Sashe 45
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Caraf Ramatu tace "dama nace maka ina neman girma ne? Karta girmama nin mana taga yadda zanci 'kashin ubanta tasan karon mu da ita ai abin baya mata dad'i" Ilyah bai sake magana ba ya kalli Bara'atu yana cewa "koma d'aki ki kwanta" da sauri Bara'atu ta shige cike da tsoro ta rufo kofa hararar sa Ramatu tai "humm Ilyasu kayi asara wallahi kaji jiki da ina da wani d'an bazan zauna a gidanka ba saidai ka nemi wata uwar badai niba" shikam tari da bai kama shiba bai sake ce mata uffan ba ya juya shima yana komawa d'akin amaryarsa yayin da Ramatu taci gaba da balbali a tsakar gida ita kadai taja kujera ta zauna sai zazzaga fad'a take bakinta har kumba yake ta'ki yin shiru duk ta dami jama'ar anguwa sai Allah wadai suke har akai assalatu aka shiga masallaci bata tashi ba balle tai alwala da sallah saida gari yai haske sannan tayi niyyar yi.
Habu ne zaune yayi tagumi gaban Salamatu dake kwance sharkaf kamar gawa Sabi'u na gefensa sunyi shiru babu mai cewa uffan shigowa d'akin Rakiya tai da sallama cikin sanyin jiki tace "ya jikin nata"? Kai Sabi'u ya d'aga "da sauki Rakiya" zama tai ta wajen 'kafafun Salamatun tana cewa "amma me gida tunda likitoci sunce ba ciwon asibiti bane mezai hana muyi na gargajiya kaga ciwon gaba yake 'kara yi kuma kalli wani abun tsoro yadda jikinta yake 'kai'kashewa kalli yadda fuskarta ta koma kallonta kamar bana mutane ba" ta karasa maganar tana fashewa da kuka.
Kallon Sabi'u Habu yai cike da damuwa yace "yaya Sabi'u gaskiya wannan ciwon na babah ba 'kalau ba abun da tsoro tunda kaji likita yace a dawo gida ayi na gargajiya lallai akwai abun dubawa ga kuma kullum sai anyi mata 'karin ruwa amma yan awanni ace sun tsotse wanne irin abu ne wannan kodai mayu ne"? Numfashi Sabi'u ya sauke tare da girgiza kai ganin yadda bakinta ke kakkarwa ya kalli Habu yana cewa "nima tunanin dake raina kenan saidai bamu tabbatar ba na samu malam Zayyanu jiya akan batun yace yasan wani mutum mai maganin hausa duk abinda ya shige duhu indai anje wurinsa insha Allahu ana samun waraka dama jira nake alhaji Hamidu ya dawo daga saudiyya kud'ina da yake gurinsa ya bani sai mu tafi" gyara zama Habu yai yana cewa "ba matsala yaya Sabi'u indai maganar kud'i ba damuwa mudai lafiyar ta muke bukata bari naje gida na dawo saimu tafi tunda kaga yanzu na iya motar dana sayo ba haya nake bada itaba sai muje" mikewa Sabi'u yai shima yana cewa "to bari naje gurin malam Zayyanun yamin kwatancen garin kafin ka dawo" Rakiya ya kalla "ki jirani a gurinta ina zuwa" to tace yayin da suka fito tare Sabi'u yai gurin da zai sami malam Zayyanu Habu kuma yai gida.
Zaune ya sami Saude da amayarsa A'i dan Binta kam tana gida wanka ganinsa da damuwa yasa Saude cewa "lafiya meya faru naganka haka"? 'Dan tsayawa yai yana kallon Asma'u dake zaune gaban A'i tana mata kitso yace "eh lafiya babah zamu kai gurin magani wani gari yanzu" "subahanallahi sake tashi jikin yai"? Wucewa habu yai zuwa d'akinsa yana cewa "ai dama baya sauka kullum a tashe yake" shiru sukai cike da jimami harya fito Saude tace "bari muje mu gano ta A'i bar kitson nan sai mun dawo" mikewa suka kowa na dauko hijab suka fita motar na waje yace su shiga tunda shine zai jasu shiga sukai duk inda ya gifta da ido ake bin motar masu hassada nayi masu tayashi murna nayi saidai yan ba'kin ciki sunfi yawa a sanda sukaje al'ajabine ya kamasu ganin yadda kumfa ke fita a bakinta sai mummurd'ewa take tana surutai duk zaro ido sukai jiki na rawa musamman A'i da sauri tai baya Dan akwaita da tsoro cicci'bota habu da Sabi'u sukai suna fita da ita wajen motar da'kyar suka tan'kwasata suka sata a cikin kafin suka shiga habu na baarwa Saude sakon yadda zasuyi amfani da kayan abinci kafin suka dau hanya.
