Sashe 96
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Kai anan garin a ina ake sayar da abinci"?.
Kallonsa yaron yai yana cewa "babu inda ake sayarwa saidai kaje gidan cin abinci".
Kallon bokitin hannun nasa malam Habu yai ga kuma fork da plate🍽️ dan haka yace "kai me kake sayarwa"?.
Amsa yaron ya bashi "gurasa ce mai 'kuli amma ta kare saina d'ebo wata zaku saya"?.
Kai malam Habu ya d'aga "eh zamu saya idan ka d'ebo ka kawo mana kayi sauri yanzu" to yace yana yin gaba ba'a dad'e ba ya dawo ya ciko bokitin yace guda d'aya d'ari haka suka saye masa ita du saida bokitin ya koma gida.
Har bayan sallar isha suna nan zaune shiru shiru sunata jiran drivan nan daya kawosu ya dawo ya fad'a musu ko an samu amma har dare yayi nisa kusan karfe sha biyu ba labari harsun cire rai saigashi yazo da mota yayi parking bayan ya fito yace.
"Kayi hakuri malam wallahi ba mantawa nai daku ba nayi kiransa tun d'azu uzirin gida ya hanani dawowa kaga munyi waya dashi yace min babu sauran gidaje a hannunsa kayi hakuri saidai zanyi kokari na lalubo muku wani amma kafin nan ku shiga kangon nan ku aje kayanku nasan mai gidan sunansa Alhaji Musa mutumin kirki kafin dai na samo muku gidan hayar da zaku zauna nasan zai barku".
Kai malam Habu ya d'aga yana cewa "to shikenan na gode Allah ya saka da alkhairi" mi'kewa yai yana d'iban kayan suna shiga dashi sannan ya shikuma ya tafi haka suka kwana a kangon amma saboda tsoron nan ba garinsu bane basusan ya tsarinsa yake ba kada su ta'ba kayan wanda zai wulakanta su yasa tun kiran sallar farko na asuba malam Habu ya tashesu bayan yayi alwala ya fita xuwa masallaci tare da basu umarnin idan sunyi sallah kada su zauna su d'ebo kayan su dawo waje kada mai gidan yazo musu zuwan bazata kamasun dayai a ciki ya jawo musu matsala shiba wani kud'i ke gareshi ba.
Aiko suna ana shiga sallah bayan anyi sallama wuta-wuta sukai suka fita da komai waje kamar yadda ya umarcesu sai a wajen suka yi 'yan addu'o'i gari yayi haske malam Habu ya dawo dukka suka gaidashi bakin A'i da baya shiru ta kalleshi tana cewa.
"Oh ni A'i na fad'o daga sama na zarce rijiya gaba dubu Malam muna d'an zaman mu a gida cikin rufin asiri Rakiya tayi mana sutura ta bamu gurin zama haka kawai ka tashi tafiya batare da kasan inda zakaje ba kuma kaiba gurin kowa kazo ba ka kawomu tsakiyar birni ka ajemu ko tsoron azo a sace mu bakayi yanzu kila wani ya ganmu rakwacam har mu takwas kila yana nan yana fakon mu sai dare yayi yazo ya yashemu da d'ai d'ai wallahi nidai da ido d'aya da rabi nayi barcin jiya saboda naji ance birni ana yankewa mutane kai wai dama haka Kanon take da kyau tabdijan gaskiya dole su yaya Ilyah da Bara'atu su dage akan Nafisa ta auri d'an birni wa ya'ki dad'i umm kalli dan Allah Malam gidaje masu kyau ai ban ta'ba fitowa daga 'kauyen mu naje wani wuri ba kice muba rayuwa muke ba muna binne a kasa nifa idan ba yanzu ba ko a mafarki ban ta'ba zuwa Kano ba gashi dai a jihar nake kodan muna nisa dasu kuma cikin lungu sosai kai gaskiya garin yayi Masha Allah" ita kad'ai A'i sai sambatu take babu wanda yace mata ta tafar sau'ke suna zaune zaman jiran wannan yaron na jiya daya kawo musu gurasa suka saya ga drivan daya kawosu jiya shima yace zai dawo da safe amma shiru har Allah ya kawo wannan yaron mai gurasa kamar yadda yace musu da safema in suna so zai kawo su saya kud'insa malam Habu ya bashi suka juye fal babban bokiti sannan ya basu plate suka rarraba kowa ya karya yasha ruwa kafin yaron ya tattare kayansa yayi hanyar gida yana murnan zuwan wadannan ba'ki🙃.
