Sashe 82
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Majalisa kowa da kowa ana zaune Malam ya karaso da sallama a bakinsa yana samun guri ya zauna suna gaisawa da jama'ar da aka jima ba'a had'u ba ko numfashin tafiyar dayai bai gama tsirga masa ba Tanko dake kallonsa yana 'kunshe dariyar mugunta ganin har lokacin da sauran ta'bo a jikinsa ya kalleshi cike da sha'kiyanci yace "a'a alhaji Malam Habubakar mai ruwan nairori kaga d'an Baffah na Sabi'u d'an uwan Ilyah attajirin 'yan 'kauyen nan me nake gani haka meke faruwa ne wato a kwana a tashi babu sallama ba d'aga hannu sai ji muke wai kun tashi kun tafi neman kud'i kaida Sadi batare da kun sanar mana ba saboda bakin hali Dan karmu biku sai gashi dubunku ta cika a hanyar dawowa 'yan fashi sun tareku sun muku tsinannan duka sun 'kwace komai kila dama kayan da kuka taho da shi da kud'in ba halal d'inku bane wayasani ko sata dama kuke da kukaje shiyasa alhakin mutane yasa aka tareku aka kar'be dukiyar da za'a zo a mana tunkaho ana bubbud'a mana kafad'u ana hura hanci hhhhhhhhhhh mudi kaji da Allah".
Ya karasa maganar yana she'kawa da dariya had'e rai malam Habu yai cike da takaicin maganar da Tankon ya fad'a masa ransa a'bace yana shirin mayar da martani Sadi yace.
"Dan Allah dan Annabi badan niba malam Habu kada ka tanka musu idan kaddara ce bata wuce kan kowanne bawa ba Dama tun farko a rubuce take abinda muka tara bazai zo 'kauyen nan ba badan haka ba wallahi kudai👉 ya fad'a yana nunasu da yatsa yaci gaba da cewa "da saidai ku zamo 'yan kallo hum bakuba hatta Ilyah da yakejin duk garin nan shine mai tashen kud'i yafi kowa arziki wallahi koshi baida bakin magana da ace dukiyan da muka tara tazo garin nan kuma insha Allahu zamu sake komawa nan ba da jimawa ba zakuga irin alherin da zamuzo dashi saikun kasa furta komai kuma Nina fad'a muku wata rana zakuyi dana sanin wannan abinda kukeyi".
Baki bud'e Tanko, da Mudi suke kallon juna kafin suka sakar masa wata uwar harara Mudi yace "tofa sannu d'an iya ikon Allah Sadi yau kaine har kasamu damar furta wata magana wato zama da malam Habu ko ya koya maka ya'ba magana? Hum aiko kanada aiki babba a gabanka garama tun farko kaja gefe kamar yadda sauran sukai idan kuma ka'ki zakai bayani".
Mudi yana rufe baki Tanko yace "fad'a masa dai dan Naga shima yanada masifar shishshigi, Sadi babu ruwanka anan da Malam Habu mukeyi badakai ba karamin alhaki ka gane"?.
Kai Sadi ya jinjina "ai Tanko indai kunyi da Malam Habu tamkar kunyi da dani ne".
Wani irin kallo Tanko yai masa yana cewa "au haba? Ko shiyasa ka gayyaceshi kuka tafi bara har wata kasar kuka 'bige da sata kuma kukai rashin sa'a da yake ba dukiyarku ce ta halal ba a hanyar dawowa kukaci na jaki a gurin 'yan fashi"?.
Kafin Sadi yai magana suka ji muryar Malam Habu yace "uban waye ya fad'a maka sata muka je"?.
Gyara zama Tanko yai yana sake fuskantar malam Habu sosai cikin son 'kular dashi yace "Wa kake tunanin zai fad'a min dawa kukaje garin waye ya gayyaceka ba Sadi bane? To shine munje yo masa bangajiya washe garin da kuka dawo anan muka bugi cikinsa ya fad'a mana komai da kuke acan" Tanko ya karasa maganar yana kallon yadda Sadi ya zaro ido waje cike da mamakin sharrin dayai masa danshi idan ba yauba tunda suka dawo baiga Tanko ba kallon malam Habu yai yaga a yanayin yadda zai dau maganar da Tankon ya fad'a masa yana cewa.
"Wallahi sharri yai min Habubakar bansan komai ba ni tunda muka dawo ban ta'ba ganinsa ba sai yau Amma kaji tsabar 'karya danya had'amu harda wai sunje min ban gajiya a ina"? Ya fad'a yana hararar Tanko dake murmushi.
Caraf Mudi yace "ka tuna mana munje gurin ka washe garin da kuka dawo kodai sannan rad'ad'in ciwo bai sakeka ba baka gane su wayeba shiyasa ka saki baki ya layar uban tafiya ka fad'a mana sirrin ku"?.
