Sashe 83
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai ya d'aga masa "no da ace tafiya na zai yuwu ayau zan tafi Isham Ina so nayi magana da Abba".
"Ok shikenan Buddy na fahimta muje" mi'kewa Asad yai yana rufe laptop d'in suka fita daga gidan domin suje gurin sir murtih akan maganarsa zuwa gida.
<OSUN> gidan amare
Uhmm Indo/Dauda munzo ganin cin amarci duk da ba'a gayyace mu sayan baki☺️ ba fans ga mota🚗 ga Wanda zaije?😶 kuzo muje nikam zanje zanga yadda ake soyayya🙈🤸.
Indo tana kwance🤭 akan katuwar katifa ta lullu'be jikinta duka amma banda fuskarta idonta biyu suna rufe tanajin qarar 'yar qaramar Tv su dake aje akan wani center table saidai ba barci take ba shigowar ango Dauda😂 yasa da sauri taja bargon tana rufe kanta tare da yin tsit kamar ta mutu zama yai a bakin katifar yana janye abun rufar yace.
"Indo".
Shiru tai ta kasa amsawa saida ya kirata a karo na biyu sannan da'kyar ta amsa amma har lokacin bata bud'e ido ba yana rufe kamar makauniya.
"Ki tashi daga kwanciyar haka ki shirya inafa da mutane zuwa nan da jimawa zakiga sun fara shigowa tayani murna kuma suzo su sameki a haka ai sai kisa naji kunya".
Ita dai shiru tai tana sauraron sa kamar ta fashe da kuka domin da yasan yadda take ji a jikinta da bazaice ta tashi ba kawai ya kakkarya mata 'kasusuwan jiki taya zata iya tashi balle har tayi tafiya............
Tana cikin tunani taji ya d'agota qara tayi tana samai kuka zaro ido yai yana kallon ta da mamaki kafin yace.
"Lafiya meya faru"?.
Cikin kuka Indo tace "nifa bazan iya tashi ba".
Kallon yadda take shashshe'ka Dauda yai yana jinjina kai bai sake magana ba ya mi'ke tsaye yana d'aukarta yai waje da ita domin yanzu kam ya yarda bada banza ba take kuka ba Indo tana da juriya duk abinda kaga tayi masa rauni to lallai ka bincike shi barota yayi a toilet din ya dawo d'akin ya gyara ko'ina ya share ya fesa air freshener😛 sauran kayan marmarin da basu shanye ba ya d'auke yakai kitchen kafin ya koma toilet d'in ya d'aukota yana dawowa da ita d'aki a daddafe tasha tea saboda jin wani mayan zazza'bi yana shirin kamata kawai ta koma kan katifar ta sake kwanciya baice mata komai ba ya tattare kayan suma ya kai kitchen ya dawo yana zama akan doguwar kujera ya maida hankalin sa kan TV Indo kam tana lullu'be batasan abinda yake ba shine madai lokaci zuwa lokaci yake d'agowa ya kalleta har tayi barci ganin haka yasa ya mi'ke yana d'aukar key d'in mashin ya fita zuwa kafin ta farka ya dawo.
INDIA CHENNAI🏥
Wani qwararran doctor ne zaune cikin office gabansa su Ajeeb ne yana musu bayanin halin da Khimiyyah take na cewa insha Allahu shi ya gano inda matsalar take bayan bincike daya zurfafa yayi game da ita wanda sauran likitocin suka gagara ya tabbatar musu da cewa tana gaf da farfadowa saidai bashi da tabbacin zata dawo cikin hayyacinta maybe kwakwalwar ta baza ta'bu sanyi farin cikin jin zata farfad'o amma kuma sunyi ba'kin cikin cewa zata samu ta'buwar kwakwalwa.
Ajeeb dake kallonsa cike da damuwa yace "Amma doctor babu wata hanyar da za'a bi ta dawo cikin hankalin ta bayan ta farfad'o dan saboda akwai matsala ace bata dawo daidai yadda take da ba gashi an d'auki shekaru a haka".
