Sashe 5
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Tunanin tane ya katse jin tsawar da Balarabe ya daka yana kaiwa Indo duka yace "dan bantan uban ki dan darar ubanki dan 'kashin singallin uwarki yau saikin barmin gida na kore ki bani bake har abada Indo ki kama gabanki'.
Kukan takaici da damuwa Indo ta fashe dashi tana sake durkusawa sosai ta soma bashi hakuri da batasan laifin datai masa ba ace uba na garine amma ya tsani yarsa ya rikajin duk duniya ba wanda baya son gani sai ita, "baki ji me nace bane zaki tashi a gabana ko saina fasa miki baki" yai maganar yana kai mata harbi da kafa jan kujera Asabe tai tana zama tare da zubo musu ido bakinta har kunne tace "malam kayi hakuri ka kyale ta tana mace idan ka koreta yanzu ina zataje duniya zata shiga karshe ta dirko cikin shege kuma ta dawo ta haife maka shi a gida" a zafafe Balarabe yace "Allah ya sauwake saidai ta nufi gidan marina amma ba gida ba dan ni na sallama ta" "to yanzun dai kayi hakuri na fanshe ta da sharadin zata rika yi mini duk wani aikin gida kama daga shara wanki wanke kwanuka aikin abinci kai inaso Bahijjah ma ta huta Indo ta dawo fita min da abincin sayarwa ta" ta karasa maganar tana sakarwa Indo muguwar harara.
"Wannan shi kike bukata"? Balarabe ya tambaya jiki na mazari d'aga kai Asabe tai "eh hakan ma yayi daga yau ka zama sarki ni gimbiya Indo da Dala bayin mu ko me kace"? Da sauri ya amsa mata "eh na amince na amince ba damuwa dama ai bayin ne aikin jakuna ne ya dace dasu" murmushi Asabe tai yauwa bari a fara yanzu ke Indo dauki bokatin san kije yanzu ki kawo min ruwa ke kuma Dala saiki dora mana tuwo".
Cikin takaici Dala tace "baki isa ba Asabe kinyi kadan a gidan nan kikazo kika sameni dan haka baza ki min mulkin mallaka ba" zaro ido Asabe tai tare da fashewa da dariya tace "au ashe har yanzu da d'an saurin karfin ki Dalah lallai kam na jinjina miki" sai kuma ta hade rai cikin tsawa tana kallon Indo tace "ke kuma ubanki kike jira da bazaki tashi ki fara abinda nace miki ba idan kin debo ga wankin Bahijjah can ya na jiran ki" mikewa Indo tai tana sake goge hawayen fuskarta tadau bokiti tana yin waje.
"Malam gaskiya nifa ban gane anyi gabas da kare ya zanyi magana Dala ta musa min kuma kana jinta baka dau mataki ba ko tsoron ta kake domin labari yazo min idan bana nan nayi tafiya wai wannan abar mai kamar ta'barya har ka zauna tana maka masifa to wallahi bazai yiwu ba gaskiya da sake idan baka gyara ba zan karbe kudade na dana baka kake juyawa" jin barazanar da Asabe ke masa yasa cikin rarrashi yace " kiyi hakuri hakan bata ta'ba faruwa ba karya ake min har nine zan tsaya sauraron wannan abar kibar wata magana kawai ke kadai nake so da Bahijjan ki" dariya Asabe tai "da gaske kake"? Cikin nuna an gama dashi an shanye shi yace "kwarai Asabe da gaske nake " hade rai Asabe tai tana cewa "to ni ban yarda ba baka nuna min a zahiri ba saika saitawa wannan agwagwar matar taka hanya idan kuma ba haka ba daga yau baka sake mora ta sisi kaji na fad'a maka" jiki na rawa cikin tsawa Balarabe yace "ke wai Dalah wacce iriyar bulkuma ce gidahuma bance ki wuce ki fara aiki ba so kike ki silar auren ki yanzun nan kinsan halina sarai ni ba ba'kon ki bane" a damuwance Dalah ta wuce ta barsu a gurin da harara Balarabe ya bita yana cewa "ke kam Dalah kinyi asara mace sai bakin hali yadda fuskar take haka Zuciyar take wuluk da baki da mugun hali nayi da nasanin auren ki Dalah dole ce tasa nake zaune dake amma a juri zuwa rafi wata rana tulu zai fashe" yana fadin haka ya fita yana sake babbaka fad'a kamar bazai ta'ba shiru.
