Sashe 103
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"kwarai na tabbata wannan mutumin d'an arziki ne zai baka koda ace bakai masa komai ba kuma ka gwada ka gani Alhaji amma nikam ina maka kwadayin auren yarinyar haka nan bansan miyasa ba dan Allah kada kace a'a ka sameshi wallahi shawara mai kyau ce kaji"?.
Shiru yai cikin nazari da tunani shikam yana jin kunyar tunkarar malam Habu da wannan babbar bu'kata duk da yasan bazai ta'ba hana shiba amma dai gaskiyar magana bazai iyaba yana jin nauyi...........
Muryar Hajiya Aisha ce ta katse masa tunani "Alhaji kabar 'bata lokaci akan tunani Allah da gaske nake magana komai da nake fad'a maka kuma kaga auren mutum biyu zaka nema domin d'azun nan shalele yace min shikuma Jamila 'kanwarta yake so kaga shikenan fad'uwa tazo daidai da zama".
Kasa magana ma shikam Alhaji Musa yai sai zulumi da tunanin ta yadda zai 'bullowa al'amarin yake iya Hajiya Aisha ke magana tana sake lalla'ba shi da bashi qwarin gwiwa akan auren domin taga alamar har lokacin baiyi accepted din nasa auren da Asma'un ba.
Bayan sati biyu Amatu tana zaune a dakinsu babu kowa ita kad'ai ce tana duba laptop d'inta kamar kullum saidai yau aikin assignment take ba bincike ba ba zato kwatsam taji saukar abu a d'akin kamar zai zubar da gidan gabadaya yadda taji dirarsa da mugun 'karfi a firgice ta d'ago tana kallon gurin arba idonta yai da 'yan mata biyu tsaye da kayan tsafi jawur a jikinsu fuskarsu sun fanteta da kaloli sun zagaye idanuwansu da ba'kin kwalli kome saninka dasu bazaka ganesu ba a wannan shigar (Khimiyyah ce da Hudayyah🤔) suna tsaye sun zubo mata ido kamar yadda itama take kallon nasu cike da tsananin mamaki a ranta kafin batare da jin wani tsoro ko d'ar ba tace.
"Su waye ku daga ina kuke me kuke nema anan meya kawo ku"?.
Kallon juna sukai suna murmushi sannan suka jinjina kai kallonta Hudayyah tai tana cewa "ke kada kiso sanin komu su waye domin zaki hallaka kin gane ba wannan ya kawo mu gurin kiba idan da ace zuwa mukai don kisanmu ai bazamu 'boye miki siffarmu ba".
Matsowa kusa Khimiyyah tai tana cewa "ke bari kiji abinda ya kawo mu gurin ki munzo ne muyi miki gargad'i na farko kuma na karshe akan shishshigin da kikeyi kina neman jefa rayuwarki cikin risks indai baki saurara kin dakata haka kin nutsu kin d'auke hankalinki akan muba to Ina mai tabbatar miki da an kusa kaiki kabari domin duk wanda yasan sirrinmu bai kamata ya rayu ba duk mai son gano wani dake cikin 'kungiyarmu kashe shi muke mu ma'kiyan kashe shi muke dan haka kada ki kuskura tsautsayi yasa ki sake bincike a kanmu zakiga sakamakon taurin kai sannan idan muka tafi kika fad'awa wani zakiga 'karshen ki abu na karshe mi'ko min laptop din nan" Khimiyyah ta fad'a tana mi'ka mata hannu.
Wani banzan kallo Amatu tai mata tana cewa "waye zai baki laptop din amma dai ba dani kike ba domin Wallahi koda uwarki kike tafiya duk inda zakije bazan bayar ba kin gane baki da fuskar da za'a kalla ki razana mutum balle har ki sanya tsoro yayi tasiri a raina maza maza kuyi gaggawar barin nan kafin kuga yadda ake hauka domin na fiku d'anyan kai duk abinda kukaje a ranku na zarta ku".