Suna ta zaune dai suga ta inda driver zai 'bullo yazo ya fad'a musu idan ya samo musu gidan hayar amma shiru babu shi babu alamarsa sauke ajiyar zuciya malam Habu yai yana girgiza kai tare da d'an rufe ido a ransa yana tunanin indai yau drivan nan bai zo ya fad'a musu an samu gidan ko ba'a samu ba tofa baza suci gaba da zama anan ba duk dare yau sai sun sauya anguwa ko Allah zai basu rabons............................
A firgice Malam Habu ya bud'e ido sakamakon jin 'kara har baisan lokacin daya mi'ke tsaye daga zaune ba kallon motar da tazo tai parking gaf dasu yai amma baiga mutumin ciki ba saboda duhun glass d'in salati ya fara a cikin ransa tuni yaji hankalin sa ya tashi karfa ace mai wannan gidan ne yazo to yanzu me zasuce masa¿.....................
Jin an sake horn yasa Malam Habu d'agowa daga tunanin da yake ya kallo motar zuciyarsa na harbawa da karfi sosai daidai an bud'e kofar yaga wani lafiyayyan Alhaji ya fito yasha wanka cikin shadda mai tsada ga d'oneniyar hula wacce taji sitati tasha kari sannan takalmi👞 da agogo⌚ na ma'kudan kud'ad'e kai harda zobe💍 humm kawai siffarsa a kirashi sugar Dad☺️ sannan beauty no filter😃 haka yake ta ko'ina cass kuma kyakkyawa ne mai hanci ga fari ba irin alhazawan nan ne da suka aje tumbi kamar kayan wanki ba😳🤐.
Ganin ya kallesu yana dafe da murfin motar yasa jikin malam Habu ya d'an fara rawa neman jarumtarsa yake amma ya kasa saboda ganin irin kallon da mutumin ke musu da yake su matane har sufi malam Habun rud'ewa da hannu mutumin ya yafito malam Habu yana masa nuni da yaje gurin sa,.
Da'kyar Malam Habu dake tsaye daskare guri d'aya ya d'aga takalminsa ya fara tafiya zuwa inda Alhajin yake kamar mai ciwon 'kafa haka yake janta yana d'ari-d'ari da d'ar-d'ar d'in tsoro😞😥 saida ya kusa dashi sannan yaja ya tsaya murmushi mutumin yai yana cewa.
"Haba kai kuwa aboki karaso man ba wani abu bane magana zamuyi matso kusa kada ka damu".
Sauke numfashi Malam Habu yai jin abinda yace masa sai sannan ya d'anji hankalin sa ya lafa amma dai bai kwanta ba karasawa yai zai dur'kusa ya gaida dashi mutumin ya d'ago kafad'arsa da sauri yana cewa.
"A'a basai ka gaida dani a kasa ba aboki bani hannunka mu gaisa🤝" ya fad'a yana ri'ke hannu malam Habu sukai musabaha yace.
"Barka da asuba yakake"?.
Cikin jin sassauci malam Habu yace "lafiya alhamdulillah".
