Sashe 20
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Fitowa Jummai tai cikin mamaki take kallon Ramatu dake ta jibgar 'ya'yan ta kamar ta samu kayan wanki sai ihu suke rai bace tazo tana rufe Ramatu da duka ita nan fad'a ya kaure hayaniya ta cika gida mutanen ma'kota sai shigowa suke tuni akai caaa aka rabasu kowa na tambayar mai ya faru.
"Jummai na huci tace "ina nasan abinda ke faruwa kawai ji nai yara suna ihu ina lekowa naga ta danne su sai dukan su take komai sukai mata oho matsiyaciyar mata kawai" han'kurowa Ramatu tai zata kawowa Jummai cafka mutane suka tare tana cewa "dama taya zaki san abinda sukai min tsinanniyar kanta munafika mai ba'kin hali wallahi bazan yarda ko kijawa yaranki kunne ko jiki yai tsami ina d'an dalili zasu tisa min 'ya a gaba sai ramar ta suke bata da sukuni kamar wata mujiya kullum tana ra'be a gefen dandali bata da wargi hakan bai ishe suba sai sunce mata jahila to ku sani ba itace jahila ba Jummai ce" ta karasa maganar tana sake kai hannu zata cafko yarinyar dake gefe tana kuka tace "zo nan dan uwar ki mai siffar aljanu har nice zanyi magana ki zuro min ido kina kallona.
Mamakin 'karfin halin Ramatu kowa keyi Jummai takai matukar jin d'acin maganganun da Ramatun keyi amma ta dake tana kallon yaran nata tace "meyasa zaku ce wa 'yarta jahila ina ruwanku da ita" cikin kuka Hanne tace "wallahi babah bansan da wannan zancen ba ni a yau ma ban had'u da Lami ba" kallon dayar 'yar Jummai tai cikin fad'a tace "dan ubanki kece ko? ina ruwan ki da ita"? Itama cikin kuka tace "ni fa bani bace wallahi bance mata komai ba" a hangule t Ramatu tace "kuna nufin sharri zatai muku dan darar ubanku"? Haushi ya kama Jummai tace "Ramatu wulakancin ya isa haka sunce basu bane dole saikin tilasta musu sun karbi laifin da ba nasu ba na rantse da Allah bazan yarda ba sai munje gaban me gari yai mana iyaka bani bake ba 'yarki ba 'ya'yana karar ki zankai".
Shewa Ramatu tai tana cewa "kin dad'e baki kaini ba mai garin banza da wofi ai ni kare ya fishi a wajena in kinga dama ki kaini ramin gyare karewar kara aikin banza kawai ina jiranki idan kin fasa kaini uwarki cikin shegen ki tayi ta haife idan kin fasa kaina ba'a haifeki da jini ba idan kin fasa kaini ke ba yar halak bace goyon bola da juji ce ke" tana gama fadin ta sa'bi gyalen ta dake 'kar tai waje kamar wacce ta samu ta'bi sai hararrami take.
Kowa mamaki yake duk da dama sun san Ramatu sani na ha'ki'ka ba mace mai kirki bace wata mata dake kusa da Jummai ce ta kalle ta tana cewa "ke kwa Jummai wanne tsautsayin ne ya had'o ki fad'a da rahma"? 'kwafa Jummai tai cikin takaici tace "taya zan sani Ladi ina d'aki fa naji kukan yaran nan kawai tazo ta rufe su da duka wai sunce wa Lami jahila kiji fa dan Allah gashi yaran da bakin sun ce basu bane".
"Aiko wallahi Jummai karki yarda ki kai kararta gurin mai gari ko ki biya kud'i ki hau mashin kije ki d'ebo mata 'yan sanda domin wannan cin fuskar yayi yawa azo har gidan a zageka a d'aki yayanka" Ladi ta fad'a ranta a'bace "ai basai kince komai ba Ladi dole na kaita kara idan na bari ni banza tasha gaba ma wata tsiyar zata sake tsirowa tazo ta sauke min idan taga ban dau mataki a wannan ba" "a tabbas karki ta'ba yarda Jummai ki kaita kara a yau din nan kice baki yarda ba a bi miki kadin zuwa miki gar gida datai ta dakar miki 'ya'ya" hijab Jummai ta dauka tana cewa "yanzu ma kuwa zanje" fita sukai tare da sauran mutanen da suka zo ceto Jummai ta nufi gidan mai gari.