Baki bud'e suke kallonta mamaki ya cikasu wato dai ta nuna jarumtakarta a fili ta cancanti jinjina wannan da alama za'a fafata da ita to su yanxu me zasuwa Prof Jibril daya ce kada su koma daba laptop d'inba zasuji kunya su biyu kuma suna cikin kayan tsafi su kasa yi da mutum d'aya kuma mace kallon Hudayyah Khimiyyah tai da ido sukai magana kafin cikin zafin nama Khimiyyah tayi wuf zata d'auke laptop din wanda dama Amatu already a ankare take dasu tana cikin shiri itama a zafafe ta janye laptop din tana d'aga wata kwalbar lemo dake kusa da ita da dukkan qarfinta ta dokawa Khimiyyah a hannu wanda saida kwalbar ta fashe tuni jini ya fara zuba ihu Khimiyyah tai cike da azaba Hudayyah data zaro ido da sauri ta matso ganin jinin har tsartuwa yake yasa ta sakarwa Amatu wani micijin🐍 tsafi yayo kan wuuuuuu baki a bud'e mi'kewa tsaye Amatu tai tare da d'aukar wani sanda dake jingine ta d'aga zata kwad'awa micijin ya 6ace 'bat huci Hudayyah cikin kunar tana kallon Khimiyyah dake du'ke tana lashe jininta daya zuba kafin ta d'ago tana kallon Amatu wacce ke ri'ke da sanda zatai magana Amatu ta d'aga mata hannu.
"Kinga malamai kun ishe shi wannan kuje ku nemi mahauci irin ku wanda baida aikin yi kun gane mayu kawai ke ki daina lashe wannan jinin are you a witch"? (Mayya) nace ku mayu ne to kun ganni nan ni Hauwa'u Abubakar nafi qarfinku.
Mi'kewa Khimiyyah tai a fusace tana tada tsafi suka sake yowa kanta duk su biyun daidai Binta ta karaso kofar d'akin tana cewa.
"Mamar gida anan nake jin ihu ne"?.
Da sauri su Khimiyyah suka 'bace sai d'an haya'ki kadan shigowa Binta tai ganin haya'ki yasa tace "wannan hayakin kuma daga Ina ko wutar da A'i ta hura a kitchen ce dama yana shigo muku baku fad'a ba"?.
Kai Amatu ta girgiza tana cewa "a'a baya shigowa".
"Oh to ina ganin yau din ko iska ce take kad'oshi da yake yau an tashi da iskar ai shikenan me kikeyi ne duk muna waje yau harda su Asma'u basuje aiki ba Hajiya tayi tafiya ga kaji can malam ya kawo munata gyarawa kar ace bakya gurin ki fito".
To Amatu tace bayan Binta ta fice ta tsaya kallon d'akin komai ya koma tsaf tsaf a gyare kamar babu abinda ya faru cafd'i hatta kwalbar data fasa ta koma yadda take gudarta🍶 jinin ma babu tsaki taja tana cewa.
"Humm dama ai tun daga ganin sunan wannan tsinanniyar 'kungiyar nasan bata mutanen arziki bace harda jini kuke sha waini zaku nunawa fear and fear barazana in action😂? sai kuma tayi dariya tana cewa "wallahi ina daidai daku na mu zuba mu gani saina kawo baku mamaki nice karshen zaluncinku banzaye kawai ma'karyatan banza da wasu tatsuniyoyin ku na rainin hankali mtswwwwogon tsuka tana d'aukar laptop d'inta tayi waje.