Dalah na zaune Balarabe ya shigo da kaya cikin leda a hannunsa ya aje mata ba magana d'agowa tayi a damuwance tana kallon sa kamar hawaye zai zubo mata dan tasan ba kalau ba yanzu gabadaya ya canza ya zama wani iri tace "wannan meye a ciki"? Bai kalleta ba yace ki bud'e ki gani mana ba kina da ido ba"? Bud'ewa Dalah tai ganin kayane yasa tace "na maye"? Kai tsaye Balarabe yace "na fad'ar kishiya ne kin gane aure zanyi Asabe zan aura dan haka duk wani shirginki da kika san yana wancan d'akin ki tattare zan gyara" sauke zazzafan numfashi Dalah tai tana cewa "shikenan Allah yasa haka ne mafificin alkairi" Amin inda gaske kike" ya fad'a yana Mi'kewa zai fita sai kuma ya tsaya tare da cewa "nayi gidan Asabe kada ki dafa abinci dani" kafin Dalah tai magana Indo tace "baba ka taho min da biskin" "da uban biskin zan taho miki dashi tsohuwarki ta baki kud'i kije shagon Habu ki sayo ni bani da kud'i" yana fad'in haka yai waje yabar Dalah tana sharar 'kwalla Innalillahi wa inna ilaihi raji'un tun ba'aje ko'ina ba Balarabe ya fara canzawa ina ga yayi auren kenan.
Tafiyar su habu da kwana biyu Rakiya ta haihu gashi ba waya a tsakani balle ta fad'a sai wata tsohuwa ce daga ma'koftansu take kula da ita da jaririn mutane nata zuwa barka ranar suna itace ta za'ba masa tunda Sabi'un bayanan cikin dabbobin da yake kiwo aka yanka mata raguna biyu Binta ma tazo bikin sunan saboda tayi wata biyu jira take Habu ya dawo daga tafiya ta dawo d'akin ta gashi dama Bashir ya bar gida ya tafi dutse karatu sai lokaci lokaci yake d'an zuwa gida su gaisa yana can yayi gidansa da matarsa harda d'an sa Ahmad.
Suna zaune anata hira irin wacce akeyi idan an had"u a gidan biki Dalah da shigo da atamfar biki a hannunta suna gaisawa ta shiga d'akin Rakiya domin 'kawarta ce sosai tun suna yara sakamakon zafi yasa Dalah ta fito waje tana zama cikin mutane a 'kar'kashin bishiyar badalar dake tsakiyar gidan yafendo ce ta kalleta tana cewa "sannu 'yarnan kinji Allah ya miki tsari da sharrin wannan muguwar mace Asabe da mijinki yake kokarin aura" zaro ido waje Hajjah tai "ke wacce Asaben amma dai ba Asabe ta bayan layin muba matar da tai zaman logus ko lagwas (Lagos) yake na manta sunan garin ai itace zai aura"? Kai yafendo ta d'aga "eh itafa" har 'kwaruwa Hajjah take waje tafa hannu da cewa "Innalillahi amma gaskiya Balarabe baiyi zabin mace ta gari ba na taya ki ba'kin ciki Dalah Allah ya tsare ki daga sharrin ta dan wannan matar kwalba ma haka ta ganta" "aike dai kawai bari dan ko wancan mijin nata ma ba mutuwar Allah yai ba kashe shi tai haka mutane suke cewa dama saboda dukiyar sa ta aure shi* "oh ni kinji irin abun ko? Kuna zamanku lafiya zai yayo muku bala'i ke dashi" ita dai shiru tai kawai tana sauraron su yayin da suke tsinka mata zuciya da maganganunsu amma ya zatai bayan ha'kuri da addu'ar Allah ya tsare ta da tarkon Asaben.
