Sashe 46
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Tunanin sane ya katse jin ta fasa ihu tana cewa "gasu nan sun shigo ka gansu nan da yawa idanuwan su yayi ja kallona suke wayyo Allah zasu kama ni zasu tafi dani" habawa a guje Ilyah yai tsalle ya shige bayan murfin kofar d'akin cike da tsoro daidai su Bara'atu sunzo ganin yadda Ramatu take 'barin kwanuka duk ta hargitsa d'akin yasa mamaki suma ya kamasu saidai da yake sun san rigimammiya ce zata aikata fiye da haka ma yasa suka tsaya kawai suna kallon ta sai susa take tana yagar gashin kanta ganin takalmin Ilyah a kofar d'aki yasa Bara'atu cewa.
"Kana ciki ne"?.
Jin anyi magana yasa Ilyah kallon Ramatu idanuwan ta sun sauya kala a tsorace ya sand'a zai fice yuuuu tayo kansa tana cewa "ina kuma zaka je bazaka tsaya muyi wasa ba zonan taho muyi rawa" ganin ta kawo masa rifka yasa yai wani irin ihu tare da dira tsalle sai gashi a waje da mugun 'karfi ya zuba a guje ya fad'a d'aki yana banko kofa kaiii suma aguje suka shige d'ayan d'akin yayin da Ramatu ta d'auki ta'barya tana dukan kofar kamar me karfin doki "dan uwarku bazaku bud'e min kofa ba matsiya wato dodo kuka mayar dani tsinannu wallahi gobe sai Ilyah ya sake ku sai kun bar gidan bankad'add'u 'ya'yan talakawa" dukan kofar take da karfi suna jinta kowa jiki na 'bari haka ta kwana tana abu daya har asuba sannan ta koma d'akinta ta sheme ta kama barci babu wanda ya iya fitowa a cikin su duk da sunji shiru an rasa me wannan jarumtar saida suka ji shirun har yayi yawa sannan suka bud'e kofa suna le'ke ganin dai bata nan yasa suka fito suna 'kwan'kwasawa Ilyah shiru yai yana jinsu yay kamar ya mutu🤣 saida sukai magana ya tabbatar sune sannan ya bud'e shima ya fito yana zazzara ido ya had'a gumi shir'bim sauke ajiyar zuciya yai yana kallon kofar d'akin ta yayi 'kasa da murya yana cewa "ina take"? suma kallon kofar d'akin sukai Maimuna tace "kila tana ciki" tura ta Ilyah yai "jeki gano😂" tirjewa Maimuna tai tana had'e rai tace "ba kaine namiji ba kaine ya kamata ka gano" shiru yai alamar bazai iya ba sai kuma ya kalli Bara'atu "ko ke zaki gano mana"🤣? Itama baya taja tana cewa "a'a wallahi bazan iya ba ni dama jinin mu bai had'u ba bari ma kagani sallah zanje nayi gashi har rana ta fito muna kulle kamar wanda mukai lefi" tana barin gurin itama Maimuna tabi bayanta dole tasa Ilyah tafiya a hankali yana d'auke sau yaje ta window ya le'ka ta tana kwance tana sharara bacci dur'kusawa yai ya dauki takalmi shima ya tafi sallah daga nan ya zarce gidan malam Zayyanu ya masa bayani tunda dama shine wakilin Baffah".
Balarabe ya auri Asabe ta tare abinta cike da murna dan tana sonshi sai zuba masa soyayya take irin ta 'yan bariki Dalah kam ta zama abar tausayawa gashi yanzu hatta Indo bai damu da ita sosai ba ada baya so yaji tayi kuka ko yaga hawayen ta amma yanzu ko zatai kukan jini yana ji bazai kula ba a yadda ake ciki ko mutuwa Indo zatai a yanzu kila bazai nuna damuwa ba yafi son agolarsa bahijjah yar gidan Asabe akan Indo yakan sayo mata komai jiki na rawa ya bata ya dauketa suje yawo amma banda Indo saidai tace ya mata haka a da😢.