GIDAN NURAIN
Sosai Zainab ta kwantar da hankalinta kamar auren Nurain d'in baya cin raita amma tayi mamakin yadda ta iya dannewa bata nuna masa ba sai wata sabuwar soyayya da suka bud'e babinta suke zubawa juna a bangare guda kuma ta roki alfalmar bayan biki tana so 'kanninta Mimah da Meelat zasu Dan tsaya suyi mata gyare gyare a part d'inta da nasa dan bataso yar aiki taga asirin su da kuma goge gogen kayan kitchen kuma ya amince mata a ranar tayi waya dasu tace suzo Nurain shima yana da 'kanwa gud'a d'aya sunanta Mimih da kuma 'yar riko sunanta Meenah taso Nurain amma ya'ki tayi bi tayi kuka ya'ki aurenta tana bala'in kishi da Zainab ana haka taji wai zai auro yar qauye humm ta shiga d'imuwa ta shiga damuwa da kukanta ta samu Mom din Nurain amma ta bata ha'kuri tace itama Allah zai kawo mata.
Mimih itace suke uwa daya uba d'aya da Nurain akwai ta da iya wulakanci salo-salo 'yar rainin hankali ce ta bugawa a jarida Zainab ma da take 'yar cikin birni kuma wayayyiya sun goga da ita kafin su daidata balle wannan da zata zo daga qauye tunda taji zai kara aure ga daga inda za'a kawo amaryar tace a'a yaya ba aure zaiyi soko zaiyi kamarsa ya auri village girl heyeee inaa girma ya fad'i rakumi🐪 yasha ruwan kaji🐓 tun bataga amaryar ba ta d'au 'kwarzaba ta zuba mata kullum bata da aikin sai kushe auren balle Meenah da take jin kamar tayi hauka dan takaici Mimih kam har tacewa Dad tayi ya hana Nurain auren ya auri Meenah tunda ta dad'e tana sonshi Daddy shikam yace ba ruwansa ra'ayin sane Mimih har daina kula Nurain tai in yazo gidan sai ta ri'ka kakkare hanci har abun ya bashi haushi ya tambaye ta uban me take rufewa hanci tace masa wai warin karkara yake🙊😂.
🥕OSUN🥕
______Yau da wuri Dauda zai tafi gurin hayar mashin d'in sa kamar yadda ya saba akwai kayan abinci komai a aje sai kud'i mahad'i dazai bayar ya baiwa Indo dubu d'aya akan tayo cefanan kayan miya sannan ya tafi saida ya riga ya dad'e da tafiya wani tunani yazo mata tun shekaran jiya tace masa zataje kitso yace to kuma bataje ba dan haka tunda taga dai ta tambaye shi sai kawai tayi wanka ta shirya da nufin idan anyo mata kitson sai tayo cefanan a hanya dama maman Niseh ce take musu markad'e.
Lokacin data gama shiri ta fito tsaye tayi a kofar d'akin maman Amrat tana kiran sunanta jin shiru yasa tayi tunanin ko ta koma barcin safe ne sai bata tashe taba kawai ta tafi dama tunda ta tambayi Dauda yayi mata kwatance a anguwar ne kuma yana yawan fita da ita yawo ya nuna mata gurare ta sani saboda wata rana.
Tayi sa'a kuwa matar ta gama aikinta na safe tana zaune suna zance da 'yar budurwa wacce ke harhad'a kayan da take abubuwan saidawa na yara irinsu tsami gaye tuwon madara carbin malam alawar Kano da Jigawa dasu aya da sauran su sallama Indo tai musu suka amsa mata cikin fara'a tare da bata gurin zama suka gaisa matar ta kalleta tana cewa.
"Ehem madam ko kaine wanda kuka tare mana kwana baya da dad'ewa anan"?.
Kai Indo ta d'aga " eh nice".
"Ayya haayy na ganka ranar walay da husband naka kun biyo mana tanan kunje anguwa ko"?.
Nan ma kai Indo ta d'aga mata tana cewa "eh munje anguwa ne".
"Ok ok nagane kana wajen gidan madam maman Niseh mai markade ko meyene sunanka"?.
Ita Indo dariya ma abun yake bata qarfi da yaji ta koma namiji tana murmushi tace "suna na Aisha Indo".