Ramatu na shiga gida ta aje gyale tare da bud'e randa ta kamfato ruwa tasha ta sake debowa tana jan kujera tace "haba kai sai yanzu naji sanyi a raina da naje na idar musu hankali na ya kwanta mu zuba idan basu gaji da ce wa Lami jahila ba nima bazan gaji da jibgar su ba haba mutum matsoraci ma bai had'u malam kowa ya d'ebo bolarsa kai zai zubawa tunda yaga baka da kata'bus amma idan ka iya masifa zakaga kowa yana tsoron ka" tana rufe baki yaro yai sallama yana cewa "wai malam yana nan"? Lekowa daga d'aki Baffah yai yana cewa "eh ina nan meya faru"? Yaro na kallon yadda Ramatu ke hararar sa yace "malam isubu ne yace wai kaje inji me gari" wani kallo Baffah yaiwa Ramatu kafin yace "jeka ina zuwa" yaro na fita Baffah ya kalli Ramatu yana cewa "sai ki tashi kije aina fad'a miki idan kinsan farkon fitina bakisan karshen taba babu ruwa na a cikin wannan al'amarin duk tsuntsun daya ja ruwa shi ruwa ke duka indai bazan fad'a miki magana kiji ba nima na zare hannu na daga safgarki" yana fadin haka ya koma daki.
Mi'kewa Ramatu tai tana cewa "bari nidin naje rigima ba uban wanda ta kashe kowa yaci tuwo dani miya yasha ba'ai d'an dazai taka ni na barshi ya huta ba saina 'kaddamar masa da daukar fansa" sa'ba gyale ta kuma yi tai waje matar Baffah Salamatu ta bita da kallo ta gaza gane wacce Ramatu takamaimai mutum ce ko aljan.
Fal ta samu gaban mai gari ya cika da mutane ana jiran zuwan ta ga Jummai a gefe tana zaune da yaranta itama zama tai tana harararsu can ta hango Lami tafi bayanta Iluh ne yaron mai gari da alama a dandali yaje ya kirata bayan sun 'karaso mai gari yace "Ramatu kinsan dalilin kiran ki nan"? Kamar bazatai magana ba sai kuma tace "eh na sani tunda naga wannan ba'kar munafikar tare da yaran ta nasan karata ta kawo" a fusace Jummai tace "kece babbar ba'kar munafika annamimiya mai hana zaman lafiy............................
Katse su mai gari yayi da cewa "ba hayaniya na ce kumin ba sannan bance kuyi zagi na zaga a gaba ba ke Jummai ba ke na tambaya ba ki bari nazo kanki" "kayi hakuri mai gari amma ka hana ta zagina" Jummai na rufe baki Ramatu tace "an zageki tsinanniyar tasha😲" tsawa Bukar ya daka musu cikin fad'a yace "gaban mai gari kuke hatta ko yanzu nan a kira muku hukuma" ta'be baki Ramatu "kai kuma asuwa baka da wannan matsayin ka bari wanda ya isa yai magana zaka kancaro mana jajayen ha'kora wani kai kai gaban mai gari kuke😂 ai mun sani tunda ba makafi bane mu" "ya ishe ki haka Ramatu" Bukar ya fad'a yana nuna ta da yatsa zatai magana taji mai gari yace "wai wannan wanne irin iskanci ne zaku saurare ni ko harkar gaban naku zakuyi shin kun dauke ni mutumin banza ne"? Shiru sukai sai isubu da yace "Allah ya huci zuciyar ka kayi hakuri ayi musu afuwa sunyi kuskure" caraf Ramatu tace "amma dai Isubu na kayan miya kake nema wanda yai lefi baibada hakuri ba sai d'an kallo" "karki 'kara domin ni ba sa'an yinki bane" dariya Ramatu tai kamar zararriya tace "a lallai Isubu wannan ai borin kunya ne idan na kara me zaka iya yi"? Kai tsaye isubu da ransa ya gama 'baci yace "zan kai ki gaban hukuma ne" nan ma dariya ta kuma yi tana cewa "anzo inda nake son ji kaga idan ka turo yan sanda suka kamani 'kalau dani gaba ta kaini dama ina son zuwa garin sarin kayan miya saina saro abina ko ya kace tunani me kyau" kowa kallon mamaki yai mata wato wannan matar ta zama annuba ba mai iyawa da ita.