Hummm duk nisan jifa zai dawo kasa inda jirgin sama yaje wata rana za'a cewa kunkuru barka da zuwa kuma duk nisan turin da za'ai wa lilo zaije ya dawo inda yake👌 Ramatu dai an haukace gara Salamatu dan ita yanzu inta faki ido ta fito sai bola kuma bakinta baya shiru tana fad'a-fad'e da zage zaga dama hali a jikin rai maganganu iri iri wanda ba'a san dasu ba sai fad'a take haka duk sunan mutumin daya zo bakinta a 'kauyen inta fara ambatonsa tana tsine masa tana 'kwal'kwale masa albarka saita wuni batai shiru ba kullum idan an rasa ta dama ansan inda za'a sameta saidai a tsinto ta kan bola tana ta tsintar ledodi tana daurewa a jikinta tana surutai kala kala wanda babu wanda yasan me take cewa wanne irin yare ne sudai yan 'kauyen basu ta'ba ji ba saifa a bakinta gajiya Ilyah yai ga kud'i yanzu yana ta bun'kasa amma jinya sai cinyewa take dan haka ya yanke shawara ya dauko wani malami cewa yazo ya ganta yana zuwa da fara aiki Ramatu tahau ihu iri iri da kururuwa yana yayyafa mata ruwan addu'a sai burgima take tana tsalle ta tumu a kasa timm ta tashi ta daki bango tai girgiza har katanga saida ta ture ta zube mutane kwa sun cika gidan kamar anyi busa sai gulma ake babu wanda ya ankara har malam kawai sai gani akai ta zuba da gudu tana yage yage a guje Ilyah da malam suka bi bayanta yan gari ma d'uuuu suka bisu aguje dan ganin 'kwa'kwaf daji Ramatu ta ri'ka linkuwa suna bita ga wata ba'kar iska me duhu data taso ta lullu'besu da guguwa a cikinta da 'kura duk 'kasa ta cika musu ido amma basu daina binta ba kwatsam sukaga kogi a gaban su ruwan har kumfa yake yana murd'ewa da ambaliya amma Ramatu takai take gudu kamar tana bin normal hanya tsayawa sukai suna haki ganin zata bace musu malam yace "ba ruwa bane sharrin miyagun makiya shed'anu ne muje cikin azama suka fara bi ta kan ruwa aiko sai sukaji kasa kawai suke takawa ashe rufa ido ne suna shiga wani ba'kin daji sukaga abu jimmmn ya fad'o gaban su wani shirgegen dodo jikinsa duk gashi ga jan ido turus mutane sukai wasu suka yanke jiki a gurin suka fad'i a sume wasu suka juya da aguje dariya dodan yai wanda tasa bishiyoyi ganyensu ya fara kad'ewa ya zuba muryarsa kamar saukar tsawa yace.
"Me kuke nema anan waccan tamu ce ku juya inda kuna son ranka Wanda kuma yake son muyi fate fatansa to yazo" malam na haki cike da gajiya yace "waye kai" hhhhhhhhhhh!!! Dariya ta hauka da tashin hankali dodon keyi yace "baka sanni ba kawai kalleni a haka saidai zaku wahalar da kanku domin ta zama tamu aiki tasa mukaiwa kishiyar ta har muka zu'ke mata jini ta mutu kuma dama mun fad'a mata aikin zai dawo kanta ta duk daran dad'ewa ta amince dan haka yanzu ido ne naku babu abinda ya isa ya 'kwaceta a wurin mu tayi bankwana kenan bazan hana ku binta ba ga hanya nan saidai zaku mutu hhhhhhhhhhh ku taho👻👹" yana fad'in haka ya 'bace addu'a malam yaci gaba tayi ba fashi da gudu suka sake yin dajin can suka hango Ramatu a wani wuri tana lilo abinda ya basu mamaki babu alamar igiya amma bala'in hillon da take ya 'baci addu'a malamin keyi yana nifar inda take yaje gaf da ita yaga wani ba'kin abu yazo ya shiga jikinta bai fasa ba ya sake matsawa wani irin tattarashi yeji anyi kafin ya ankara an li'kashi da kasa da sauri ya mike bai fasa addu'ar ba gashi gurin sai canza kala yake yana duhu kamar yanayin almuru Ramatu kuwa kamar wacce ake 'kara hilla ta can ta tsaya sai kuma ta dirgo ta sauka ta soma wata kalar tafiya kamar yar maye tana rangaji tayi gaba tayi baya ihuuuu ta zunduma tana rike kanta wanda malam yai amfani da wannan damar zai ri'ko ta aka daukeshi fiiiii kiffff aka watsa shi gefe har rawaninsa Saida ya fad'i yana yai yunkurin tashi da sauri yana sake nufota kafin ya karaso inda take sai gani sukai ta zama ba'ki 'kirim kamar ta 'kone bata da kyan gani daga haka ta zama 'bakin murtukekken haya'ki ta 'bace 'bat🙊😣 shikenan.
Haki malam keyi sosai yana innalillahi wa inna ilaihi raji'un mutane na amsa masa kowa jiki na bari malam yace "ya kamata mu barnan yanzu yanzu" aguje kowa ya ruga sai gware suke wadanda suka fad'i ana take su a haka suka samu da'kyar suka fita dajin suka koma gida da labarin abinda suka gani gari sai gulmar ake ana Allah wadai da halinta dama itace taiwa Salamatu asiri ya dawo kanta kowa da abinda zaice shikenan fa'kat masifa ta mutu Bara'atu ta huta ba wanda zai fadi abun alkairi a kanta sai na tsiya ga Ilyah bai nuna alamar zaiyi wani zaman makoki ba ko kadan kawai yadan zauna wunin ranar amma shikenan ya basar sai ranar sadakar uku.