"Ayya sunan sofi ni Aysha sunan kaka nace shine ya haife uwana amma ya rasu da dadewa ai mai suna aysha akwai kirki walay".
Shiru yai cikin nazari da tunani shikam yana jin kunyar tunkarar malam Habu da wannan babbar bu'kata duk da yasan bazai ta'ba hana shiba amma dai gaskiyar magana bazai iyaba yana jin nauyi...........
Muryar Hajiya Aisha ce ta katse masa tunani "Alhaji kabar 'bata lokaci akan tunani Allah da gaske nake magana komai da nake fad'a maka kuma kaga auren mutum biyu zaka nema domin d'azun nan shalele yace min shikuma Jamila 'kanwarta yake so kaga shikenan fad'uwa tazo daidai da zama".
Kasa magana ma shikam Alhaji Musa yai sai zulumi da tunanin ta yadda zai 'bullowa al'amarin yake iya Hajiya Aisha ke magana tana sake lalla'ba shi da bashi qwarin gwiwa akan auren domin taga alamar har lokacin baiyi accepted din nasa auren da Asma'un ba.
Bayan sati biyu Amatu tana zaune a dakinsu babu kowa ita kad'ai ce tana duba laptop d'inta kamar kullum saidai yau aikin assignment take ba bincike ba ba zato kwatsam taji saukar abu a d'akin kamar zai zubar da gidan gabadaya yadda taji dirarsa da mugun 'karfi a firgice ta d'ago tana kallon gurin arba idonta yai da 'yan mata biyu tsaye da kayan tsafi jawur a jikinsu fuskarsu sun fanteta da kaloli sun zagaye idanuwansu da ba'kin kwalli kome saninka dasu bazaka ganesu ba a wannan shigar (Khimiyyah ce da Hudayyah🤔) suna tsaye sun zubo mata ido kamar yadda itama take kallon nasu cike da tsananin mamaki a ranta kafin batare da jin wani tsoro ko d'ar ba tace.
"Su waye ku daga ina kuke me kuke nema anan meya kawo ku"?.
Kallon juna sukai suna murmushi sannan suka jinjina kai kallonta Hudayyah tai tana cewa "ke kada kiso sanin komu su waye domin zaki hallaka kin gane ba wannan ya kawo mu gurin kiba idan da ace zuwa mukai don kisanmu ai bazamu 'boye miki siffarmu ba".
Matsowa kusa Khimiyyah tai tana cewa "ke bari kiji abinda ya kawo mu gurin ki munzo ne muyi miki gargad'i na farko kuma na karshe akan shishshigin da kikeyi kina neman jefa rayuwarki cikin risks indai baki saurara kin dakata haka kin nutsu kin d'auke hankalinki akan muba to Ina mai tabbatar miki da an kusa kaiki kabari domin duk wanda yasan sirrinmu bai kamata ya rayu ba duk mai son gano wani dake cikin 'kungiyarmu kashe shi muke mu ma'kiyan kashe shi muke dan haka kada ki kuskura tsautsayi yasa ki sake bincike a kanmu zakiga sakamakon taurin kai sannan idan muka tafi kika fad'awa wani zakiga 'karshen ki abu na karshe mi'ko min laptop din nan" Khimiyyah ta fad'a tana mi'ka mata hannu.
Wani banzan kallo Amatu tai mata tana cewa "waye zai baki laptop din amma dai ba dani kike ba domin Wallahi koda uwarki kike tafiya duk inda zakije bazan bayar ba kin gane baki da fuskar da za'a kalla ki razana mutum balle har ki sanya tsoro yayi tasiri a raina maza maza kuyi gaggawar barin nan kafin kuga yadda ake hauka domin na fiku d'anyan kai duk abinda kukaje a ranku na zarta ku".
