Sashe 51
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai Ajeeb ya d'aga "eh tambayar ka nake ina son sani ka fad'a min yanzun nan ko jiki yai tsami🙄" wani kallo Asad ya watsa masa ta nuna cewa bismilllah kafin ya kara gaba daga nan yai bangaren mahaifansu dukkan su suna tare har mai girma Alhussain da matansa da kuma yaransa yan mata guda hud'u kowacce ta hakimce cike da sarauta da sallama ya shiga yana gaidasu ya samu wuri d'an nesa dasu kan wasu kyawawan cushions masu kalar golden and white ya zauna bai sake cewa kowa komai ba Alhussain yace.
" 'Dan gidana meya faru naga ka ware kanka kai d'aya ina sauran suke"? 'Dagowa Asad yai zaiyi magana suma suka shigo da sallama duk gurin sa suka nufa suna zama sai aiko masa da harara suke musamman Ajeeb kamar idonsa zai fito waje ya kalli Alhussain yana cewa.
"Daddy kayi masa magana ya daina harara ta dan naga yau tsokana yake ji tun muna part dinmu yake zagina 🙊".
Murmushi Alhussain yai yana cewa "babyn Mami meyasa kake harararsa".
Asad na yiwa Ajeeb kallon mamakin sharrin daya 'kuga masa yace "ni ban zageshi ba shine kawai ina barci na ya zuba min ruwan fridge mai sanyi a jikina wai hakan bai ishe shiba saina gaidashi kamar wani ubana".
Kallon Ajeeb Alhussain yai yana cewa "to kaji meyasa zaka zuba masa ruwa"?.
"Daddy ya'ki tashi ne gashi rana ta fito baiyi sallah ba shine naji haushi na zuba masa".
"Ok to ka yarda bakai daidai ba ka bashi hakuri, meye abin d'aga hankali bayan kwanan nan zakuyi bankwana zai wuce Marshall islands ko duk fad'an karshen ne"? Ya karasa maganar da murmushi dan shiru Ajeeb yai sai kuma ya kalli Asad daya d'auke kai yace "kayi hakuri Bros" ya fad'a yana mi'ka masa hannu d'agowa Asad yai ya kalleshi dan kar yaje sha'kiyanci yake masa sai kuma yaga serious face dan haka shima ya mi'ko masa hannun sukai musahaba ya mi'kewa Ameer ma sannan yace "nima kayi hakuri" kai Ajeeb ya d'aga "ba komai ai mun saba indai rigima ce zuwa jimawa ma zamuyi wata jiki da jini kuma Asad nefa da Ajeeb" 'yar dariya yasa sauran sukai dan haka ne abinda Ajeeb d'in yace kullum suna cikin fad'a indai suna tare kamar Tom and Jerry 🤗 Alhussain yace "shikenan komai ya wuce Asad zai tafi tare da abokina abdul-kareem ranar Monday sai yayi shekara biyar zai dawo kuyi masa fatan alkairi da samun nasara" hannu Ajeeb ya bud'e yana cewa "a ro'ka da babban masaki nine mai karantowa" shiru kowa yai Ajeeb na zayyano addu'o'in nasara ga d'an uwansa saida ya gama kowa zai shafa yace "addu'ata ta 'karshe gareka Asad Allah ya baka mace jaruma mai ra'ayi irin naka amma banda fusata da son yin dambe da d'an uwa 🙉" Ajeeb na rufe baki khimiyyah da Makiyyah har had'a baki sukai kowacce na cewa "ai nice" kallon su Alhussain yai bayan sun shafa addu'ar yace "ai kune me"? Caraf khimiyyah tace "nice jarumar domin ina sonsa" zaro ido Makiyyah tai "kan bala'i kina sonsa a ina bayan na riga ki tun wuri kije ki nemi naki kafin lokaci ya'kure miki" a masife khimiyyah tace "wallh baki isa ba hauka ma kenan me kike nufi da na nemi nawa kar lokaci ya kure min? Humm Makiyyah kenan sorry yarinya wallahi Asad nawa ne gaba da baya gara kisan nayi" Makiyyah na shirin magana ganin shashancin da suke Alhussain ya d'aga musu hannu.