Batun su habu kam sunje gurin me magani mutumin ya matukar 'kwarewa a iya cire aljanu komai taurinsu amma me abun ya bashi mamaki babu aljanu jikin Salamatu kuma ba mayu bane yayi iya bakin kokarin sa amma baiga komai ba dan haka shawara ya basu cewa kawai saidai ai mata sauka ko Allah zaisa a dace damuwa da tashin hankali baisa sun iya ce masa 'kala ba sai shine ya fahimci suna wani hali na d'imuwa ya taimaka musu amma dai labarin yana nan yadda yake babu sauki ko sasssuci a jikin Salamatu sunfi wata yana abu d'aya karshe yace sunyi hakuri su koma gida su sake jarrabawa zuwa gurin wani malamin ko zasu dace shikam ya gaza haka suka tattaro suka dawo gida jiki a sanyaye mutane sai zuwa dubota ake harda masu kuka ganin yadda ta koma kamar ba mutum ba ta wani rame halittarta ta canza.
Wata biyar tsakani Salamatu tabar duniya😥 wanda kowa yana mata fatan mutuwa ta zama hutu gareta madadin wuyar da take sha lokacin da Ramatu taji mutuwar cewa tai "uhm kace yau Salamatu da shan duka a kabari🙊" to waiwaye ance adon tafiya ne amma fa ta tuna me wadannan halittun suka ce mata koba dad'e koba jima abinda tai zai dawo kanta nanfa tashin hankali ya same ta ta ri'ka gurza kuka a gidan mutuwar nan kowa yayi zaton akan Salamatun ne ashe ita abinda ke damunta dabam ko gida data koma 'kin cin abinci tai har dare saida Ilyah ya shigo Bara'atu take fad'a masa ya shiga d'aki ya ganta zaune tayi tagumi mamaki ne ya kama shi yaushe rabo yaga Ramatu a haka ai harya manta zama yai yana sake kallon ta da karantar meke damun ta yace.
"Babah lafiya me akai miki"? Jin tashin murya yasa a gigice Ramatu ta tashi a guje tana fad'awa saman katifa tare da jan bargo ta lullu'ba muryarta na rawa tace "na shiga uku na lalace wayyo Allah na dan Allah kuyi hakuri wallahi ba a son raina bane dama fa nace muku na ha'kura kune kuka 'ki wallahi ba ruwana nidai ku 'kyaleni".
Tsananin mamaki ne ya kama Ilyah wannan kuma lafiya maganganun me take haka kamar ta samu ta'bi yaye mayafin data lullu'ba yayi yana cewa "babah nine fa me kikeyi ne haka"? Jin tashin muryar Ilyah yasa ta bud'e ido tana kallon sa tare da sauke ajiyar zuciya tace "Ilyah kaine aina dauka wadannan tsinannun ne" da alamar tambaya yace "su waye tsinannu"? Dan shi ya dauka da Bara'atu da Maimuna take sai kuma yaji tace "wasu tambad'add"un halittu ne saida nace musu bana so na ha'kura amma suka 'ki" Ilyah jiyai hankalin sa ya sake tashi gashi ta kuma lumar dashi ya kasa gane inda ta dosa........................
Habu ne zaune yayi tagumi gaban Salamatu dake kwance sharkaf kamar gawa Sabi'u na gefensa sunyi shiru babu mai cewa uffan shigowa d'akin Rakiya tai da sallama cikin sanyin jiki tace "ya jikin nata"? Kai Sabi'u ya d'aga "da sauki Rakiya" zama tai ta wajen 'kafafun Salamatun tana cewa "amma me gida tunda likitoci sunce ba ciwon asibiti bane mezai hana muyi na gargajiya kaga ciwon gaba yake 'kara yi kuma kalli wani abun tsoro yadda jikinta yake 'kai'kashewa kalli yadda fuskarta ta koma kallonta kamar bana mutane ba" ta karasa maganar tana fashewa da kuka.
Kallon Sabi'u Habu yai cike da damuwa yace "yaya Sabi'u gaskiya wannan ciwon na babah ba 'kalau ba abun da tsoro tunda kaji likita yace a dawo gida ayi na gargajiya lallai akwai abun dubawa ga kuma kullum sai anyi mata 'karin ruwa amma yan awanni ace sun tsotse wanne irin abu ne wannan kodai mayu ne"? Numfashi Sabi'u ya sauke tare da girgiza kai ganin yadda bakinta ke kakkarwa ya kalli Habu yana cewa "nima tunanin dake raina kenan saidai bamu tabbatar ba na samu malam Zayyanu jiya akan batun yace yasan wani mutum mai maganin hausa duk abinda ya shige duhu indai anje wurinsa insha Allahu ana samun waraka dama jira nake alhaji Hamidu ya dawo daga saudiyya kud'ina da yake gurinsa ya bani sai mu tafi" gyara zama Habu yai yana cewa "ba matsala yaya Sabi'u indai maganar kud'i ba damuwa mudai lafiyar ta muke bukata bari naje gida na dawo saimu tafi tunda kaga yanzu na iya motar dana sayo ba haya nake bada itaba sai muje" mikewa Sabi'u yai shima yana cewa "to bari naje gurin malam Zayyanun yamin kwatancen garin kafin ka dawo" Rakiya ya kalla "ki jirani a gurinta ina zuwa" to tace yayin da suka fito tare Sabi'u yai gurin da zai sami malam Zayyanu Habu kuma yai gida.