Baki bud'e suke kallonta mamaki ya cikasu wato dai ta nuna jarumtakarta a fili ta cancanti jinjina wannan da alama za'a fafata da ita to su yanxu me zasuwa Prof Jibril daya ce kada su koma daba laptop d'inba zasuji kunya su biyu kuma suna cikin kayan tsafi su kasa yi da mutum d'aya kuma mace kallon Hudayyah Khimiyyah tai da ido sukai magana kafin cikin zafin nama Khimiyyah tayi wuf zata d'auke laptop din wanda dama Amatu already a ankare take dasu tana cikin shiri itama a zafafe ta janye laptop din tana d'aga wata kwalbar lemo dake kusa da ita da dukkan qarfinta ta dokawa Khimiyyah a hannu wanda saida kwalbar ta fashe tuni jini ya fara zuba ihu Khimiyyah tai cike da azaba Hudayyah data zaro ido da sauri ta matso ganin jinin har tsartuwa yake yasa ta sakarwa Amatu wani micijin🐍 tsafi yayo kan wuuuuuu baki a bud'e mi'kewa tsaye Amatu tai tare da d'aukar wani sanda dake jingine ta d'aga zata kwad'awa micijin ya 6ace 'bat huci Hudayyah cikin kunar tana kallon Khimiyyah dake du'ke tana lashe jininta daya zuba kafin ta d'ago tana kallon Amatu wacce ke ri'ke da sanda zatai magana Amatu ta d'aga mata hannu.
"Kinga malamai kun ishe shi wannan kuje ku nemi mahauci irin ku wanda baida aikin yi kun gane mayu kawai ke ki daina lashe wannan jinin are you a witch"? (Mayya) nace ku mayu ne to kun ganni nan ni Hauwa'u Abubakar nafi qarfinku.
Mi'kewa Khimiyyah tai a fusace tana tada tsafi suka sake yowa kanta duk su biyun daidai Binta ta karaso kofar d'akin tana cewa.
"Mamar gida anan nake jin ihu ne"?.
Da sauri su Khimiyyah suka 'bace sai d'an haya'ki kadan shigowa Binta tai ganin haya'ki yasa tace "wannan hayakin kuma daga Ina ko wutar da A'i ta hura a kitchen ce dama yana shigo muku baku fad'a ba"?.
Kai Amatu ta girgiza tana cewa "a'a baya shigowa".
"Oh to ina ganin yau din ko iska ce take kad'oshi da yake yau an tashi da iskar ai shikenan me kikeyi ne duk muna waje yau harda su Asma'u basuje aiki ba Hajiya tayi tafiya ga kaji can malam ya kawo munata gyarawa kar ace bakya gurin ki fito".
To Amatu tace bayan Binta ta fice ta tsaya kallon d'akin komai ya koma tsaf tsaf a gyare kamar babu abinda ya faru cafd'i hatta kwalbar data fasa ta koma yadda take gudarta🍶 jinin ma babu tsaki taja tana cewa.
"Humm dama ai tun daga ganin sunan wannan tsinanniyar 'kungiyar nasan bata mutanen arziki bace harda jini kuke sha waini zaku nunawa fear and fear barazana in action😂? sai kuma tayi dariya tana cewa "wallahi ina daidai daku na mu zuba mu gani saina kawo baku mamaki nice karshen zaluncinku banzaye kawai ma'karyatan banza da wasu tatsuniyoyin ku na rainin hankali mtswwwwogon tsuka tana d'aukar laptop d'inta tayi waje.