Yayin da Asabe tasa Dalah a gaba tana sheka dariya kamar zata kifa harda hawaye tace "to ya kikaji irin salon nawa Dalah kenan na fad'a miki baza ki iya ja dani ba bakisan wace ni Asabe ba suna a kawai kikeji amma daga yanzu ina fata sunan ya zauna a Zuciyar ki har abada domin nayi alkawarin saina 'kuntata miki daga yanzun kin fara shan dandanon azaba dake da 'yarki a hannu na mu zuba mu gani waye zai nasara saina kaiki kasa" dagowa Dalah tai tana kallon Asabe da jin maganganun da take fad'a saidai batai mamaki domin tun lokacin da Balarabe zai aureta mutane ke tausaya masa suna koka mata cewa zai auro mata masifa Asabe tsiya ce mai lasisi gashi kuwa abinda ake fad'i ya tabbata.................... "Meye kike kallo na maiya"? Muryar Asabe ce ta katse mata tunani danne damuwa da bacin ran dake cin ta Dalah tai tana kankaro murmushi tace "Allah ya shirye ki domin ke abar tausayi ce daga ranar da duniya ta juya miki baya zaki bayani" dariya dariya Asabe tai "ahayye nanaye yau ake yinta lallai kam Dalah kina lokacin yanzu har kece zakice kina tausayin wani? Ta fad'a tanai mata wani kallo na tsantsan rashin mutunci Sai kuma ta sake bushewa da dariya tana cewa amma kinci abinci a kanki shin kina duba mudubi kuwa kodan ina za'a samu darajar mudubi bayan komai bai wadata ba har kice zaki wa wani gori tirrrrr anji kunya 'yar ba'ki ai labari ya same ni tun bayan na auri Balarabe cewa ke maiya ce yar mayu jikar mayu iyayen ki korar maiya akayo musu daga wani tsinannan kauye suka dawo nan suka addabe mu wato da dare baban ki har kura yake zama ko🙊? Daidai Indo ta shigo da bokatin ruwa ta dire asabe dake binta da kallon banza tace bance kayan Bahijjah zaki wanke ba yar gwana jikar maiya Asabe take Aiko mata da mugayen kalaman da take fad'awa uwar ga tsinuwar Balarabe a kanta kuka kawai take kamar ranta zai fita bangare na Zuciyar na adduar Allah ya kawo mata sauyi cikin rayuwarta.
Amatu na zaune a kofar d'akinsu tana duba wani littafin addua Jamila na gefenta tana gyarawa A'i kayan miyar abincin saidawar su ta kalli yadda Aisha ta shigo jikinta duk a jike shakaf da gumi alamar daga aikatau take tana haki da sassarfa ta iso inda suke tana zama sai haki tace cikin tausayawa Jamila yace "sannu Aisha Allah dai ya rufa mana asiri ya kawo mana canji a rayuwar mu" murmushin karfi hali Aisha tai tana cewa "amin Amatullahi me kike dubawa ne"? Murmushi Amatu tai batare data d'ago ba domin ita ba ma'abociyar 'kure mutum da kallo bace tace "sannu Aisha kiji yadda kike haki fa dan Allah idan aiki yafi karfin ki kina ragewa wannan gajiya fa da kuke dibawa jikin ku zata tambaye ku sai lokacin tsufa" fuskar Aisha cike da damuwa tace "to ya zanyi Amatu rashi ne yasa nasan da baban mu nada shi duk haka bazata faru ba" sauke ajiyar zuciya Amatu tai tare da jinjina kai tace "haka ne amma dan Allah a rika ragewa aikin na yawa" dariya Aisha tai tana cewa "shikenan babbar aunty za a kiyaye kaka mai kamar uwa hajiya Hauwa's mai zamani" dariya sukai Amatu na mata hararar wasa tace "meye na Kiran suna na haka babu ko dan kara"? Har lokacin fuskar Aisha da fara'a tace " kakar mu na tuno duk da bamu Santa ba Allah sarki hajiya Hauwa naji mutuwar 'yar tsohuwar nan" maida hankalin ta kan littafi Amatu tai tana cewa "to ta zamuyi wanda ya fimu sonta ne ya karbeta duk wata kulawa da kauna da zamu gwada mata bayan nasa ne shike iko da kowa" sauke ajiyar zuciya Aisha tai tana kallon Saude data fito a d'aki tana mata kallon mamaki na ke kuma yaushe kika shigo mikewa tai tare da nufar ta yayin da Jamila ma ta mike tana daukar kayan miyar ta tafi gidan ni'ka.