"Kai keep quite wanne irin shirme ne wannan kukeyi"? Khimiyyah na huci tace "Abba kana jinta abinda take cewa fa wallahi impossible na zuba miki ido yarinya wuce nan kinyi kad'an.............
Cikin tsawa Alhussain yace "zaki min shiru ko sai jikinki ya fad'a miki kada na sake jin irin wannan maganar a bakinku kowa ta ha'kura tunda ba dole bane dama ai kuna sonshi amma da yan uwantaka ba aureba karna sake jin haka dan gidana ba aure zaiyi ba aikinsa zaisa a gaba ku mayar da hankalin ku jikin ku yaushe kuka d'ago har kukasan miye duniya da abinda yake cikinta"?.
Fuskar khimiyyah ranta a 'bace take aikawa da Makiyyah mugun kallo tace "amma Abba.........,.......
"Ke ki rufe min baki nace tashi anan" mi'kewa Khimiyyah tai tana kumbura baki ta fice tana maganganu 'kasa 'kasa sauran ma mi'kewa sukai suna fita daga part din Makiyyah na shiga bedroom Khimiyyah ta sha'ko wuyanta tana cewa "ke har kin isa shiga tsakani na da muradi na wacece ke me kike ta'kama dashi"? Ri'ke hannun ta Makiyyah tai tana 'bam'barewa daga wuyanta tace "bakiyi karya ba Khimiyyah na isa ne tun farko inaji a jikina Asad nawa ne mijina ne shine mafarki na dan haka ta nuna Khimiyyah da yatsa taci gaba "kada ki kuskura ki koyi son wanda na gama mi'ka wuya sakankancewa da soyayyar ta idan ba haka ba kina tare da wahala".
Bige mata hannu Khimiyyah tai a fusace tace "hannu 'kasa yarinya kada ki sake gigin nuna min yatsa idan ba haka ba saina balla shi".
"Ke har kin isa kice zaki min wani abu"? Makiyyah ta tambaye ta itama zuciyarta na turiri.
'Kirji Khimiyyah ta buga "eh na isa harna wuce inda kike zato kuma kici gaba da shiga gonata wallahi wata rana za'ai babu ke dan saina 'badda ke".
Ta'be baki Makiyyah tai "humm gyara kalaman ki yan mata saidai mu 'badda juna tare dan baki isa na zuba miki ido ba nima ba kanwar lasa bace matukar kika fad'a min cuta ni kuma saina fad'a miki mutuwa😡😠".
Gajiya da shirmensa Shaukiyyah tai wani uban tsakin takaici taja tana cewa "wai dan Allah malamai maye haka ne kun ishemu da wannan wayon 'kauyen naku gaskiya ku barmu mu sarara ko kuma ku fita a bedroom d'in akan me muna zaune lafiya zaku hana mu jin dad'i gashi abinda haushin wanda kuke fad'an akansa baisan kunayi ba bai damu daku ba bakwa gaban sa na tabbata duk tsiya ko yana ra'ayin ku saidai ya auri d'aya kunsan bazei auri ku duka ba amma kuka tsaya kuna wahalar da kanku kun manta matar mutum kabarin sa maybe babu mai rabo a cikin ku saikun gama haukan ku yaje ya auro wata daga waje gashi kun girgiza junanku da fad'a da 'kiyayya meyasa ku bakwa tunani ne? Haba kamar wasu ma'kiyan juna gaskiya nake fad'a muku koda bai shafeni ba kuna abinda bai dace ba ku gyara ku mayar da hankali".
Wani banzan kallo duk su biyun suka watsa mata Khimiyyah tace "d'an maimaita abinda kikace banji sosai ba"?.