Kai ya d'aga masa yana cewa "hakan nada kyau dama tambaya ce zanyi maka idan bazaka damu ba sakamakon nayi mamakin ganinku har yau anan a layi kamar marasa gata ga mata da yara kuma 'yan mata babu dad'i jiya nazo na wuce tanan bayan na dawo daga office zan tafi gida na ganku a zaune kuma yauma na sake ganinku a nan d'in dai baku tafi ba shine nace ko bakusan kowa bane ku ba'ki ne ko"?.
Kai Malam Habu ya d'aga yana cewa "eh gaskiya mu ba'ki ne daga wani qauye muka taso nazo nan ne domin na kama hayar gida kuma nayi sana'a to munyi magana da direban motar daya kawo mu cewa zai laluba mana gidan haya amma shiru babu alamarsa tun jiya daya tafi yace mu shiga wannan kangon mu kwana kafin yau duk da shi yasan mai kangon amma mufa muna ciki a zaune bamu sanshi ba yazo duba gidansa ya ganmu a ciki kuma ba tambayar sa mukai ba shiyasa gari yana wajewa tun asuba nace mu fito waje kada Mai gidan yazo ya samemu a ciki nan ba garinmu bane bamusan ya tsarikansu suke ba ko abun laifi baya yawa muyi abinda zaija mana d'auri"?.
Murmushi mutumin yai yana cewa "kai daga kwana sai a d'aureku kamar wanda sukai sata? To kaga kwantar da hankalinka wannan kangon bana kowa bane nawa ne mallaki nane saiku saki jiki amma tunda gidan haya kake nema inada gidaje masu tarin yawa wanda ba mutane a ciki wasu kuma da mutane sannan hawa hawan kud'i ne sai wanda kake so na daidai qarfin ka idan kuma nasa muku murfin kofa a wannan d'in tunda na ganka da iyalai sosai kuma dama shima wannan d'in haya zansa amma me kace a shekara zaka iya biyan dubu d'ari biyu da hamsin"?.
Da sauri malam Habu ya d'aga kai yana cewa "eh na amince Alhaji kwarai zan biya insha Allahu za'a samu Allah ya dafa min Wallahi nayi maka alkawari zanyi kokari na biyaka lokacin da kake bukata dan Allah Alhaji ka amince"?.
"Ok shikenan karka damu za'a sa muku murfi yau tunda dama shi ya rage anyi filasta an d'anyi fenti sai kuyi maleji ko"?.
Kai Malam Habu ya d'aga "eh Alhaji na gode sosai Allah ya biyaka da mafificin alkairi".
Murmushi yai yana cewa "Amin amma mene sunan malamin"?.
"Sunana Malam Habubakar".
Hannu Alhajin ya mi'ko masa suka sake gaisawa yana cewa "alright u're welcome Malam Abubakar ni kuma sunana Alhaji Musa sannan nima anan anguwar nake ta by pass d'inku shikenan yanzu zan tafi office I don't want to be late but idan na dawo zamu qarasa maganar".
"To Alhaji nagode a dawo lafiya Allah ya kareka".
"Amin malam Abubakar nima na gode" ya fad'a yana juyawa ya shiga mota ya tadata yabar gurin da sauri malam Habu ya juya gurin iyalansa yana musu albishir ga yadda sukai da Alhajin kowa murna yake a take suka fara d'iban kayan suna shigarwa gidan sukai sa'a dakuna biyar ne malam Habu ya d'auki d'aya su Asma'u suka shiga d'aya sannan matansa kowa ta kama d'aya duk da babu koda ledar da zasu shimfid'a dole malam Habu ya fita da tambaya har yaje ya sayo musu taburmi da 'yan sauran canjin da suka rage masa domin Rakiya ma ta d'an bashi guzuri harda butoci da kofina da turmi karami na ice ya sayo tukunya guda d'aya kafin a samu yadda za'ai a qaro da sauran abubuwan aiyukan gidan wadanda ba'a rasa ba ya sayo musu kayan abinci kad'an da sauran kud'in sannan ya hawo adaidaita ya dawo gida.