"Kana ciki ne"?.
Jin anyi magana yasa Ilyah kallon Ramatu idanuwan ta sun sauya kala a tsorace ya sand'a zai fice yuuuu tayo kansa tana cewa "ina kuma zaka je bazaka tsaya muyi wasa ba zonan taho muyi rawa" ganin ta kawo masa rifka yasa yai wani irin ihu tare da dira tsalle sai gashi a waje da mugun 'karfi ya zuba a guje ya fad'a d'aki yana banko kofa kaiii suma aguje suka shige d'ayan d'akin yayin da Ramatu ta d'auki ta'barya tana dukan kofar kamar me karfin doki "dan uwarku bazaku bud'e min kofa ba matsiya wato dodo kuka mayar dani tsinannu wallahi gobe sai Ilyah ya sake ku sai kun bar gidan bankad'add'u 'ya'yan talakawa" dukan kofar take da karfi suna jinta kowa jiki na 'bari haka ta kwana tana abu daya har asuba sannan ta koma d'akinta ta sheme ta kama barci babu wanda ya iya fitowa a cikin su duk da sunji shiru an rasa me wannan jarumtar saida suka ji shirun har yayi yawa sannan suka bud'e kofa suna le'ke ganin dai bata nan yasa suka fito suna 'kwan'kwasawa Ilyah shiru yai yana jinsu yay kamar ya mutu🤣 saida sukai magana ya tabbatar sune sannan ya bud'e shima ya fito yana zazzara ido ya had'a gumi shir'bim sauke ajiyar zuciya yai yana kallon kofar d'akin ta yayi 'kasa da murya yana cewa "ina take"? suma kallon kofar d'akin sukai Maimuna tace "kila tana ciki" tura ta Ilyah yai "jeki gano😂" tirjewa Maimuna tai tana had'e rai tace "ba kaine namiji ba kaine ya kamata ka gano" shiru yai alamar bazai iya ba sai kuma ya kalli Bara'atu "ko ke zaki gano mana"🤣? Itama baya taja tana cewa "a'a wallahi bazan iya ba ni dama jinin mu bai had'u ba bari ma kagani sallah zanje nayi gashi har rana ta fito muna kulle kamar wanda mukai lefi" tana barin gurin itama Maimuna tabi bayanta dole tasa Ilyah tafiya a hankali yana d'auke sau yaje ta window ya le'ka ta tana kwance tana sharara bacci dur'kusawa yai ya dauki takalmi shima ya tafi sallah daga nan ya zarce gidan malam Zayyanu ya masa bayani tunda dama shine wakilin Baffah".
Balarabe ya auri Asabe ta tare abinta cike da murna dan tana sonshi sai zuba masa soyayya take irin ta 'yan bariki Dalah kam ta zama abar tausayawa gashi yanzu hatta Indo bai damu da ita sosai ba ada baya so yaji tayi kuka ko yaga hawayen ta amma yanzu ko zatai kukan jini yana ji bazai kula ba a yadda ake ciki ko mutuwa Indo zatai a yanzu kila bazai nuna damuwa ba yafi son agolarsa bahijjah yar gidan Asabe akan Indo yakan sayo mata komai jiki na rawa ya bata ya dauketa suje yawo amma banda Indo saidai tace ya mata haka a da😢.