Had'e rai Shaukiyyah tai "bazan maimaita ba kada Allah yasa ki gane duk ranar da kika bud'e ido kikaga Asad da matarsa maybe ranar kyayi surrender ki gane kinyi kuskure".
"Ai wallahi Shaukiyyah babu ranar da zata zo wacce zanji wata nadama ta kamani har abada kuma zan iya yin komai dan cikar burina dan na samu abinda nake so kin gane? Dan haka bar 'bata bakinki a kaina ba fahimtarki zanyi ba".
Kai Shaukiyyah ta jinjina tana cewa "shikenan Allah yasa ki gane nikam shine fatana da ban nuna inason kowa ba a cikin su gashi na zauna lafiya sannan ban wahalar da zuciyata ba nasa mata rai akan abinda nasan bazata samu ba".
A banza Shaukiyyah take magana babu wanda ya fahimce ta a cikin su gani suke ba'kin ciki take musu ko dai akwai abinda take boyewa a ranta ita kuwa a zahirin gaskiya tana nuna musu abinda zai fishe su ne kar zuwa gaba wani mummunan abu ya faru wanda baza aji dad'i ba.
Khaldiyyah dake kwance da littafi a hannunta tana karatu batai musu magana ba tunda suka fara abinsu sai yanzu ta tashi zaune tana rufe littafin ta aje tare da kallon su har yanzu suna aikawa juna kallan kallo murmushi tai tana sake kai kallonta kan Shaukiyyah data d'auke kai daga saitinsu domin tayi iya yinta sun 'ki fahimtar ta kai ta girgiza tana cewa.
"Haba ku kuwa ladies👯 meye matsalar kune zaku li'kewa mutum daya? Ku bari na sasanta na raba muku fad'an inace mu hud'u ne kuma suma su hud'u ne? Ni a nawa ganin kawai kowa ta kama d'aya zaifi koba haka ba"?.
Kallonta Khimiyyah tai fuska ba rahma tace "me kike nufi su waye su hud'u"?.
Gyara zama Khaldiyyah tai "ina nufin mu hud'u suma su hud'u ne an raba kowa saita kama d'aya nikam dama na za'bi nawa tun tuni amma kunga da ban nuna ba ai na zauna lafiya lokaci nake jira wanda da kansa zai fahimta basai na furta masa ba domin neman kima da daraja a idonsa".
"Waye kike so a cikin su amma badai Asad ba"? Khimiyyah tai maganar tana kallon Khaldiyyah datai murmushi tace "a'a rufa min asiri ni kaza 🐔 abinci na dusa waneni Asad yafi 'karfina 😊 saidai manyan mata irinku" ta karasa maganar tana dariya.
'Kara had'e rai Khimiyyah tai "ai ba dogon bayani na nemi kimin ba cewa nai waye kike so a cikin su"?.
"Humm wannan kuma bai shafeki ba Khimiyyah dama an fad'a miki ni gariyace dazan fad'a miki wanda nake so wato kije ki fad'a masa batare dana bi a hankali ya soni ta sassaukar hanya ba ki ri'ke naki na ri'ke nawa".
Numfasawa Shaukiyyah tai tana cewa "nikam zan fad'i wanda nake so ba kuma bana jin shakkar a fad'a masa ban sani ba ko shima ya kamu da sona lokacin da banyi zato ba".
Dariya Khaldiyyah tai "ke wa kike so Allah yasa ba wanda nake so bane dan nima yanzu zamu hau sama mu fad'o".
Kafad'a Shaukiyyah ta d'aga tana cewa "to muhau man tunda yayin fad'an ake nikam wanda nake so "Ameer ne Allah yasa ke bashi bane"?.