GIDAN NURAIN
Sosai Zainab ta kwantar da hankalinta kamar auren Nurain d'in baya cin raita amma tayi mamakin yadda ta iya dannewa bata nuna masa ba sai wata sabuwar soyayya da suka bud'e babinta suke zubawa juna a bangare guda kuma ta roki alfalmar bayan biki tana so 'kanninta Mimah da Meelat zasu Dan tsaya suyi mata gyare gyare a part d'inta da nasa dan bataso yar aiki taga asirin su da kuma goge gogen kayan kitchen kuma ya amince mata a ranar tayi waya dasu tace suzo Nurain shima yana da 'kanwa gud'a d'aya sunanta Mimih da kuma 'yar riko sunanta Meenah taso Nurain amma ya'ki tayi bi tayi kuka ya'ki aurenta tana bala'in kishi da Zainab ana haka taji wai zai auro yar qauye humm ta shiga d'imuwa ta shiga damuwa da kukanta ta samu Mom din Nurain amma ta bata ha'kuri tace itama Allah zai kawo mata.
Mimih itace suke uwa daya uba d'aya da Nurain akwai ta da iya wulakanci salo-salo 'yar rainin hankali ce ta bugawa a jarida Zainab ma da take 'yar cikin birni kuma wayayyiya sun goga da ita kafin su daidata balle wannan da zata zo daga qauye tunda taji zai kara aure ga daga inda za'a kawo amaryar tace a'a yaya ba aure zaiyi soko zaiyi kamarsa ya auri village girl heyeee inaa girma ya fad'i rakumi🐪 yasha ruwan kaji🐓 tun bataga amaryar ba ta d'au 'kwarzaba ta zuba mata kullum bata da aikin sai kushe auren balle Meenah da take jin kamar tayi hauka dan takaici Mimih kam har tacewa Dad tayi ya hana Nurain auren ya auri Meenah tunda ta dad'e tana sonshi Daddy shikam yace ba ruwansa ra'ayin sane Mimih har daina kula Nurain tai in yazo gidan sai ta ri'ka kakkare hanci har abun ya bashi haushi ya tambaye ta uban me take rufewa hanci tace masa wai warin karkara yake🙊😂.
🥕OSUN🥕
______Yau da wuri Dauda zai tafi gurin hayar mashin d'in sa kamar yadda ya saba akwai kayan abinci komai a aje sai kud'i mahad'i dazai bayar ya baiwa Indo dubu d'aya akan tayo cefanan kayan miya sannan ya tafi saida ya riga ya dad'e da tafiya wani tunani yazo mata tun shekaran jiya tace masa zataje kitso yace to kuma bataje ba dan haka tunda taga dai ta tambaye shi sai kawai tayi wanka ta shirya da nufin idan anyo mata kitson sai tayo cefanan a hanya dama maman Niseh ce take musu markad'e.
Lokacin data gama shiri ta fito tsaye tayi a kofar d'akin maman Amrat tana kiran sunanta jin shiru yasa tayi tunanin ko ta koma barcin safe ne sai bata tashe taba kawai ta tafi dama tunda ta tambayi Dauda yayi mata kwatance a anguwar ne kuma yana yawan fita da ita yawo ya nuna mata gurare ta sani saboda wata rana.
Tayi sa'a kuwa matar ta gama aikinta na safe tana zaune suna zance da 'yar budurwa wacce ke harhad'a kayan da take abubuwan saidawa na yara irinsu tsami gaye tuwon madara carbin malam alawar Kano da Jigawa dasu aya da sauran su sallama Indo tai musu suka amsa mata cikin fara'a tare da bata gurin zama suka gaisa matar ta kalleta tana cewa.
"Ehem madam ko kaine wanda kuka tare mana kwana baya da dad'ewa anan"?.
Kai Indo ta d'aga " eh nice".
"Ayya haayy na ganka ranar walay da husband naka kun biyo mana tanan kunje anguwa ko"?.
Nan ma kai Indo ta d'aga mata tana cewa "eh munje anguwa ne".
"Ok ok nagane kana wajen gidan madam maman Niseh mai markade ko meyene sunanka"?.
Ita Indo dariya ma abun yake bata qarfi da yaji ta koma namiji tana murmushi tace "suna na Aisha Indo".
"Ayya sunan sofi ni Aysha sunan kaka nace shine ya haife uwana amma ya rasu da dadewa ai mai suna aysha akwai kirki walay".