Kallonsa yaron yai yana cewa "babu inda ake sayarwa saidai kaje gidan cin abinci".
Kallon bokitin hannun nasa malam Habu yai ga kuma fork da plate🍽️ dan haka yace "kai me kake sayarwa"?.
Amsa yaron ya bashi "gurasa ce mai 'kuli amma ta kare saina d'ebo wata zaku saya"?.
Kai malam Habu ya d'aga "eh zamu saya idan ka d'ebo ka kawo mana kayi sauri yanzu" to yace yana yin gaba ba'a dad'e ba ya dawo ya ciko bokitin yace guda d'aya d'ari haka suka saye masa ita du saida bokitin ya koma gida.
Har bayan sallar isha suna nan zaune shiru shiru sunata jiran drivan nan daya kawosu ya dawo ya fad'a musu ko an samu amma har dare yayi nisa kusan karfe sha biyu ba labari harsun cire rai saigashi yazo da mota yayi parking bayan ya fito yace.
"Kayi hakuri malam wallahi ba mantawa nai daku ba nayi kiransa tun d'azu uzirin gida ya hanani dawowa kaga munyi waya dashi yace min babu sauran gidaje a hannunsa kayi hakuri saidai zanyi kokari na lalubo muku wani amma kafin nan ku shiga kangon nan ku aje kayanku nasan mai gidan sunansa Alhaji Musa mutumin kirki kafin dai na samo muku gidan hayar da zaku zauna nasan zai barku".
Kai malam Habu ya d'aga yana cewa "to shikenan na gode Allah ya saka da alkhairi" mi'kewa yai yana d'iban kayan suna shiga dashi sannan ya shikuma ya tafi haka suka kwana a kangon amma saboda tsoron nan ba garinsu bane basusan ya tsarinsa yake ba kada su ta'ba kayan wanda zai wulakanta su yasa tun kiran sallar farko na asuba malam Habu ya tashesu bayan yayi alwala ya fita xuwa masallaci tare da basu umarnin idan sunyi sallah kada su zauna su d'ebo kayan su dawo waje kada mai gidan yazo musu zuwan bazata kamasun dayai a ciki ya jawo musu matsala shiba wani kud'i ke gareshi ba.
Aiko suna ana shiga sallah bayan anyi sallama wuta-wuta sukai suka fita da komai waje kamar yadda ya umarcesu sai a wajen suka yi 'yan addu'o'i gari yayi haske malam Habu ya dawo dukka suka gaidashi bakin A'i da baya shiru ta kalleshi tana cewa.
"Oh ni A'i na fad'o daga sama na zarce rijiya gaba dubu Malam muna d'an zaman mu a gida cikin rufin asiri Rakiya tayi mana sutura ta bamu gurin zama haka kawai ka tashi tafiya batare da kasan inda zakaje ba kuma kaiba gurin kowa kazo ba ka kawomu tsakiyar birni ka ajemu ko tsoron azo a sace mu bakayi yanzu kila wani ya ganmu rakwacam har mu takwas kila yana nan yana fakon mu sai dare yayi yazo ya yashemu da d'ai d'ai wallahi nidai da ido d'aya da rabi nayi barcin jiya saboda naji ance birni ana yankewa mutane kai wai dama haka Kanon take da kyau tabdijan gaskiya dole su yaya Ilyah da Bara'atu su dage akan Nafisa ta auri d'an birni wa ya'ki dad'i umm kalli dan Allah Malam gidaje masu kyau ai ban ta'ba fitowa daga 'kauyen mu naje wani wuri ba kice muba rayuwa muke ba muna binne a kasa nifa idan ba yanzu ba ko a mafarki ban ta'ba zuwa Kano ba gashi dai a jihar nake kodan muna nisa dasu kuma cikin lungu sosai kai gaskiya garin yayi Masha Allah" ita kad'ai A'i sai sambatu take babu wanda yace mata ta tafar sau'ke suna zaune zaman jiran wannan yaron na jiya daya kawo musu gurasa suka saya ga drivan daya kawosu jiya shima yace zai dawo da safe amma shiru har Allah ya kawo wannan yaron mai gurasa kamar yadda yace musu da safema in suna so zai kawo su saya kud'insa malam Habu ya bashi suka juye fal babban bokiti sannan ya basu plate suka rarraba kowa ya karya yasha ruwa kafin yaron ya tattare kayansa yayi hanyar gida yana murnan zuwan wadannan ba'ki🙃.