Cikin tsokana Khaldiyyah tace "kika ce Ameer kike so? Kai Shaukiyyah ta d'aga Khaldiyyah taci gaba "innalillahi ai nima shine za'bin nawa"😲 zaro ido Shaukiyyah tai kamar zai fito waje tace "dan Allah da gaske kike Ameer kike so? Nashiga uku yanzu ya zanyi bazan iya fad'a dake ba koda hakan zai zama cutarwa ga rayuwata zan bar miki shi na dau dangana Allah ya bani wanda ya fisa".
" 'Dan gidana meya faru naga ka ware kanka kai d'aya ina sauran suke"? 'Dagowa Asad yai zaiyi magana suma suka shigo da sallama duk gurin sa suka nufa suna zama sai aiko masa da harara suke musamman Ajeeb kamar idonsa zai fito waje ya kalli Alhussain yana cewa.
"Daddy kayi masa magana ya daina harara ta dan naga yau tsokana yake ji tun muna part dinmu yake zagina 🙊".
Murmushi Alhussain yai yana cewa "babyn Mami meyasa kake harararsa".
Asad na yiwa Ajeeb kallon mamakin sharrin daya 'kuga masa yace "ni ban zageshi ba shine kawai ina barci na ya zuba min ruwan fridge mai sanyi a jikina wai hakan bai ishe shiba saina gaidashi kamar wani ubana".
Kallon Ajeeb Alhussain yai yana cewa "to kaji meyasa zaka zuba masa ruwa"?.
"Daddy ya'ki tashi ne gashi rana ta fito baiyi sallah ba shine naji haushi na zuba masa".
"Ok to ka yarda bakai daidai ba ka bashi hakuri, meye abin d'aga hankali bayan kwanan nan zakuyi bankwana zai wuce Marshall islands ko duk fad'an karshen ne"? Ya karasa maganar da murmushi dan shiru Ajeeb yai sai kuma ya kalli Asad daya d'auke kai yace "kayi hakuri Bros" ya fad'a yana mi'ka masa hannu d'agowa Asad yai ya kalleshi dan kar yaje sha'kiyanci yake masa sai kuma yaga serious face dan haka shima ya mi'ko masa hannun sukai musahaba ya mi'kewa Ameer ma sannan yace "nima kayi hakuri" kai Ajeeb ya d'aga "ba komai ai mun saba indai rigima ce zuwa jimawa ma zamuyi wata jiki da jini kuma Asad nefa da Ajeeb" 'yar dariya yasa sauran sukai dan haka ne abinda Ajeeb d'in yace kullum suna cikin fad'a indai suna tare kamar Tom and Jerry 🤗 Alhussain yace "shikenan komai ya wuce Asad zai tafi tare da abokina abdul-kareem ranar Monday sai yayi shekara biyar zai dawo kuyi masa fatan alkairi da samun nasara" hannu Ajeeb ya bud'e yana cewa "a ro'ka da babban masaki nine mai karantowa" shiru kowa yai Ajeeb na zayyano addu'o'in nasara ga d'an uwansa saida ya gama kowa zai shafa yace "addu'ata ta 'karshe gareka Asad Allah ya baka mace jaruma mai ra'ayi irin naka amma banda fusata da son yin dambe da d'an uwa 🙉" Ajeeb na rufe baki khimiyyah da Makiyyah har had'a baki sukai kowacce na cewa "ai nice" kallon su Alhussain yai bayan sun shafa addu'ar yace "ai kune me"? Caraf khimiyyah tace "nice jarumar domin ina sonsa" zaro ido Makiyyah tai "kan bala'i kina sonsa a ina bayan na riga ki tun wuri kije ki nemi naki kafin lokaci ya'kure miki" a masife khimiyyah tace "wallh baki isa ba hauka ma kenan me kike nufi da na nemi nawa kar lokaci ya kure min? Humm Makiyyah kenan sorry yarinya wallahi Asad nawa ne gaba da baya gara kisan nayi" Makiyyah na shirin magana ganin shashancin da suke Alhussain ya d'aga musu hannu.