Zuba musu ido kawai mai gari yai saida gama da akai sa'a Isubu bai sake kulata ba ya kalli me gari yana cewa "kayi hakuri ranka ya dad'e" d'an tsaki mai gari yayi kamar zai daddannawa Ramatu zagi dan ta gama 'kular dashi cikin kaiwa zuciyarsa nesa ya kalli Lami dake gefe yana cewa.
"Ke Lami me ya had'a ki da wadannan yaran har suke ce miki jahila"? Kallon su Hanne dake gefe Lami tayi tare da girgiza kai tace "basu bane Balkin gidan me layo ce ita da Razi'kah ta gidan su baba Abuh "kina nufin ba su Hanne bane suka fad'a miki"? "Eh me gari basu bane" kai ya jinjina yana cewa "kinji da kunnenki Ramatu basu bane amma kikaje har gida kika dake su kika ci zarafin uwar su" Mamman mijin Jummai dake gefe yace "nikam me gari koda ma ace sune bazan yarda da dukan datai musu ba balle yanzu da gaskiya ta bayyana a gaban kowa dan haka ina so amin adalci abi min kadin shiga min gida datai ba neman izni ta dakar min yara harda fasa baki ta ciwa mata ta mutunci ko na kaita gaba gurin yan sanda" "gun yan kokara zaka kaini wallahi baka isa ba sisi bazan bayar ba 'ya'yan kane idan kaga dama ka sai musu magani idan kaga hagu ka barsu da ciwon jiki ba matsala ta bace ba ruwa na da hakan" kai Mamman ya jinjina zaiyi magana me gari ya katse shi da cewa "kaga karka ce komai Mamman ka 'kyale zan biya kudin kaje ka sai musu maganin zuwa gobe zan kira azo a tafi da ita inda wuya zata sa tayi ladabi tunda taga nan kafad'a ta daidai take da tata zaku iya tafiya zan kira ka gobe da safe" godiya Mamman yai yana mikewa shida Jummai da yaransa sukai gida.
"Jummai na huci tace "ina nasan abinda ke faruwa kawai ji nai yara suna ihu ina lekowa naga ta danne su sai dukan su take komai sukai mata oho matsiyaciyar mata kawai" han'kurowa Ramatu tai zata kawowa Jummai cafka mutane suka tare tana cewa "dama taya zaki san abinda sukai min tsinanniyar kanta munafika mai ba'kin hali wallahi bazan yarda ko kijawa yaranki kunne ko jiki yai tsami ina d'an dalili zasu tisa min 'ya a gaba sai ramar ta suke bata da sukuni kamar wata mujiya kullum tana ra'be a gefen dandali bata da wargi hakan bai ishe suba sai sunce mata jahila to ku sani ba itace jahila ba Jummai ce" ta karasa maganar tana sake kai hannu zata cafko yarinyar dake gefe tana kuka tace "zo nan dan uwar ki mai siffar aljanu har nice zanyi magana ki zuro min ido kina kallona.
Mamakin 'karfin halin Ramatu kowa keyi Jummai takai matukar jin d'acin maganganun da Ramatun keyi amma ta dake tana kallon yaran nata tace "meyasa zaku ce wa 'yarta jahila ina ruwanku da ita" cikin kuka Hanne tace "wallahi babah bansan da wannan zancen ba ni a yau ma ban had'u da Lami ba" kallon dayar 'yar Jummai tai cikin fad'a tace "dan ubanki kece ko? ina ruwan ki da ita"? Itama cikin kuka tace "ni fa bani bace wallahi bance mata komai ba" a hangule t Ramatu tace "kuna nufin sharri zatai muku dan darar ubanku"? Haushi ya kama Jummai tace "Ramatu wulakancin ya isa haka sunce basu bane dole saikin tilasta musu sun karbi laifin da ba nasu ba na rantse da Allah bazan yarda ba sai munje gaban me gari yai mana iyaka bani bake ba 'yarki ba 'ya'yana karar ki zankai".
