← Book details Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 29 OF 145

Sashe 29

Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kai Baffah ya d'aga "to naji zancen ku kuma na amince domin nima ina son hakan ina kaunar ganin ahlina cikin farin ciki ina son naga suna walwala musamman yarinyar nan Lami ina jin tausayin ta a raina har bansan yadda zan kwatanta muku ba na amince kuyi komai kun cancanta ku 'ya'ya ne na gari".

Kai Habu ya d'aga "shikenan Baffah idan anyi sallar isha zamu samu zama dukkan mu don magance damuwar gidan nan kowa ya fad'i abinda ke ransa".

"Kwarai Habu kayi gaskiya haka za'ai Allah ya kaimu daren" Sabi'u yayi maganar yana mi'kewa yace "lokacin dawo da dabbobi gida yayi Habu taso muje" tashi habu yai suna fita yayin da Baffah ya bisu da kyakkyawar addu'a cikin jin dad'in samun su dayai matsayin 'ya'yansa nagartattu.

Bayan sallar isha kamar yadda suka tsaya haka suka shigo suna shimfida manyan tabarma guda biyu Baffah ya zaune suma suka zauna ga Salamatu da Ramatu Lami na gefe kad'an da Baffah saida suka nutsu kowa yai shiru Baffah yace Sabi'u ya bud'e musu taro da addu'a.

Duk hannu suka d'aga Sabi'u yana jero addu'o'i suna Amin Amin harya gama suka shafa sannan Baffah yace.

"Assalamu alaikum wa rahmatullahi wa barakatuhu".

Duk amsawa sukai "Amin alaika salam wa rahmatullahi wa barakatuhu".

Kafin Baffah yace Ramatu tayi farat tace "nifa na gaji bacci nake ji, meye ne na tara mu haka abinda ban ta'ba gani ba sai yau ko wata sabuwar tsirfarce ta samu"?.

Ba wanda ya kula Baffah dake kallon sauran yace "to alhamdulillahi ina godiya ga Allah daya nuna min wannan rana duk da banyi tunani ba na sani zakuyi mamaki zakuyi ta tambayar zuciyar ku meya faru akai kiranku ba komai bane dama na tara kune akan naji meke faruwa meke damunku kowa ya fad'i matsalar abinda ke ransa ina sauraron ku Salamatu mu fara daga kanki domin kece uwar gida kece babba"?.

'Dan shiru Salamatu tai tana tunani na 'yan mituna kafin ta d'ago tana kallon kowa tace "eh to gaskiya nikam ta bangare na babu komai ina wa kowa kallon kima da mutunci yara kuma na rikesu daya bana bambantawa ina yabawa da nagartarsu da kyakkyawar tarbiyyar da suka samu a gurin malam bani da bakin godiya gareka saidai nace Allah ya saka da alkairi kayi mana komai matsayin ka na me gida baka ta'ba gajiyawa damu ba ta bangaren abinci sutura harda kud'in kashewa na ihsani ka biya dukkan komai nauye nauyen dake kanka ka sauke ka karemu mu da karfinka da jarumtar Allah fatana a koda yaushe Allah ya kyautata ka kamar yadda ka kyautata mana" ta karasa maganar tana share hawaye.

"Amin nagode sosai Salamatu da shedar arziki da kikai min ina da ya'kinin cewa ko bayan raina zan samu yabo a gareki" juyawa yai saitin Ramatu yana cewa "Ramatu saura ke na dawo gareki kema meke damunki me yake faruwa akwai abinda ake miki wanda bakya jin dad'in sa".

Gyara zama Ramatu tai "nikwa ni akewa abinda raina baya so dan duk gidan nan babu wanda aka rainawa hankali kamar ni Kowacce bola aka d'ebo ni za'a lodawa saboda an tsane ni bansan me nai maka ba gara daka za'bi a zauna aji matsalar kowa sannan Ilyah ma yana da matsala domin munafikan yaran ka Sabi'u da Habu sun ware shi suna nuna masa 'yan ubanci komai su biyu suke babu ruwan su dashi".