Zaune ya sami Saude da amayarsa A'i dan Binta kam tana gida wanka ganinsa da damuwa yasa Saude cewa "lafiya meya faru naganka haka"? 'Dan tsayawa yai yana kallon Asma'u dake zaune gaban A'i tana mata kitso yace "eh lafiya babah zamu kai gurin magani wani gari yanzu" "subahanallahi sake tashi jikin yai"? Wucewa habu yai zuwa d'akinsa yana cewa "ai dama baya sauka kullum a tashe yake" shiru sukai cike da jimami harya fito Saude tace "bari muje mu gano ta A'i bar kitson nan sai mun dawo" mikewa suka kowa na dauko hijab suka fita motar na waje yace su shiga tunda shine zai jasu shiga sukai duk inda ya gifta da ido ake bin motar masu hassada nayi masu tayashi murna nayi saidai yan ba'kin ciki sunfi yawa a sanda sukaje al'ajabine ya kamasu ganin yadda kumfa ke fita a bakinta sai mummurd'ewa take tana surutai duk zaro ido sukai jiki na rawa musamman A'i da sauri tai baya Dan akwaita da tsoro cicci'bota habu da Sabi'u sukai suna fita da ita wajen motar da'kyar suka tan'kwasata suka sata a cikin kafin suka shiga habu na baarwa Saude sakon yadda zasuyi amfani da kayan abinci kafin suka dau hanya.
Dalah na zaune Balarabe ya shigo da kaya cikin leda a hannunsa ya aje mata ba magana d'agowa tayi a damuwance tana kallon sa kamar hawaye zai zubo mata dan tasan ba kalau ba yanzu gabadaya ya canza ya zama wani iri tace "wannan meye a ciki"? Bai kalleta ba yace ki bud'e ki gani mana ba kina da ido ba"? Bud'ewa Dalah tai ganin kayane yasa tace "na maye"? Kai tsaye Balarabe yace "na fad'ar kishiya ne kin gane aure zanyi Asabe zan aura dan haka duk wani shirginki da kika san yana wancan d'akin ki tattare zan gyara" sauke zazzafan numfashi Dalah tai tana cewa "shikenan Allah yasa haka ne mafificin alkairi" Amin inda gaske kike" ya fad'a yana Mi'kewa zai fita sai kuma ya tsaya tare da cewa "nayi gidan Asabe kada ki dafa abinci dani" kafin Dalah tai magana Indo tace "baba ka taho min da biskin" "da uban biskin zan taho miki dashi tsohuwarki ta baki kud'i kije shagon Habu ki sayo ni bani da kud'i" yana fad'in haka yai waje yabar Dalah tana sharar 'kwalla Innalillahi wa inna ilaihi raji'un tun ba'aje ko'ina ba Balarabe ya fara canzawa ina ga yayi auren kenan.
Tafiyar su habu da kwana biyu Rakiya ta haihu gashi ba waya a tsakani balle ta fad'a sai wata tsohuwa ce daga ma'koftansu take kula da ita da jaririn mutane nata zuwa barka ranar suna itace ta za'ba masa tunda Sabi'un bayanan cikin dabbobin da yake kiwo aka yanka mata raguna biyu Binta ma tazo bikin sunan saboda tayi wata biyu jira take Habu ya dawo daga tafiya ta dawo d'akin ta gashi dama Bashir ya bar gida ya tafi dutse karatu sai lokaci lokaci yake d'an zuwa gida su gaisa yana can yayi gidansa da matarsa harda d'an sa Ahmad.