Shewa Ramatu tai tana cewa "kin dad'e baki kaini ba mai garin banza da wofi ai ni kare ya fishi a wajena in kinga dama ki kaini ramin gyare karewar kara aikin banza kawai ina jiranki idan kin fasa kaini uwarki cikin shegen ki tayi ta haife idan kin fasa kaina ba'a haifeki da jini ba idan kin fasa kaini ke ba yar halak bace goyon bola da juji ce ke" tana gama fadin ta sa'bi gyalen ta dake 'kar tai waje kamar wacce ta samu ta'bi sai hararrami take.
Kowa mamaki yake duk da dama sun san Ramatu sani na ha'ki'ka ba mace mai kirki bace wata mata dake kusa da Jummai ce ta kalle ta tana cewa "ke kwa Jummai wanne tsautsayin ne ya had'o ki fad'a da rahma"? 'kwafa Jummai tai cikin takaici tace "taya zan sani Ladi ina d'aki fa naji kukan yaran nan kawai tazo ta rufe su da duka wai sunce wa Lami jahila kiji fa dan Allah gashi yaran da bakin sun ce basu bane".
"Aiko wallahi Jummai karki yarda ki kai kararta gurin mai gari ko ki biya kud'i ki hau mashin kije ki d'ebo mata 'yan sanda domin wannan cin fuskar yayi yawa azo har gidan a zageka a d'aki yayanka" Ladi ta fad'a ranta a'bace "ai basai kince komai ba Ladi dole na kaita kara idan na bari ni banza tasha gaba ma wata tsiyar zata sake tsirowa tazo ta sauke min idan taga ban dau mataki a wannan ba" "a tabbas karki ta'ba yarda Jummai ki kaita kara a yau din nan kice baki yarda ba a bi miki kadin zuwa miki gar gida datai ta dakar miki 'ya'ya" hijab Jummai ta dauka tana cewa "yanzu ma kuwa zanje" fita sukai tare da sauran mutanen da suka zo ceto Jummai ta nufi gidan mai gari.
Ramatu na shiga gida ta aje gyale tare da bud'e randa ta kamfato ruwa tasha ta sake debowa tana jan kujera tace "haba kai sai yanzu naji sanyi a raina da naje na idar musu hankali na ya kwanta mu zuba idan basu gaji da ce wa Lami jahila ba nima bazan gaji da jibgar su ba haba mutum matsoraci ma bai had'u malam kowa ya d'ebo bolarsa kai zai zubawa tunda yaga baka da kata'bus amma idan ka iya masifa zakaga kowa yana tsoron ka" tana rufe baki yaro yai sallama yana cewa "wai malam yana nan"? Lekowa daga d'aki Baffah yai yana cewa "eh ina nan meya faru"? Yaro na kallon yadda Ramatu ke hararar sa yace "malam isubu ne yace wai kaje inji me gari" wani kallo Baffah yaiwa Ramatu kafin yace "jeka ina zuwa" yaro na fita Baffah ya kalli Ramatu yana cewa "sai ki tashi kije aina fad'a miki idan kinsan farkon fitina bakisan karshen taba babu ruwa na a cikin wannan al'amarin duk tsuntsun daya ja ruwa shi ruwa ke duka indai bazan fad'a miki magana kiji ba nima na zare hannu na daga safgarki" yana fadin haka ya koma daki.
Mi'kewa Ramatu tai tana cewa "bari nidin naje rigima ba uban wanda ta kashe kowa yaci tuwo dani miya yasha ba'ai d'an dazai taka ni na barshi ya huta ba saina 'kaddamar masa da daukar fansa" sa'ba gyale ta kuma yi tai waje matar Baffah Salamatu ta bita da kallo ta gaza gane wacce Ramatu takamaimai mutum ce ko aljan.
Fal ta samu gaban mai gari ya cika da mutane ana jiran zuwan ta ga Jummai a gefe tana zaune da yaranta itama zama tai tana harararsu can ta hango Lami tafi bayanta Iluh ne yaron mai gari da alama a dandali yaje ya kirata bayan sun 'karaso mai gari yace "Ramatu kinsan dalilin kiran ki nan"? Kamar bazatai magana ba sai kuma tace "eh na sani tunda naga wannan ba'kar munafikar tare da yaran ta nasan karata ta kawo" a fusace Jummai tace "kece babbar ba'kar munafika annamimiya mai hana zaman lafiy............................