Kai doctor "eh gaskiya babu tabbacin dawowarta yadda take da ba nace zata dauwama a ta'bin 'kwa'kwalwar bane a'a zata iya dawowa daidai cikin hankalinta sosai saidai yin hakan ne zai zamo wahala".
"Ok shikenan doctor yanzu me kake gani za'ayi"?.
'Dan shiru doctor yai zuwa wani lokaci ya d'ago yana kallon su yace "yanzu bansan yadda zance muku ba amma ku bani lokaci akan matsalarku insha Allahu I will try to do my best na ganin ta dawo yadda take maybe idan ta dawo normal zakusa hannu ayi mata wankin 'kwa'kwalwa idan akai sa'a sai a dace".
Kai Ajeeb ya d'aga "ok doctor mun gode sosai muna jira" ya karasa maganar yana mi'ko masa hannu🤝 gaisawa sukai doctor nacewa.
"Ok sai kun jini".
Sannan ya mi'kawa Ameer ma sukai musabaha kafin ya mi'ke suka fito tare zaiyi musu rakiya yana sake basu haske da 'karin bayani har sukazo reception indai Mami da Annur suke jiransu anan Ajeeb yake sanar dasu yadda sukai da doctor yanzu ga abinda yace bayan ta farfad'o za'ai mata wankin 'kwa'kwalwa ita dai Mami shiru tai kawai tana sauraren su suna zancen tsakanin su uku batace komai ba saidai ta damu yarinyar nan ta farfad'o Allah ya bata lafiya subar India su koma gida gashi abin takaicin d'azu ta gama waya da Asad yace mata gobe zaije Nigeria ji take kamar ta barsu Ajeeb taje ta ganshi ya ganta yadda suka dad'e basu had'u ba shekara ba d'aya ba kuma ba biyu ba saidai ba yadda ta iya dole ta danne duk yadda takejin kewarsa a ranta domin yanzu idan taje zatasha magana agun Sultana Hadizah zataga kamar tayi haka ne dan ta nuna ta damu da d'anta shiyasa ta taho tabaro mata tata 'yar cikin halin rai ko mutuwa balle gashi ana zancen wankin 'kwa'kwalwa idan Sultana Hadizah taji hauka ne kawai bazatai ba.
👑EMIRATE👑
Asad kam ya diro cikin masarauta lafiya saidai rashin Mami ba karamin ciwo ya haifar masa ba ji yake kamar yaje Chennai ya ganta saidai yasan idan yaje za'ai ba dad'i shiyasa kawai ya 'kyale bai cewa kowa komai ba abun dai daya bashi mamaki kuma ya faranta masa ransa shine ganin yadda Amjadd ya tsaya tsayin daka ya kula masa da stockyards d'insa tamkar yana nan dan idan ba bud'e masa ido sukai ba gani yai sunyi wani irin girma 'yar giwar nan daya barta a jaririya yanzu itama ta zama uwa balle azo 'bangaren zakinsa humm wannan in ana sallah ba'a magana gashinsa har wani she'ki yake da'kyar yake tafiya tsabar koshi.
Bayan kwana sha biyar mighty Alhussain ne yana zaune cikin parlon sa yana waya da Ajeeb Sultana Hadizah ta shigo ta riski zancen da suke hankalinta ya tashi murna ta rufeta jin wai Khimiyyanta ta farfad'o amma a halin hauka ko bari ya gama wayar batai ba ta fashe da kuka wanda da sauri Alhussain ya kashe wayar yana mata kallon mamaki yace
"Ke kuma wannan sakarcin fa fita anan bana son hauka"?.
Jin abinda yace yasa Sultana Hadizah d'ora hannu aka tana cewa "na shiga uku na lalace shikenan na fito rana yanzun wankin 'kwa'kwalwa za'ai wa Khimiyyah? Asad ya cuceni bazan ta'ba yafe masa ba".
Kai Mai girma Alhussain ya jinjina yana kallon ta yace "Hadizah fita anan kafin kisa na aikata abinda baza aji dad'in saba".