Hummm duk nisan jifa zai dawo kasa inda jirgin sama yaje wata rana za'a cewa kunkuru barka da zuwa kuma duk nisan turin da za'ai wa lilo zaije ya dawo inda yake👌 Ramatu dai an haukace gara Salamatu dan ita yanzu inta faki ido ta fito sai bola kuma bakinta baya shiru tana fad'a-fad'e da zage zaga dama hali a jikin rai maganganu iri iri wanda ba'a san dasu ba sai fad'a take haka duk sunan mutumin daya zo bakinta a 'kauyen inta fara ambatonsa tana tsine masa tana 'kwal'kwale masa albarka saita wuni batai shiru ba kullum idan an rasa ta dama ansan inda za'a sameta saidai a tsinto ta kan bola tana ta tsintar ledodi tana daurewa a jikinta tana surutai kala kala wanda babu wanda yasan me take cewa wanne irin yare ne sudai yan 'kauyen basu ta'ba ji ba saifa a bakinta gajiya Ilyah yai ga kud'i yanzu yana ta bun'kasa amma jinya sai cinyewa take dan haka ya yanke shawara ya dauko wani malami cewa yazo ya ganta yana zuwa da fara aiki Ramatu tahau ihu iri iri da kururuwa yana yayyafa mata ruwan addu'a sai burgima take tana tsalle ta tumu a kasa timm ta tashi ta daki bango tai girgiza har katanga saida ta ture ta zube mutane kwa sun cika gidan kamar anyi busa sai gulma ake babu wanda ya ankara har malam kawai sai gani akai ta zuba da gudu tana yage yage a guje Ilyah da malam suka bi bayanta yan gari ma d'uuuu suka bisu aguje dan ganin 'kwa'kwaf daji Ramatu ta ri'ka linkuwa suna bita ga wata ba'kar iska me duhu data taso ta lullu'besu da guguwa a cikinta da 'kura duk 'kasa ta cika musu ido amma basu daina binta ba kwatsam sukaga kogi a gaban su ruwan har kumfa yake yana murd'ewa da ambaliya amma Ramatu takai take gudu kamar tana bin normal hanya tsayawa sukai suna haki ganin zata bace musu malam yace "ba ruwa bane sharrin miyagun makiya shed'anu ne muje cikin azama suka fara bi ta kan ruwa aiko sai sukaji kasa kawai suke takawa ashe rufa ido ne suna shiga wani ba'kin daji sukaga abu jimmmn ya fad'o gaban su wani shirgegen dodo jikinsa duk gashi ga jan ido turus mutane sukai wasu suka yanke jiki a gurin suka fad'i a sume wasu suka juya da aguje dariya dodan yai wanda tasa bishiyoyi ganyensu ya fara kad'ewa ya zuba muryarsa kamar saukar tsawa yace.
"Me kuke nema anan waccan tamu ce ku juya inda kuna son ranka Wanda kuma yake son muyi fate fatansa to yazo" malam na haki cike da gajiya yace "waye kai" hhhhhhhhhhh!!! Dariya ta hauka da tashin hankali dodon keyi yace "baka sanni ba kawai kalleni a haka saidai zaku wahalar da kanku domin ta zama tamu aiki tasa mukaiwa kishiyar ta har muka zu'ke mata jini ta mutu kuma dama mun fad'a mata aikin zai dawo kanta ta duk daran dad'ewa ta amince dan haka yanzu ido ne naku babu abinda ya isa ya 'kwaceta a wurin mu tayi bankwana kenan bazan hana ku binta ba ga hanya nan saidai zaku mutu hhhhhhhhhhh ku taho👻👹" yana fad'in haka ya 'bace addu'a malam yaci gaba tayi ba fashi da gudu suka sake yin dajin can suka hango Ramatu a wani wuri tana lilo abinda ya basu mamaki babu alamar igiya amma bala'in hillon da take ya 'baci addu'a malamin keyi yana nifar inda take yaje gaf da ita yaga wani ba'kin abu yazo ya shiga jikinta bai fasa ba ya sake matsawa wani irin tattarashi yeji anyi kafin ya ankara an li'kashi da kasa da sauri ya mike bai fasa addu'ar ba gashi gurin sai canza kala yake yana duhu kamar yanayin almuru Ramatu kuwa kamar wacce ake 'kara hilla ta can ta tsaya sai kuma ta dirgo ta sauka ta soma wata kalar tafiya kamar yar maye tana rangaji tayi gaba tayi baya ihuuuu ta zunduma tana rike kanta wanda malam yai amfani da wannan damar zai ri'ko ta aka daukeshi fiiiii kiffff aka watsa shi gefe har rawaninsa Saida ya fad'i yana yai yunkurin tashi da sauri yana sake nufota kafin ya karaso inda take sai gani sukai ta zama ba'ki 'kirim kamar ta 'kone bata da kyan gani daga haka ta zama 'bakin murtukekken haya'ki ta 'bace 'bat🙊😣 shikenan.
Haki malam keyi sosai yana innalillahi wa inna ilaihi raji'un mutane na amsa masa kowa jiki na bari malam yace "ya kamata mu barnan yanzu yanzu" aguje kowa ya ruga sai gware suke wadanda suka fad'i ana take su a haka suka samu da'kyar suka fita dajin suka koma gida da labarin abinda suka gani gari sai gulmar ake ana Allah wadai da halinta dama itace taiwa Salamatu asiri ya dawo kanta kowa da abinda zaice shikenan fa'kat masifa ta mutu Bara'atu ta huta ba wanda zai fadi abun alkairi a kanta sai na tsiya ga Ilyah bai nuna alamar zaiyi wani zaman makoki ba ko kadan kawai yadan zauna wunin ranar amma shikenan ya basar sai ranar sadakar uku.