Katse su mai gari yayi da cewa "ba hayaniya na ce kumin ba sannan bance kuyi zagi na zaga a gaba ba ke Jummai ba ke na tambaya ba ki bari nazo kanki" "kayi hakuri mai gari amma ka hana ta zagina" Jummai na rufe baki Ramatu tace "an zageki tsinanniyar tasha😲" tsawa Bukar ya daka musu cikin fad'a yace "gaban mai gari kuke hatta ko yanzu nan a kira muku hukuma" ta'be baki Ramatu "kai kuma asuwa baka da wannan matsayin ka bari wanda ya isa yai magana zaka kancaro mana jajayen ha'kora wani kai kai gaban mai gari kuke😂 ai mun sani tunda ba makafi bane mu" "ya ishe ki haka Ramatu" Bukar ya fad'a yana nuna ta da yatsa zatai magana taji mai gari yace "wai wannan wanne irin iskanci ne zaku saurare ni ko harkar gaban naku zakuyi shin kun dauke ni mutumin banza ne"? Shiru sukai sai isubu da yace "Allah ya huci zuciyar ka kayi hakuri ayi musu afuwa sunyi kuskure" caraf Ramatu tace "amma dai Isubu na kayan miya kake nema wanda yai lefi baibada hakuri ba sai d'an kallo" "karki 'kara domin ni ba sa'an yinki bane" dariya Ramatu tai kamar zararriya tace "a lallai Isubu wannan ai borin kunya ne idan na kara me zaka iya yi"? Kai tsaye isubu da ransa ya gama 'baci yace "zan kai ki gaban hukuma ne" nan ma dariya ta kuma yi tana cewa "anzo inda nake son ji kaga idan ka turo yan sanda suka kamani 'kalau dani gaba ta kaini dama ina son zuwa garin sarin kayan miya saina saro abina ko ya kace tunani me kyau" kowa kallon mamaki yai mata wato wannan matar ta zama annuba ba mai iyawa da ita.
Zuba musu ido kawai mai gari yai saida gama da akai sa'a Isubu bai sake kulata ba ya kalli me gari yana cewa "kayi hakuri ranka ya dad'e" d'an tsaki mai gari yayi kamar zai daddannawa Ramatu zagi dan ta gama 'kular dashi cikin kaiwa zuciyarsa nesa ya kalli Lami dake gefe yana cewa.
"Ke Lami me ya had'a ki da wadannan yaran har suke ce miki jahila"? Kallon su Hanne dake gefe Lami tayi tare da girgiza kai tace "basu bane Balkin gidan me layo ce ita da Razi'kah ta gidan su baba Abuh "kina nufin ba su Hanne bane suka fad'a miki"? "Eh me gari basu bane" kai ya jinjina yana cewa "kinji da kunnenki Ramatu basu bane amma kikaje har gida kika dake su kika ci zarafin uwar su" Mamman mijin Jummai dake gefe yace "nikam me gari koda ma ace sune bazan yarda da dukan datai musu ba balle yanzu da gaskiya ta bayyana a gaban kowa dan haka ina so amin adalci abi min kadin shiga min gida datai ba neman izni ta dakar min yara harda fasa baki ta ciwa mata ta mutunci ko na kaita gaba gurin yan sanda" "gun yan kokara zaka kaini wallahi baka isa ba sisi bazan bayar ba 'ya'yan kane idan kaga dama ka sai musu magani idan kaga hagu ka barsu da ciwon jiki ba matsala ta bace ba ruwa na da hakan" kai Mamman ya jinjina zaiyi magana me gari ya katse shi da cewa "kaga karka ce komai Mamman ka 'kyale zan biya kudin kaje ka sai musu maganin zuwa gobe zan kira azo a tafi da ita inda wuya zata sa tayi ladabi tunda taga nan kafad'a ta daidai take da tata zaku iya tafiya zan kira ka gobe da safe" godiya Mamman yai yana mikewa shida Jummai da yaransa sukai gida.