Bud'e baki Tai zatai magana cikin tsawa yace "get of my sight" jin tsawar dayai mata yasa da sauri tai waje tana sake fashewa da kuka.
Takaici ne ya cikashi har a ransa yana kokwanton anya itama Sultana Hadizah bata samu ta'bin 'kwa'kwalwar ba dan yawancin lokuta bata abu na masu cikekken hankali tsuka yaja yana tashi ganin kiran mai martaba Alhassan yasa ya d'aga cikin girmamawa yana gaidashi wanda in kaga yadda yake bashi girma saika rantse da Allah ba rana d'aya aka haifesu ba magana ya masa akan yazo part dinsa yanzu ya sameshi amsa masa yai yana sauke wayar kafin ya mi'ke yana fita zuwa 'bangaren mai martaba a zaune ya sameshi ga Asad a gabansa da alama magana suke zama yai da murmushi a fuskarsa yace.
"D'an gidana yau duk ban ganka ba sai yanzu Ina kaje ne"?.
Gaida shi Asad yai murya a nutse yace "Ina part d'ina aiki nake yi".
"Ok Allah ya taimaka d'an gidana".
Maida hankalin sa kan me martaba yai yana cewa "yaya ka Kira nine"?.
Kai Mai martaba ya d'aga yana cewa "eh Alhussain magana ce akan Khimiyyah dama nace a bari sai Asad ya dawo gida za'ayi ta".
'Dan shiru mai girma Alhussain yai cikin damuwa shifa harga Allah bayaso a ri'ka tada maganar ma sam d'agowa yai yana kallon d'an uwan nasa yace .
"Amma yaya nikam nace abar maganar dan Allah kada a tada zaune tsaye yanzu nayi waya da Ajeeb ya fad'a min cewa ta farfad'o saidai bata hankalinta ba sai anyi mata wankin 'kwa'kwalwa idan akai sa'a zata dawo daidai shiyasa nace a 'kyale maganar komai ya wuce"…
Kai Mai martaba ya girgiza yana cewa "amma meyasa zamu bar maganar bayan kasan me matarka tace tad'au abun da zafi dole mu zauna akan haka amma sai bayan sun dawo daga India ayi komai a gaban kowa karka damu d'an uwana babu sa'banin dazai shiga tsakanin mu insha Allahu mace baza ta ta'ba raba muba".
Sauke ajiyar zuciya Mai girma Alhussain yai yana cewa "shikenan to yaya Allah ya rufa asiri" kallon Asad wanda ke saurarensu yai yana cewa "d'an gidana muje kai min rakiya zuwa wani guri dama nayi kewar fita tare dakai tsawon shekaru".
Murmushi mai martaba yai yana duban Asad batare da yace komai ba Asad ya mi'ke suna fita daga parlon daidai kiran Mami ya shigo wayar Mai martaba ya katse yana danna kiranta ta d'aga suna magana duka dai labarin d'aya ne akan Khimiyyah ne.
🌆KANO🌆
Nurain ne zaune gaban mahaifansa suna masa fad'an ya akai Zainab tai yaji watanni kusa hud'u duk dan ya mayar dasu kakanun mutane shine bai iya zuwa ya sanar dasu ba har saida iyayen Zainab d'in sukaga shirun yayi yawa sukai magana shi kuma Nurain ya nuna musu ga abinda ya hadasu har tayi yajin.
Wani kallo Mum tai masa tana cewa "au kuma dan zaka qara aure tsabar shashanci baka zo kayi magana damu ba kawai saika kama fad'a da matarka wacce yarinya kake so"?.
Shiru Nurain yai cikin fargaba yana kuma addu'a da fatan Allah yasa kada su hana shi idan ya bayyana musu ita...........
Saukar muryar Daddy yaji yace "Nuraddeen ba magana Mumynka take maka ba kayi shiru wacce yarinya kake so a ina take waye ubanta"?.
Cikin d'an samun 'kwarin gwiwa Nurain ya kalli Daddy yana cewa "Daddy Nafisa ce 'yar gidan Alhaji Ilyasu🙊".