Dafe kai Sadi yai jin zasu sashi a uku yace "Allah ya tsinewa mai 'karya indai abinda kuka fad'a a kaina haka yake gaskiya ne Allah ya tagayyara mai 'karya Allah yai d'ai d'ai dashi🙊".
Shiru su Tanko sukai yayin da Jama'ar gurin suka fara cewa Amin Amin kallon malam Habu yai yana cewa "wallahi Habubakar ba gaskiya bane abinda suka fad'a basuje gurina ba kuma ni bamu had'u dasu na fada musu komai ba ko a mafarki".
Ta'be baki Malam Habu yai yana mi'kewa ya kalleshi yana cewa "karka damu Sadi ba yauba na sanka koda kowa zaici amanata Banda kai sharesu kawai taso mu tafi idan isgili suke mana wanda ya jarrabe mu yana jinsu kuma babu wanda ya isa tsallake 'kaddararsa sannan garani iyalaina suna Sona suna alfahari dani sun fahimce ni basa guduna duk irin halin Dana shiga amma wani fa ba iya gidansa ko anguwarsa ba hatta dukkan mutanen gari tsine masa suke suna Allah wadai da tofin alatsine akansa saboda ya wadata kansa ya hana ahlinsa ga rashin yafiyar iyaye wai wanda yake da wannan ta'bon ne har ya samu bakin magana tsabar rashin hankali dayake shi laifi tudu ne ya take nasa ya hango na wani"? Malam Habu ya fad'a yana kallon Tanko dake dafe da kirji yace.
"Ko nayi 'karya ne Tanko"?.
Mi'kewa Tanko yai yana cewa "kaga malam Habu ka daina yi dani eh ban wadata iyalan nawa ba kai me zai hana ka d'ebo dukiyar gidanka ka wadata su sannan zansan ka damu dasu har haka in kuma zaka debesu ka had'a danaka ka ri'ke kofa a bud'e take nayi maka izini kaje ka d'iba na bar makasu duka mutum yana fama da ba'kin talauci yana sawa wani ido ban kula da iyalan nawaba da zama irin na gidanka cikin yunwa ba gara mutum ya mutu babu aure ba kaima me kake baiwa iyalan naka har zaka damu Dana wani kayi ta kanka"..
Kai Malam Habu ya d'aga yana kallon Tanko yace "kuma fa kaima kayi gaskiya da zama irin na gidanka gara mutum ya zauna babu aure na yarda da wannan shiyasa na'ki yin auren tsabar asaranci na zauna tuzuru sai iya kwartanci da 'kananan yara a guna Ina basu kud'i saboda jahilci gaskiya ne Tanko kayi magana anan da irin wannan mutumin gara kai da baka wadata iyalan naka".
Dariya guri ya rud'e kowa yana kallon Mudi Dan kaf gurin sunsan dashi malam Habu yake waye wanda ya'ki aure inba shiba kuma kullum 'yan iskan 'yan Mata daga wasu 'kauyukan suna zuwa masa ansha ganinsu Dan haka bashi da bakin magana balle ya musa kowa cewa yake "Allah dai ya biya Malam Habu gaskiya kana sanya mu nishad'i" Mudi kam sak yayi jikinsa yai la'asar kamar an jefa akuya a ruwan sanyi ransa na turiri gashi yana tsoron yai magana kada Malam Habun ya sake gasa masa wata maganar da zaizo yai dana sani yana kallo malam Habu da Sadi suka bar gurin mutane sai cagwada suke masa amma Saboda yasan halinsa ne tari dabai kamashi ba baiyi ba.
🌃 MARSHALL ISLANDS🌃
Asad yana zaune tare da Isham yana fad'a masa cewa akwai wanda ya gano 'kungiyar kuma mace ce saidai bai santa ba baisan a inda take ba ko 'yar waye Isham ya matukar kad'uwa kuma ya karaya dajin batun yana ganin kamar tunda haka ta faru shikenan Asad yayi losing komai kamar yadda shima Asad d'in a nasa 'bangaren yake jin hakan kallonsa Isham yai yana cewa.
"What do you do now bayan daka gano an samu wacce ta sani a ina take"?.
Kai Asad ya girgiza yana kallon laptop yace "I don't know Isham".
A damuwance Isham yace "amma Buddy mai zai hana kad'au hutu koda na wata d'aya ne ka zauna guri d'aya ka samu nutsuwa kayi bincike a hankali saikafi fahimtar komai".
'Dagowa Asad yai yana kallon sa jin abinda yace cikin nazari kuma yaga kamar hakan shine daidai ya kar'bi hutun ya tsaya guri guda ya samu yayi bincike akan koma wacece kuma dama yana son zuwa gida gurin Abba (mai martaba) daga nan saiya tsaya ya bincika sosai acan d'in ma zaifi samun nutsuwa fiye danan babu takurar Kiran wayar Clarah da damunsa akai akai.....
Muryar Isham ce ta katse shi "Buddy tunanin me kake ko shawaran dana baka batai ba"?.