Shiru Amatu tai tana kallon kowa da komai gida babban gida amma yanayin tsarinsa da gyara gashi babanta nada dangi amma duk laifinsa suke gani wai ya zauna kara zube ba sana'a yasa rashin zuciya gashi ya tara iyalai shiru tai ta nutsa cikin tunani lokacin da baban ta yaje gurin yayansa ya bashi kud'i zai biya mata ta zana jarrabawa ya hana dan rufe ido tai maganganun da kawu Ilyah ya fad'awa babanta na mata yawo a kunne daga lokacin data tambayi kudin jarrabawar.
Cikin mamaki shigowar malam habu ganin Amatu zaune tana kuka yasa ya karaso da sauri yana d'ago ta tare da goge mata hawaye cikin lallahi yace "Mamana kukan me kike ba na raka ki har makaranta ba meyasa kika dawo" Amatu na shashshekar kuka tace "baba wai malamin yace ban bada kud'i ba wannan shekarar ma bazan zana jarrabawa ba saidai na jira yan ajin baya" dafe kai malam Habu yai yana kallonta yace "kiyi hakuri Mamana kinji taho taso muje gurin yaya kila yau tunda yaga dake yaji tausayin na ko aro ya bani kudin nan na biya miki" rike hannunta yai suna fita daga gidan suka shiga dayan daya kasance gidan yayansa da sallama ya samu matansa zaune suna gyaran kaji gefe ga yara can suna ta fama da kan saniyar da sukai dafgensa abu yaji ya tsirga masa mai d'aci amma ya daure bayan sun gaisa yace "ko yaya na nan"? Da'kyar suka bashi amsa a wulakance ganin ko shi yayan nasa Ilyah yadda yake masa kenan yana tutture shi babbar matar ce ta budi baki tace "eh kamar dai yana ciki karasa ka duba".
Kukan takaici da damuwa Indo ta fashe dashi tana sake durkusawa sosai ta soma bashi hakuri da batasan laifin datai masa ba ace uba na garine amma ya tsani yarsa ya rikajin duk duniya ba wanda baya son gani sai ita, "baki ji me nace bane zaki tashi a gabana ko saina fasa miki baki" yai maganar yana kai mata harbi da kafa jan kujera Asabe tai tana zama tare da zubo musu ido bakinta har kunne tace "malam kayi hakuri ka kyale ta tana mace idan ka koreta yanzu ina zataje duniya zata shiga karshe ta dirko cikin shege kuma ta dawo ta haife maka shi a gida" a zafafe Balarabe yace "Allah ya sauwake saidai ta nufi gidan marina amma ba gida ba dan ni na sallama ta" "to yanzun dai kayi hakuri na fanshe ta da sharadin zata rika yi mini duk wani aikin gida kama daga shara wanki wanke kwanuka aikin abinci kai inaso Bahijjah ma ta huta Indo ta dawo fita min da abincin sayarwa ta" ta karasa maganar tana sakarwa Indo muguwar harara.
"Wannan shi kike bukata"? Balarabe ya tambaya jiki na mazari d'aga kai Asabe tai "eh hakan ma yayi daga yau ka zama sarki ni gimbiya Indo da Dala bayin mu ko me kace"? Da sauri ya amsa mata "eh na amince na amince ba damuwa dama ai bayin ne aikin jakuna ne ya dace dasu" murmushi Asabe tai yauwa bari a fara yanzu ke Indo dauki bokatin san kije yanzu ki kawo min ruwa ke kuma Dala saiki dora mana tuwo".