Da alamar tambaya Daddy yace "waye Alhaji Ilyasu kuma a ina yake"?.
"Ok shikenan Buddy na fahimta muje" mi'kewa Asad yai yana rufe laptop d'in suka fita daga gidan domin suje gurin sir murtih akan maganarsa zuwa gida.
<OSUN> gidan amare
Uhmm Indo/Dauda munzo ganin cin amarci duk da ba'a gayyace mu sayan baki☺️ ba fans ga mota🚗 ga Wanda zaije?😶 kuzo muje nikam zanje zanga yadda ake soyayya🙈🤸.
Indo tana kwance🤭 akan katuwar katifa ta lullu'be jikinta duka amma banda fuskarta idonta biyu suna rufe tanajin qarar 'yar qaramar Tv su dake aje akan wani center table saidai ba barci take ba shigowar ango Dauda😂 yasa da sauri taja bargon tana rufe kanta tare da yin tsit kamar ta mutu zama yai a bakin katifar yana janye abun rufar yace.
"Indo".
Shiru tai ta kasa amsawa saida ya kirata a karo na biyu sannan da'kyar ta amsa amma har lokacin bata bud'e ido ba yana rufe kamar makauniya.
"Ki tashi daga kwanciyar haka ki shirya inafa da mutane zuwa nan da jimawa zakiga sun fara shigowa tayani murna kuma suzo su sameki a haka ai sai kisa naji kunya".
Ita dai shiru tai tana sauraron sa kamar ta fashe da kuka domin da yasan yadda take ji a jikinta da bazaice ta tashi ba kawai ya kakkarya mata 'kasusuwan jiki taya zata iya tashi balle har tayi tafiya............
Tana cikin tunani taji ya d'agota qara tayi tana samai kuka zaro ido yai yana kallon ta da mamaki kafin yace.
"Lafiya meya faru"?.
Cikin kuka Indo tace "nifa bazan iya tashi ba".
Kallon yadda take shashshe'ka Dauda yai yana jinjina kai bai sake magana ba ya mi'ke tsaye yana d'aukarta yai waje da ita domin yanzu kam ya yarda bada banza ba take kuka ba Indo tana da juriya duk abinda kaga tayi masa rauni to lallai ka bincike shi barota yayi a toilet din ya dawo d'akin ya gyara ko'ina ya share ya fesa air freshener😛 sauran kayan marmarin da basu shanye ba ya d'auke yakai kitchen kafin ya koma toilet d'in ya d'aukota yana dawowa da ita d'aki a daddafe tasha tea saboda jin wani mayan zazza'bi yana shirin kamata kawai ta koma kan katifar ta sake kwanciya baice mata komai ba ya tattare kayan suma ya kai kitchen ya dawo yana zama akan doguwar kujera ya maida hankalin sa kan TV Indo kam tana lullu'be batasan abinda yake ba shine madai lokaci zuwa lokaci yake d'agowa ya kalleta har tayi barci ganin haka yasa ya mi'ke yana d'aukar key d'in mashin ya fita zuwa kafin ta farka ya dawo.
INDIA CHENNAI🏥
Wani qwararran doctor ne zaune cikin office gabansa su Ajeeb ne yana musu bayanin halin da Khimiyyah take na cewa insha Allahu shi ya gano inda matsalar take bayan bincike daya zurfafa yayi game da ita wanda sauran likitocin suka gagara ya tabbatar musu da cewa tana gaf da farfadowa saidai bashi da tabbacin zata dawo cikin hayyacinta maybe kwakwalwar ta baza ta'bu sanyi farin cikin jin zata farfad'o amma kuma sunyi ba'kin cikin cewa zata samu ta'buwar kwakwalwa.
Ajeeb dake kallonsa cike da damuwa yace "Amma doctor babu wata hanyar da za'a bi ta dawo cikin hankalin ta bayan ta farfad'o dan saboda akwai matsala ace bata dawo daidai yadda take da ba gashi an d'auki shekaru a haka".