Suna ta zaune dai suga ta inda driver zai 'bullo yazo ya fad'a musu idan ya samo musu gidan hayar amma shiru babu shi babu alamarsa sauke ajiyar zuciya malam Habu yai yana girgiza kai tare da d'an rufe ido a ransa yana tunanin indai yau drivan nan bai zo ya fad'a musu an samu gidan ko ba'a samu ba tofa baza suci gaba da zama anan ba duk dare yau sai sun sauya anguwa ko Allah zai basu rabons............................
A firgice Malam Habu ya bud'e ido sakamakon jin 'kara har baisan lokacin daya mi'ke tsaye daga zaune ba kallon motar da tazo tai parking gaf dasu yai amma baiga mutumin ciki ba saboda duhun glass d'in salati ya fara a cikin ransa tuni yaji hankalin sa ya tashi karfa ace mai wannan gidan ne yazo to yanzu me zasuce masa¿.....................
Jin an sake horn yasa Malam Habu d'agowa daga tunanin da yake ya kallo motar zuciyarsa na harbawa da karfi sosai daidai an bud'e kofar yaga wani lafiyayyan Alhaji ya fito yasha wanka cikin shadda mai tsada ga d'oneniyar hula wacce taji sitati tasha kari sannan takalmi👞 da agogo⌚ na ma'kudan kud'ad'e kai harda zobe💍 humm kawai siffarsa a kirashi sugar Dad☺️ sannan beauty no filter😃 haka yake ta ko'ina cass kuma kyakkyawa ne mai hanci ga fari ba irin alhazawan nan ne da suka aje tumbi kamar kayan wanki ba😳🤐.
Ganin ya kallesu yana dafe da murfin motar yasa jikin malam Habu ya d'an fara rawa neman jarumtarsa yake amma ya kasa saboda ganin irin kallon da mutumin ke musu da yake su matane har sufi malam Habun rud'ewa da hannu mutumin ya yafito malam Habu yana masa nuni da yaje gurin sa,.
Da'kyar Malam Habu dake tsaye daskare guri d'aya ya d'aga takalminsa ya fara tafiya zuwa inda Alhajin yake kamar mai ciwon 'kafa haka yake janta yana d'ari-d'ari da d'ar-d'ar d'in tsoro😞😥 saida ya kusa dashi sannan yaja ya tsaya murmushi mutumin yai yana cewa.
"Haba kai kuwa aboki karaso man ba wani abu bane magana zamuyi matso kusa kada ka damu".
Sauke numfashi Malam Habu yai jin abinda yace masa sai sannan ya d'anji hankalin sa ya lafa amma dai bai kwanta ba karasawa yai zai dur'kusa ya gaida dashi mutumin ya d'ago kafad'arsa da sauri yana cewa.
"A'a basai ka gaida dani a kasa ba aboki bani hannunka mu gaisa🤝" ya fad'a yana ri'ke hannu malam Habu sukai musabaha yace.
"Barka da asuba yakake"?.
Cikin jin sassauci malam Habu yace "lafiya alhamdulillah".
