan matsalar data shigo ciki amma Allah ya tsayarta da sau'ki ta 6angaren Asad domin shi nafi ji babyn Mami uhm muje" fita sukai suna shiga part d'in Mami har an kawo amarya su Aunty Fadilah sun kar'beta zama Mami tai cikin zulumi kafin ta kalli futuha tana cewa.

"Asad ya shigo nan ne"?.

Kaita girgiza "a'a bai shigo ba ai kila suna can tare da ango Ajeeb"?.

"Humm wanne irin ango Ajeeb ai futuha ki bar maganar in ana sallah ba'a magana duk wannan abu da Ajeeb yakeyi da rawar jikinsa ashe basaja ce wai Asad yake nemawa auren u're highness ya sani bai fad'a min sai yanzu da zancen ya tashi bakiga yadda suka hargitsa masa parlor ba ni damuwa ta a yanxu inda Asad d'in yake nasan ba lallai yana nan ba banaji a jikina yana cikin masarautar nan".

Zaro mata Aunty Fadilah tai tana kallon Mami da mamaki tace "da Asad aka d'aura auren kuma garin yaya haka ta faru shi da yace sai yayi retire miyasa Ajeeb zaiyi masa haka"?.

"Garin tsautsayi da karambanin Ajeeb wallahi Kinga ya jawo mana tashin hankali ana cikin nishad'i duk murna ta koma ciki".

Kai Aunty Fadilah ta d'aga "ok bari naje part d'in Asad d'in mu gani ko yana nan"?.

"A'a Fadilah karki tunkari Asad yanxu ba lallai ya gane kiba kada yayi miki kallon Ajeeb kina shiga ya sha'ke ki mu shiga uku ana kukan targad'e karaya ta samu"?.

Dariya Aunty Fadilah tai tana cewa "ayya kada ki damu bari na gano" ta karasa maganar tana fita nannauyan numfashi Mami ta fitar tana mi'kewa tace.

"Fatima muje muji da Shaukiyyah tukuna daga baya naji da wannan zafin dana dauka cakwakiya tayi min yawa dole saina bu'kaci ganin likita bayan biki".

'Yar dariya Sultana Fatima tana cewa "uhm Allah ya rufa asiri dai nikam saidai ki d'auki Futuha ko Aleemah kuje kin manta"?.

Dafe kai Mami tai "oh ha'kuri sha'afa nayi gabadaya a gigice nake ok bari muje" ta fad'a tana shiga bedroom d'inta Sultana Fatima kuma ta fita.

Aunty Fadilah kam bata samu kowa a part d'in Asad ba har Amjadd ta tambaya ko Asad yana ina ya fad'a mata ya ganshi goye da jaka ya fice ko tsayawa ya bar masa sa'kon stockyard d'insa bai samu dama ba saboda fushin daya d'auka.

Jin haka yasa Aunty Fadilah juyawa a hanya ta had'u da Mami tare da Aunty Futuha da Aunty Aleemah suka sake juyawa zuwa 6angaren mighty Alhussain tana fad'a mata abinda Amjadd yace mata itakam Mami bata iya cewa komai ba dan tasan gurin aikinsa ya koma amma hakan ma ta godewa Allah tanan hankalinta taji ya d'an kwanta sakamakon ba Asad d'in za'a fi jin sau'ki kowa zai zauna lafiya.

Sun shiga part tun daga nesa suke jiwo kuka da ihu a part d'in Sultana Shafi'ah mahaifiyar amarya Shaukiyyah da Makiyyah da sauri suka karasa shiga uhmm Makiyyah ce sai kururuwa da fisge-fisge take tana cewa.
Chapter 118 · 0% Book details