"Kai keep quite wanne irin shirme ne wannan kukeyi"? Khimiyyah na huci tace "Abba kana jinta abinda take cewa fa wallahi impossible na zuba miki ido yarinya wuce nan kinyi kad'an.............
Cikin tsawa Alhussain yace "zaki min shiru ko sai jikinki ya fad'a miki kada na sake jin irin wannan maganar a bakinku kowa ta ha'kura tunda ba dole bane dama ai kuna sonshi amma da yan uwantaka ba aureba karna sake jin haka dan gidana ba aure zaiyi ba aikinsa zaisa a gaba ku mayar da hankalin ku jikin ku yaushe kuka d'ago har kukasan miye duniya da abinda yake cikinta"?.
Fuskar khimiyyah ranta a 'bace take aikawa da Makiyyah mugun kallo tace "amma Abba.........,.......
"Ke ki rufe min baki nace tashi anan" mi'kewa Khimiyyah tai tana kumbura baki ta fice tana maganganu 'kasa 'kasa sauran ma mi'kewa sukai suna fita daga part din Makiyyah na shiga bedroom Khimiyyah ta sha'ko wuyanta tana cewa "ke har kin isa shiga tsakani na da muradi na wacece ke me kike ta'kama dashi"? Ri'ke hannun ta Makiyyah tai tana 'bam'barewa daga wuyanta tace "bakiyi karya ba Khimiyyah na isa ne tun farko inaji a jikina Asad nawa ne mijina ne shine mafarki na dan haka ta nuna Khimiyyah da yatsa taci gaba "kada ki kuskura ki koyi son wanda na gama mi'ka wuya sakankancewa da soyayyar ta idan ba haka ba kina tare da wahala".
Bige mata hannu Khimiyyah tai a fusace tace "hannu 'kasa yarinya kada ki sake gigin nuna min yatsa idan ba haka ba saina balla shi".
"Ke har kin isa kice zaki min wani abu"? Makiyyah ta tambaye ta itama zuciyarta na turiri.
'Kirji Khimiyyah ta buga "eh na isa harna wuce inda kike zato kuma kici gaba da shiga gonata wallahi wata rana za'ai babu ke dan saina 'badda ke".
Ta'be baki Makiyyah tai "humm gyara kalaman ki yan mata saidai mu 'badda juna tare dan baki isa na zuba miki ido ba nima ba kanwar lasa bace matukar kika fad'a min cuta ni kuma saina fad'a miki mutuwa😡😠".
Gajiya da shirmensa Shaukiyyah tai wani uban tsakin takaici taja tana cewa "wai dan Allah malamai maye haka ne kun ishemu da wannan wayon 'kauyen naku gaskiya ku barmu mu sarara ko kuma ku fita a bedroom d'in akan me muna zaune lafiya zaku hana mu jin dad'i gashi abinda haushin wanda kuke fad'an akansa baisan kunayi ba bai damu daku ba bakwa gaban sa na tabbata duk tsiya ko yana ra'ayin ku saidai ya auri d'aya kunsan bazei auri ku duka ba amma kuka tsaya kuna wahalar da kanku kun manta matar mutum kabarin sa maybe babu mai rabo a cikin ku saikun gama haukan ku yaje ya auro wata daga waje gashi kun girgiza junanku da fad'a da 'kiyayya meyasa ku bakwa tunani ne? Haba kamar wasu ma'kiyan juna gaskiya nake fad'a muku koda bai shafeni ba kuna abinda bai dace ba ku gyara ku mayar da hankali".
Wani banzan kallo duk su biyun suka watsa mata Khimiyyah tace "d'an maimaita abinda kikace banji sosai ba"?.
Had'e rai Shaukiyyah tai "bazan maimaita ba kada Allah yasa ki gane duk ranar da kika bud'e ido kikaga Asad da matarsa maybe ranar kyayi surrender ki gane kinyi kuskure".