Cikin takaici Dala tace "baki isa ba Asabe kinyi kadan a gidan nan kikazo kika sameni dan haka baza ki min mulkin mallaka ba" zaro ido Asabe tai tare da fashewa da dariya tace "au ashe har yanzu da d'an saurin karfin ki Dalah lallai kam na jinjina miki" sai kuma ta hade rai cikin tsawa tana kallon Indo tace "ke kuma ubanki kike jira da bazaki tashi ki fara abinda nace miki ba idan kin debo ga wankin Bahijjah can ya na jiran ki" mikewa Indo tai tana sake goge hawayen fuskarta tadau bokiti tana yin waje.
"Malam gaskiya nifa ban gane anyi gabas da kare ya zanyi magana Dala ta musa min kuma kana jinta baka dau mataki ba ko tsoron ta kake domin labari yazo min idan bana nan nayi tafiya wai wannan abar mai kamar ta'barya har ka zauna tana maka masifa to wallahi bazai yiwu ba gaskiya da sake idan baka gyara ba zan karbe kudade na dana baka kake juyawa" jin barazanar da Asabe ke masa yasa cikin rarrashi yace " kiyi hakuri hakan bata ta'ba faruwa ba karya ake min har nine zan tsaya sauraron wannan abar kibar wata magana kawai ke kadai nake so da Bahijjan ki" dariya Asabe tai "da gaske kake"? Cikin nuna an gama dashi an shanye shi yace "kwarai Asabe da gaske nake " hade rai Asabe tai tana cewa "to ni ban yarda ba baka nuna min a zahiri ba saika saitawa wannan agwagwar matar taka hanya idan kuma ba haka ba daga yau baka sake mora ta sisi kaji na fad'a maka" jiki na rawa cikin tsawa Balarabe yace "ke wai Dalah wacce iriyar bulkuma ce gidahuma bance ki wuce ki fara aiki ba so kike ki silar auren ki yanzun nan kinsan halina sarai ni ba ba'kon ki bane" a damuwance Dalah ta wuce ta barsu a gurin da harara Balarabe ya bita yana cewa "ke kam Dalah kinyi asara mace sai bakin hali yadda fuskar take haka Zuciyar take wuluk da baki da mugun hali nayi da nasanin auren ki Dalah dole ce tasa nake zaune dake amma a juri zuwa rafi wata rana tulu zai fashe" yana fadin haka ya fita yana sake babbaka fad'a kamar bazai ta'ba shiru.
Yayin da Asabe tasa Dalah a gaba tana sheka dariya kamar zata kifa harda hawaye tace "to ya kikaji irin salon nawa Dalah kenan na fad'a miki baza ki iya ja dani ba bakisan wace ni Asabe ba suna a kawai kikeji amma daga yanzu ina fata sunan ya zauna a Zuciyar ki har abada domin nayi alkawarin saina 'kuntata miki daga yanzun kin fara shan dandanon azaba dake da 'yarki a hannu na mu zuba mu gani waye zai nasara saina kaiki kasa" dagowa Dalah tai tana kallon Asabe da jin maganganun da take fad'a saidai batai mamaki domin tun lokacin da Balarabe zai aureta mutane ke tausaya masa suna koka mata cewa zai auro mata masifa Asabe tsiya ce mai lasisi gashi kuwa abinda ake fad'i ya tabbata.................... "Meye kike kallo na maiya"? Muryar Asabe ce ta katse mata tunani danne damuwa da bacin ran dake cin ta Dalah tai tana kankaro murmushi tace "Allah ya shirye ki domin ke abar tausayi ce daga ranar da duniya ta juya miki baya zaki bayani" dariya dariya Asabe tai "ahayye nanaye yau ake yinta lallai kam Dalah kina lokacin yanzu har kece zakice kina tausayin wani? Ta fad'a tanai mata wani kallo na tsantsan rashin mutunci Sai kuma ta sake bushewa da dariya tana cewa amma kinci abinci a kanki shin kina duba mudubi kuwa kodan ina za'a samu darajar mudubi bayan komai bai wadata ba har kice zaki wa wani gori tirrrrr anji kunya 'yar ba'ki ai labari ya same ni tun bayan na auri Balarabe cewa ke maiya ce yar mayu jikar mayu iyayen ki korar maiya akayo musu daga wani tsinannan kauye suka dawo nan suka addabe mu wato da dare baban ki har kura yake zama ko🙊? Daidai Indo ta shigo da bokatin ruwa ta dire asabe dake binta da kallon banza tace bance kayan Bahijjah zaki wanke ba yar gwana jikar maiya Asabe take Aiko mata da mugayen kalaman da take fad'awa uwar ga tsinuwar Balarabe a kanta kuka kawai take kamar ranta zai fita bangare na Zuciyar na adduar Allah ya kawo mata sauyi cikin rayuwarta.