Wani kallo Habu yaiwa Ilyah yana cewa "shine yace miki ba ruwan mu dashi sau nawa muna binsa yana zamewa ko abinci da kike ganin muna ci mu biyu ga Ilyan nan ki tambaye shi har gobe idan zamuci sai mun masa magana amma yace Allah ya sauwake to ya kike so muyi iya so muna nuna masa baya gani kema bakya gani bari kiji wata magana daga yau baza mu sake...........................

Katse shi Baffah yai "Habubakar bari kayi shiru haka Ramatu uwa ce gareka".

"Ah dole malam ka gama 'kwarkwance su cewa su wulakanta ni kuma yanzu dan kar nace da hannunka shine harda wani kayi shiru ni uwarsa ce tab Allah ya suturu bu'kwui inji kishiyar 'konanna nikam ban haifeshi ba yaje can kabari ya nemi uwarsa na haifi wanda na haifa".

Kowa kallon Ramatu yake da mamaki duk da dama ba ba'kuwarsu bace amma cewar Habu ba d'anta bane yaje ya nemi uwarsa a kabari bai kamata ba bata kyauta ba.

Baffah yaji zafin hakan da tace amma ya share cikin kaiwa zuciyarsa nesa yace "Ramatu wannan shine abinda yake damunki sun ware Ilyasu a cikin su babu ruwan su dashi haka ne"?.

"Eh haka ne basa kaunarsa kuma idan sharri na musu ko suna ganin na musu karya ka tambaye su basa kaunar Ilyah sam".

Kai Baffah ya jinjina "shikenan naji matsalar ki bari nayi magana dasu" kallon Sabi'u yayi yana cewa "Sabi'u meye matsalar ka matsayinka na babba cikin 'ya'yana kaine jagoran gida".

Fara magana Sabi'u yayi "ni Baffah damuwa ta rashin biyayyar da Ilyah yake maka da zama cikin samari yan shaye shaye da yake bugu da 'kari kullum idan muka ce yazo muci abinci ko kallon arziki baya mana matsayin mu na 'yan uwansa baida kamar mu a duk fadin duniya ko me zaiyi saiya yi shawara damu Baffah ka fahimtar dashi ka farkar dashi ka tuna masa matsayin mu a gunsa".

Yana rufe baki Ramatu ta wurga masa harara tana cewa "dama har wani matsayi kuke dashi a gurinsa in kuna tunanin kuna da mahimmanci ku daina Ilyah ba sa'an shirmenku bane abinci kuma bazai ci daku ba wannan doka tace dana kafa masa har abada".

Cikin 'bacin rai habu yace "to saime dan kin hana shi hakan bazai rage mu da komai b.....................

"HABUBAKAR kayi shiru dan Allah ka bari Ramatu uwace a gunka" Salamatu ta fad'a tana d'aga masa hannu huci Habu keyi ransa duk babu dad'i amma sakamakon Salamatu tayi masa magana yasa dole yai shiru bai amayar abinda ke cin ransa ba.

Baffah baice 'kala ba ya kalli Ilyah dake gefe kamar ba babu shi a gun yace "saura kai Ilyasu muna sauraron ka meye matsalar ka".

'Dan tsaki Ilyah yaja yana kau dakai kamar bazai magana sai kuma yace "ni bani da matsala kalau nake rayuwa ta idan akan haka ka tara mu ni zan fita dan ina da gurin zuwa daya fi min wannan zaman".

Kaiii duk kallon sa sukai a hasale Habu yace "Allah ya wadaran ka Ilyah wallahi kaji kunya kayi asara wannan d'abi'ar daka dauko sam babu inda zata kai ka sai halaka tun wuri ka gyara kafin lokaci ya'kure maka".

"Ban sako dakai ba Habu kada na sake jin bakinka yace min wani abu idan ba haka ba ran kowa da yake nan saiya 'baci" Ilyah ya fad'a tare da mi'kewa ya kalli Baffah dake binsa da kallo kafin yace.