"Ai wallahi Shaukiyyah babu ranar da zata zo wacce zanji wata nadama ta kamani har abada kuma zan iya yin komai dan cikar burina dan na samu abinda nake so kin gane? Dan haka bar 'bata bakinki a kaina ba fahimtarki zanyi ba".
Kai Shaukiyyah ta jinjina tana cewa "shikenan Allah yasa ki gane nikam shine fatana da ban nuna inason kowa ba a cikin su gashi na zauna lafiya sannan ban wahalar da zuciyata ba nasa mata rai akan abinda nasan bazata samu ba".
A banza Shaukiyyah take magana babu wanda ya fahimce ta a cikin su gani suke ba'kin ciki take musu ko dai akwai abinda take boyewa a ranta ita kuwa a zahirin gaskiya tana nuna musu abinda zai fishe su ne kar zuwa gaba wani mummunan abu ya faru wanda baza aji dad'i ba.
Khaldiyyah dake kwance da littafi a hannunta tana karatu batai musu magana ba tunda suka fara abinsu sai yanzu ta tashi zaune tana rufe littafin ta aje tare da kallon su har yanzu suna aikawa juna kallan kallo murmushi tai tana sake kai kallonta kan Shaukiyyah data d'auke kai daga saitinsu domin tayi iya yinta sun 'ki fahimtar ta kai ta girgiza tana cewa.
"Haba ku kuwa ladies👯 meye matsalar kune zaku li'kewa mutum daya? Ku bari na sasanta na raba muku fad'an inace mu hud'u ne kuma suma su hud'u ne? Ni a nawa ganin kawai kowa ta kama d'aya zaifi koba haka ba"?.
Kallonta Khimiyyah tai fuska ba rahma tace "me kike nufi su waye su hud'u"?.
Gyara zama Khaldiyyah tai "ina nufin mu hud'u suma su hud'u ne an raba kowa saita kama d'aya nikam dama na za'bi nawa tun tuni amma kunga da ban nuna ba ai na zauna lafiya lokaci nake jira wanda da kansa zai fahimta basai na furta masa ba domin neman kima da daraja a idonsa".
"Waye kike so a cikin su amma badai Asad ba"? Khimiyyah tai maganar tana kallon Khaldiyyah datai murmushi tace "a'a rufa min asiri ni kaza 🐔 abinci na dusa waneni Asad yafi 'karfina 😊 saidai manyan mata irinku" ta karasa maganar tana dariya.
'Kara had'e rai Khimiyyah tai "ai ba dogon bayani na nemi kimin ba cewa nai waye kike so a cikin su"?.
"Humm wannan kuma bai shafeki ba Khimiyyah dama an fad'a miki ni gariyace dazan fad'a miki wanda nake so wato kije ki fad'a masa batare dana bi a hankali ya soni ta sassaukar hanya ba ki ri'ke naki na ri'ke nawa".
Numfasawa Shaukiyyah tai tana cewa "nikam zan fad'i wanda nake so ba kuma bana jin shakkar a fad'a masa ban sani ba ko shima ya kamu da sona lokacin da banyi zato ba".
Dariya Khaldiyyah tai "ke wa kike so Allah yasa ba wanda nake so bane dan nima yanzu zamu hau sama mu fad'o".
Kafad'a Shaukiyyah ta d'aga tana cewa "to muhau man tunda yayin fad'an ake nikam wanda nake so "Ameer ne Allah yasa ke bashi bane"?.
Cikin tsokana Khaldiyyah tace "kika ce Ameer kike so? Kai Shaukiyyah ta d'aga Khaldiyyah taci gaba "innalillahi ai nima shine za'bin nawa"😲 zaro ido Shaukiyyah tai kamar zai fito waje tace "dan Allah da gaske kike Ameer kike so? Nashiga uku yanzu ya zanyi bazan iya fad'a dake ba koda hakan zai zama cutarwa ga rayuwata zan bar miki shi na dau dangana Allah ya bani wanda ya fisa".