Amatu na zaune a kofar d'akinsu tana duba wani littafin addua Jamila na gefenta tana gyarawa A'i kayan miyar abincin saidawar su ta kalli yadda Aisha ta shigo jikinta duk a jike shakaf da gumi alamar daga aikatau take tana haki da sassarfa ta iso inda suke tana zama sai haki tace cikin tausayawa Jamila yace "sannu Aisha Allah dai ya rufa mana asiri ya kawo mana canji a rayuwar mu" murmushin karfi hali Aisha tai tana cewa "amin Amatullahi me kike dubawa ne"? Murmushi Amatu tai batare data d'ago ba domin ita ba ma'abociyar 'kure mutum da kallo bace tace "sannu Aisha kiji yadda kike haki fa dan Allah idan aiki yafi karfin ki kina ragewa wannan gajiya fa da kuke dibawa jikin ku zata tambaye ku sai lokacin tsufa" fuskar Aisha cike da damuwa tace "to ya zanyi Amatu rashi ne yasa nasan da baban mu nada shi duk haka bazata faru ba" sauke ajiyar zuciya Amatu tai tare da jinjina kai tace "haka ne amma dan Allah a rika ragewa aikin na yawa" dariya Aisha tai tana cewa "shikenan babbar aunty za a kiyaye kaka mai kamar uwa hajiya Hauwa's mai zamani" dariya sukai Amatu na mata hararar wasa tace "meye na Kiran suna na haka babu ko dan kara"? Har lokacin fuskar Aisha da fara'a tace " kakar mu na tuno duk da bamu Santa ba Allah sarki hajiya Hauwa naji mutuwar 'yar tsohuwar nan" maida hankalin ta kan littafi Amatu tai tana cewa "to ta zamuyi wanda ya fimu sonta ne ya karbeta duk wata kulawa da kauna da zamu gwada mata bayan nasa ne shike iko da kowa" sauke ajiyar zuciya Aisha tai tana kallon Saude data fito a d'aki tana mata kallon mamaki na ke kuma yaushe kika shigo mikewa tai tare da nufar ta yayin da Jamila ma ta mike tana daukar kayan miyar ta tafi gidan ni'ka.
Shiru Amatu tai tana kallon kowa da komai gida babban gida amma yanayin tsarinsa da gyara gashi babanta nada dangi amma duk laifinsa suke gani wai ya zauna kara zube ba sana'a yasa rashin zuciya gashi ya tara iyalai shiru tai ta nutsa cikin tunani lokacin da baban ta yaje gurin yayansa ya bashi kud'i zai biya mata ta zana jarrabawa ya hana dan rufe ido tai maganganun da kawu Ilyah ya fad'awa babanta na mata yawo a kunne daga lokacin data tambayi kudin jarrabawar.
Cikin mamaki shigowar malam habu ganin Amatu zaune tana kuka yasa ya karaso da sauri yana d'ago ta tare da goge mata hawaye cikin lallahi yace "Mamana kukan me kike ba na raka ki har makaranta ba meyasa kika dawo" Amatu na shashshekar kuka tace "baba wai malamin yace ban bada kud'i ba wannan shekarar ma bazan zana jarrabawa ba saidai na jira yan ajin baya" dafe kai malam Habu yai yana kallonta yace "kiyi hakuri Mamana kinji taho taso muje gurin yaya kila yau tunda yaga dake yaji tausayin na ko aro ya bani kudin nan na biya miki" rike hannunta yai suna fita daga gidan suka shiga dayan daya kasance gidan yayansa da sallama ya samu matansa zaune suna gyaran kaji gefe ga yara can suna ta fama da kan saniyar da sukai dafgensa abu yaji ya tsirga masa mai d'aci amma ya daure bayan sun gaisa yace "ko yaya na nan"? Da'kyar suka bashi amsa a wulakance ganin ko shi yayan nasa Ilyah yadda yake masa kenan yana tutture shi babbar matar ce ta budi baki tace "eh kamar dai yana ciki karasa ka duba".