"Kaja masa kunne ya fita harkata kafin ayi 'batacciya sai nayi abinda kowa zaiyi danasani".

"Yau d'an halak haka nake son ji karka ragawa kowa" Ramatu ta fad'a tana hararar Habu.

'Diban takalmansa Ilyah yai zai fita Baffah ya dakatar dashi "kada ka fita Ilyasu bamu gama magana ba ka zauna ban baka izinin tafiya ba".

Batare da Ilyah ya juyo ko ya dakata daga tafiyar da yake yace "dama umarnin ka nake nema saika sani abu zanyi basan zauna ba na fita zaka iya sawa a taro ni".

Da kallo suka bishi yana fita Baffah da gabadaya zuciyar sa ke masa zafi take masa shiru yayi ya rasa me zaiwa Ilyah ya dawo kan hanya addu'ar nan kullum yi yake ba fashi amma abun na Ilyah gaba yake saidai bazai 'kosa ba zaici gaba da nema masa shiriya...................

"To nima dai zan tashi dan na gaji bacci nake ji" Ramatu ta fad'a tana mikewa ta shige d'aki tare da rufo kofa.

Har lokacin Baffah yana shiru ganin yanayin yasa Sabi'u cewa "kayi hakuri Baffah mun 'bata maka rai ka yafe mu na dauka idan muka samu zama zamu fahimci juna ashe saidai mu fahimci damuwa munyi kuskure bansan me zamuyi yanzu ba na kasa gane komai".

"Me zamuyi kuwa daya wuce hakuri da addu'a dan Allah Baffah kayi hakuri ka kwantar da hankalin ka insha Allahu komai zai setu" Habu yai maganar.

Ganin dai jiya iyau Baffah baice komai yasa Sabi'u cewa "BAFFAH ka gafarce mu dan Allah idan mun saka a wani hali".

'Dagowa Baffah yayi yana kallon su tare da girgiza kai yace "Sabi'u Habu Allah ya muku albarka baku ta'ba 'bata min ku farin ciki nane ina alfahari da samunku ina fata ku kasance cikin farin ciki har abada Allah ya tsare min ku ya shiga al'amarin ku ya baku 'ya'ya da matan aure na gari yasa ku gama da duniya lafiya duk abinda kuka san zaisa naji dad'i kuna kokarin yi min Allah yasa kuma ku samu masu yi muku".

"Amin Baffah mun gode sosai".

"Karku damu kuje ku kwanta" mi'kewa sukai suna masa saida safe ya rage daga shi sai Salamatu da Lami kallon Lami yai yana cewa "kiyi hakuri ke ba'a tambayi taki damuwar ba ko"? Kai Lami ta girgiza tana share hawaye cikin takaicin abinda taga Ilyah ya masa tace "ka gafarce ni Baffah ka yafewa yaya Ilyah abinda yake maka ka bishi da addu'a ka masa fatan gamawa da duniya lafiya shine fata na".

Kallonta Baffah keyi yarinyar nan za'a tona kafin a samu irinta zai wahala shiyasa koda yaushe yake farin ciki da samunta matsayin 'ya gareshi sake kallonta yayi yana cewa "kada ki damu indai wannan shine burinki zan cika miki tashi kije ki kwanta" mi'kewa tayi tana masa saida safe ta tafi, numfasawa Salamatu tai tana kallon Baffah tace.

"Malam na sani kana cikin damuwa a gidan nan mun gaza gyara zamantakewar mu badan bazamu iya ba sai rarrabuwar kai nayi tunanin a yau zamu magance matsalar mu amma sai naga abun yaci tura dan Allah malam kayi hakuri" kai Baffah ya girgiza "babu komai Salamatu tashi kije Allah ya mana sutura" Amin tace tana mikewa itama ta shiga d'akinta aka bar iya Baffah a tsakar gida yana sa'ka da warwara ya dad'e kafin ya mi'ke yana daukar buta yai alwala ya shiga d'akinsa ya fara nafila yana rokon daidaituwar al'amari a tsakanin zaman zuriyar gidan sa.
Chapter 29 · 0% Book details