Kai doctor "eh gaskiya babu tabbacin dawowarta yadda take da ba nace zata dauwama a ta'bin 'kwa'kwalwar bane a'a zata iya dawowa daidai cikin hankalinta sosai saidai yin hakan ne zai zamo wahala".
"Ok shikenan doctor yanzu me kake gani za'ayi"?.
'Dan shiru doctor yai zuwa wani lokaci ya d'ago yana kallon su yace "yanzu bansan yadda zance muku ba amma ku bani lokaci akan matsalarku insha Allahu I will try to do my best na ganin ta dawo yadda take maybe idan ta dawo normal zakusa hannu ayi mata wankin 'kwa'kwalwa idan akai sa'a sai a dace".
Kai Ajeeb ya d'aga "ok doctor mun gode sosai muna jira" ya karasa maganar yana mi'ko masa hannu🤝 gaisawa sukai doctor nacewa.
"Ok sai kun jini".
Sannan ya mi'kawa Ameer ma sukai musabaha kafin ya mi'ke suka fito tare zaiyi musu rakiya yana sake basu haske da 'karin bayani har sukazo reception indai Mami da Annur suke jiransu anan Ajeeb yake sanar dasu yadda sukai da doctor yanzu ga abinda yace bayan ta farfad'o za'ai mata wankin 'kwa'kwalwa ita dai Mami shiru tai kawai tana sauraren su suna zancen tsakanin su uku batace komai ba saidai ta damu yarinyar nan ta farfad'o Allah ya bata lafiya subar India su koma gida gashi abin takaicin d'azu ta gama waya da Asad yace mata gobe zaije Nigeria ji take kamar ta barsu Ajeeb taje ta ganshi ya ganta yadda suka dad'e basu had'u ba shekara ba d'aya ba kuma ba biyu ba saidai ba yadda ta iya dole ta danne duk yadda takejin kewarsa a ranta domin yanzu idan taje zatasha magana agun Sultana Hadizah zataga kamar tayi haka ne dan ta nuna ta damu da d'anta shiyasa ta taho tabaro mata tata 'yar cikin halin rai ko mutuwa balle gashi ana zancen wankin 'kwa'kwalwa idan Sultana Hadizah taji hauka ne kawai bazatai ba.
👑EMIRATE👑
Asad kam ya diro cikin masarauta lafiya saidai rashin Mami ba karamin ciwo ya haifar masa ba ji yake kamar yaje Chennai ya ganta saidai yasan idan yaje za'ai ba dad'i shiyasa kawai ya 'kyale bai cewa kowa komai ba abun dai daya bashi mamaki kuma ya faranta masa ransa shine ganin yadda Amjadd ya tsaya tsayin daka ya kula masa da stockyards d'insa tamkar yana nan dan idan ba bud'e masa ido sukai ba gani yai sunyi wani irin girma 'yar giwar nan daya barta a jaririya yanzu itama ta zama uwa balle azo 'bangaren zakinsa humm wannan in ana sallah ba'a magana gashinsa har wani she'ki yake da'kyar yake tafiya tsabar koshi.
Bayan kwana sha biyar mighty Alhussain ne yana zaune cikin parlon sa yana waya da Ajeeb Sultana Hadizah ta shigo ta riski zancen da suke hankalinta ya tashi murna ta rufeta jin wai Khimiyyanta ta farfad'o amma a halin hauka ko bari ya gama wayar batai ba ta fashe da kuka wanda da sauri Alhussain ya kashe wayar yana mata kallon mamaki yace
"Ke kuma wannan sakarcin fa fita anan bana son hauka"?.
Jin abinda yace yasa Sultana Hadizah d'ora hannu aka tana cewa "na shiga uku na lalace shikenan na fito rana yanzun wankin 'kwa'kwalwa za'ai wa Khimiyyah? Asad ya cuceni bazan ta'ba yafe masa ba".
Kai Mai girma Alhussain ya jinjina yana kallon ta yace "Hadizah fita anan kafin kisa na aikata abinda baza aji dad'in saba".
Bud'e baki Tai zatai magana cikin tsawa yace "get of my sight" jin tsawar dayai mata yasa da sauri tai waje tana sake fashewa da kuka.