Suna zaune anata hira irin wacce akeyi idan an had"u a gidan biki Dalah da shigo da atamfar biki a hannunta suna gaisawa ta shiga d'akin Rakiya domin 'kawarta ce sosai tun suna yara sakamakon zafi yasa Dalah ta fito waje tana zama cikin mutane a 'kar'kashin bishiyar badalar dake tsakiyar gidan yafendo ce ta kalleta tana cewa "sannu 'yarnan kinji Allah ya miki tsari da sharrin wannan muguwar mace Asabe da mijinki yake kokarin aura" zaro ido waje Hajjah tai "ke wacce Asaben amma dai ba Asabe ta bayan layin muba matar da tai zaman logus ko lagwas (Lagos) yake na manta sunan garin ai itace zai aura"? Kai yafendo ta d'aga "eh itafa" har 'kwaruwa Hajjah take waje tafa hannu da cewa "Innalillahi amma gaskiya Balarabe baiyi zabin mace ta gari ba na taya ki ba'kin ciki Dalah Allah ya tsare ki daga sharrin ta dan wannan matar kwalba ma haka ta ganta" "aike dai kawai bari dan ko wancan mijin nata ma ba mutuwar Allah yai ba kashe shi tai haka mutane suke cewa dama saboda dukiyar sa ta aure shi* "oh ni kinji irin abun ko? Kuna zamanku lafiya zai yayo muku bala'i ke dashi" ita dai shiru tai kawai tana sauraron su yayin da suke tsinka mata zuciya da maganganunsu amma ya zatai bayan ha'kuri da addu'ar Allah ya tsare ta da tarkon Asaben.
Batun su habu kam sunje gurin me magani mutumin ya matukar 'kwarewa a iya cire aljanu komai taurinsu amma me abun ya bashi mamaki babu aljanu jikin Salamatu kuma ba mayu bane yayi iya bakin kokarin sa amma baiga komai ba dan haka shawara ya basu cewa kawai saidai ai mata sauka ko Allah zaisa a dace damuwa da tashin hankali baisa sun iya ce masa 'kala ba sai shine ya fahimci suna wani hali na d'imuwa ya taimaka musu amma dai labarin yana nan yadda yake babu sauki ko sasssuci a jikin Salamatu sunfi wata yana abu d'aya karshe yace sunyi hakuri su koma gida su sake jarrabawa zuwa gurin wani malamin ko zasu dace shikam ya gaza haka suka tattaro suka dawo gida jiki a sanyaye mutane sai zuwa dubota ake harda masu kuka ganin yadda ta koma kamar ba mutum ba ta wani rame halittarta ta canza.
Wata biyar tsakani Salamatu tabar duniya😥 wanda kowa yana mata fatan mutuwa ta zama hutu gareta madadin wuyar da take sha lokacin da Ramatu taji mutuwar cewa tai "uhm kace yau Salamatu da shan duka a kabari🙊" to waiwaye ance adon tafiya ne amma fa ta tuna me wadannan halittun suka ce mata koba dad'e koba jima abinda tai zai dawo kanta nanfa tashin hankali ya same ta ta ri'ka gurza kuka a gidan mutuwar nan kowa yayi zaton akan Salamatun ne ashe ita abinda ke damunta dabam ko gida data koma 'kin cin abinci tai har dare saida Ilyah ya shigo Bara'atu take fad'a masa ya shiga d'aki ya ganta zaune tayi tagumi mamaki ne ya kama shi yaushe rabo yaga Ramatu a haka ai harya manta zama yai yana sake kallon ta da karantar meke damun ta yace.
"Babah lafiya me akai miki"? Jin tashin murya yasa a gigice Ramatu ta tashi a guje tana fad'awa saman katifa tare da jan bargo ta lullu'ba muryarta na rawa tace "na shiga uku na lalace wayyo Allah na dan Allah kuyi hakuri wallahi ba a son raina bane dama fa nace muku na ha'kura kune kuka 'ki wallahi ba ruwana nidai ku 'kyaleni".
Tsananin mamaki ne ya kama Ilyah wannan kuma lafiya maganganun me take haka kamar ta samu ta'bi yaye mayafin data lullu'ba yayi yana cewa "babah nine fa me kikeyi ne haka"? Jin tashin muryar Ilyah yasa ta bud'e ido tana kallon sa tare da sauke ajiyar zuciya tace "Ilyah kaine aina dauka wadannan tsinannun ne" da alamar tambaya yace "su waye tsinannu"? Dan shi ya dauka da Bara'atu da Maimuna take sai kuma yaji tace "wasu tambad'add"un halittu ne saida nace musu bana so na ha'kura amma suka 'ki" Ilyah jiyai hankalin sa ya sake tashi gashi ta kuma lumar dashi ya kasa gane inda ta dosa........................