Kai ya d'aga masa yana cewa "hakan nada kyau dama tambaya ce zanyi maka idan bazaka damu ba sakamakon nayi mamakin ganinku har yau anan a layi kamar marasa gata ga mata da yara kuma 'yan mata babu dad'i jiya nazo na wuce tanan bayan na dawo daga office zan tafi gida na ganku a zaune kuma yauma na sake ganinku a nan d'in dai baku tafi ba shine nace ko bakusan kowa bane ku ba'ki ne ko"?.
Kai Malam Habu ya d'aga yana cewa "eh gaskiya mu ba'ki ne daga wani qauye muka taso nazo nan ne domin na kama hayar gida kuma nayi sana'a to munyi magana da direban motar daya kawo mu cewa zai laluba mana gidan haya amma shiru babu alamarsa tun jiya daya tafi yace mu shiga wannan kangon mu kwana kafin yau duk da shi yasan mai kangon amma mufa muna ciki a zaune bamu sanshi ba yazo duba gidansa ya ganmu a ciki kuma ba tambayar sa mukai ba shiyasa gari yana wajewa tun asuba nace mu fito waje kada Mai gidan yazo ya samemu a ciki nan ba garinmu bane bamusan ya tsarikansu suke ba ko abun laifi baya yawa muyi abinda zaija mana d'auri"?.
Murmushi mutumin yai yana cewa "kai daga kwana sai a d'aureku kamar wanda sukai sata? To kaga kwantar da hankalinka wannan kangon bana kowa bane nawa ne mallaki nane saiku saki jiki amma tunda gidan haya kake nema inada gidaje masu tarin yawa wanda ba mutane a ciki wasu kuma da mutane sannan hawa hawan kud'i ne sai wanda kake so na daidai qarfin ka idan kuma nasa muku murfin kofa a wannan d'in tunda na ganka da iyalai sosai kuma dama shima wannan d'in haya zansa amma me kace a shekara zaka iya biyan dubu d'ari biyu da hamsin"?.
Da sauri malam Habu ya d'aga kai yana cewa "eh na amince Alhaji kwarai zan biya insha Allahu za'a samu Allah ya dafa min Wallahi nayi maka alkawari zanyi kokari na biyaka lokacin da kake bukata dan Allah Alhaji ka amince"?.
"Ok shikenan karka damu za'a sa muku murfi yau tunda dama shi ya rage anyi filasta an d'anyi fenti sai kuyi maleji ko"?.
Kai Malam Habu ya d'aga "eh Alhaji na gode sosai Allah ya biyaka da mafificin alkairi".
Murmushi yai yana cewa "Amin amma mene sunan malamin"?.
"Sunana Malam Habubakar".
Hannu Alhajin ya mi'ko masa suka sake gaisawa yana cewa "alright u're welcome Malam Abubakar ni kuma sunana Alhaji Musa sannan nima anan anguwar nake ta by pass d'inku shikenan yanzu zan tafi office I don't want to be late but idan na dawo zamu qarasa maganar".
"To Alhaji nagode a dawo lafiya Allah ya kareka".
"Amin malam Abubakar nima na gode" ya fad'a yana juyawa ya shiga mota ya tadata yabar gurin da sauri malam Habu ya juya gurin iyalansa yana musu albishir ga yadda sukai da Alhajin kowa murna yake a take suka fara d'iban kayan suna shigarwa gidan sukai sa'a dakuna biyar ne malam Habu ya d'auki d'aya su Asma'u suka shiga d'aya sannan matansa kowa ta kama d'aya duk da babu koda ledar da zasu shimfid'a dole malam Habu ya fita da tambaya har yaje ya sayo musu taburmi da 'yan sauran canjin da suka rage masa domin Rakiya ma ta d'an bashi guzuri harda butoci da kofina da turmi karami na ice ya sayo tukunya guda d'aya kafin a samu yadda za'ai a qaro da sauran abubuwan aiyukan gidan wadanda ba'a rasa ba ya sayo musu kayan abinci kad'an da sauran kud'in sannan ya hawo adaidaita ya dawo gida.