Takaici ne ya cikashi har a ransa yana kokwanton anya itama Sultana Hadizah bata samu ta'bin 'kwa'kwalwar ba dan yawancin lokuta bata abu na masu cikekken hankali tsuka yaja yana tashi ganin kiran mai martaba Alhassan yasa ya d'aga cikin girmamawa yana gaidashi wanda in kaga yadda yake bashi girma saika rantse da Allah ba rana d'aya aka haifesu ba magana ya masa akan yazo part dinsa yanzu ya sameshi amsa masa yai yana sauke wayar kafin ya mi'ke yana fita zuwa 'bangaren mai martaba a zaune ya sameshi ga Asad a gabansa da alama magana suke zama yai da murmushi a fuskarsa yace.
"D'an gidana yau duk ban ganka ba sai yanzu Ina kaje ne"?.
Gaida shi Asad yai murya a nutse yace "Ina part d'ina aiki nake yi".
"Ok Allah ya taimaka d'an gidana".
Maida hankalin sa kan me martaba yai yana cewa "yaya ka Kira nine"?.
Kai Mai martaba ya d'aga yana cewa "eh Alhussain magana ce akan Khimiyyah dama nace a bari sai Asad ya dawo gida za'ayi ta".
'Dan shiru mai girma Alhussain yai cikin damuwa shifa harga Allah bayaso a ri'ka tada maganar ma sam d'agowa yai yana kallon d'an uwan nasa yace .
"Amma yaya nikam nace abar maganar dan Allah kada a tada zaune tsaye yanzu nayi waya da Ajeeb ya fad'a min cewa ta farfad'o saidai bata hankalinta ba sai anyi mata wankin 'kwa'kwalwa idan akai sa'a zata dawo daidai shiyasa nace a 'kyale maganar komai ya wuce"…
Kai Mai martaba ya girgiza yana cewa "amma meyasa zamu bar maganar bayan kasan me matarka tace tad'au abun da zafi dole mu zauna akan haka amma sai bayan sun dawo daga India ayi komai a gaban kowa karka damu d'an uwana babu sa'banin dazai shiga tsakanin mu insha Allahu mace baza ta ta'ba raba muba".
Sauke ajiyar zuciya Mai girma Alhussain yai yana cewa "shikenan to yaya Allah ya rufa asiri" kallon Asad wanda ke saurarensu yai yana cewa "d'an gidana muje kai min rakiya zuwa wani guri dama nayi kewar fita tare dakai tsawon shekaru".
Murmushi mai martaba yai yana duban Asad batare da yace komai ba Asad ya mi'ke suna fita daga parlon daidai kiran Mami ya shigo wayar Mai martaba ya katse yana danna kiranta ta d'aga suna magana duka dai labarin d'aya ne akan Khimiyyah ne.
🌆KANO🌆
Nurain ne zaune gaban mahaifansa suna masa fad'an ya akai Zainab tai yaji watanni kusa hud'u duk dan ya mayar dasu kakanun mutane shine bai iya zuwa ya sanar dasu ba har saida iyayen Zainab d'in sukaga shirun yayi yawa sukai magana shi kuma Nurain ya nuna musu ga abinda ya hadasu har tayi yajin.
Wani kallo Mum tai masa tana cewa "au kuma dan zaka qara aure tsabar shashanci baka zo kayi magana damu ba kawai saika kama fad'a da matarka wacce yarinya kake so"?.
Shiru Nurain yai cikin fargaba yana kuma addu'a da fatan Allah yasa kada su hana shi idan ya bayyana musu ita...........
Saukar muryar Daddy yaji yace "Nuraddeen ba magana Mumynka take maka ba kayi shiru wacce yarinya kake so a ina take waye ubanta"?.
Cikin d'an samun 'kwarin gwiwa Nurain ya kalli Daddy yana cewa "Daddy Nafisa ce 'yar gidan Alhaji Ilyasu🙊".
Da alamar tambaya Daddy yace "waye Alhaji Ilyasu kuma a ina yake"?.