Kai Asad ya girgiza "no tayi zuwa gobe zanje nayi magana da sir murtih Jonah Ina so zamu had'u da sir Jalalunddeen kafin na tafi domin wannan al'amarin babba ne inaso na tambaye shi ko akwai wanda yazo cikin jami'an mu yace an samu wanda ya gano abinda ake nema Kuma wai mace? Mace dai"? Asad ya karasa maganar da surprise sosai a fuskarsa wanda yasa Isham ya saki dariya yana cewa..
"Oh Asad kaifa yanzu baka shiri da mace tun daga abinda sister d'inka tai maka mine a ciki idan macen ce ka nemeta ka bincike ta ka samu abinda kake so shine magana aiba duka suka taru suka zama d'aya ba akwai matan da zasu saka kayi sanyi Asad".
Isham ya karasa maganar yana kallon yanayin da Asad zai shiga akan abinda yace aiko da qarfi Asad ya d'ago har yana zaro ido waje yace "me kace Isham mace tasa nayi sanyi amma dai ba mace wacce na sani ba"😠?.
'Dan murmushi Isham yai dan tsaf ya gano Asad son bijirewa maganar daya fad'a yakeyi yace "eh Asad mace dai wacce ka sani ba abinda mamaki bane kasan miyasa nace haka? Saboda macen suna ne amma kada kayi musu kud'in goro kowacce halinta daban akwai na musamman a cikinsu".
"Amma irinsu Mami kake fad'a ko? Ina nufin uwaye"?😛.
Dariya Isham yai "a'a ina nufin irin 'yan Mata nake fad'a maka kagane kamar.......
Katse shi Asad yai da cewa "eh na gane abar maganar haka muje inason zamuyi magana dasu a yau Isham gobe nake son tafiya gida".
Cike da tsokana Isham yace "kai Asad da wuri haka aina d'auka sai kamar zuwa qarshen watan nan ko"?.
Ya karasa maganar yana she'kawa da dariya had'e rai malam Habu yai cike da takaicin maganar da Tankon ya fad'a masa ransa a'bace yana shirin mayar da martani Sadi yace.
"Dan Allah dan Annabi badan niba malam Habu kada ka tanka musu idan kaddara ce bata wuce kan kowanne bawa ba Dama tun farko a rubuce take abinda muka tara bazai zo 'kauyen nan ba badan haka ba wallahi kudai👉 ya fad'a yana nunasu da yatsa yaci gaba da cewa "da saidai ku zamo 'yan kallo hum bakuba hatta Ilyah da yakejin duk garin nan shine mai tashen kud'i yafi kowa arziki wallahi koshi baida bakin magana da ace dukiyan da muka tara tazo garin nan kuma insha Allahu zamu sake komawa nan ba da jimawa ba zakuga irin alherin da zamuzo dashi saikun kasa furta komai kuma Nina fad'a muku wata rana zakuyi dana sanin wannan abinda kukeyi".
Baki bud'e Tanko, da Mudi suke kallon juna kafin suka sakar masa wata uwar harara Mudi yace "tofa sannu d'an iya ikon Allah Sadi yau kaine har kasamu damar furta wata magana wato zama da malam Habu ko ya koya maka ya'ba magana? Hum aiko kanada aiki babba a gabanka garama tun farko kaja gefe kamar yadda sauran sukai idan kuma ka'ki zakai bayani".
Mudi yana rufe baki Tanko yace "fad'a masa dai dan Naga shima yanada masifar shishshigi, Sadi babu ruwanka anan da Malam Habu mukeyi badakai ba karamin alhaki ka gane"?.
Kai Sadi ya jinjina "ai Tanko indai kunyi da Malam Habu tamkar kunyi da dani ne".
Wani irin kallo Tanko yai masa yana cewa "au haba? Ko shiyasa ka gayyaceshi kuka tafi bara har wata kasar kuka 'bige da sata kuma kukai rashin sa'a da yake ba dukiyarku ce ta halal ba a hanyar dawowa kukaci na jaki a gurin 'yan fashi"?.
Kafin Sadi yai magana suka ji muryar Malam Habu yace "uban waye ya fad'a maka sata muka je"?.
Gyara zama Tanko yai yana sake fuskantar malam Habu sosai cikin son 'kular dashi yace "Wa kake tunanin zai fad'a min dawa kukaje garin waye ya gayyaceka ba Sadi bane? To shine munje yo masa bangajiya washe garin da kuka dawo anan muka bugi cikinsa ya fad'a mana komai da kuke acan" Tanko ya karasa maganar yana kallon yadda Sadi ya zaro ido waje cike da mamakin sharrin dayai masa danshi idan ba yauba tunda suka dawo baiga Tanko ba kallon malam Habu yai yaga a yanayin yadda zai dau maganar da Tankon ya fad'a masa yana cewa.
"Wallahi sharri yai min Habubakar bansan komai ba ni tunda muka dawo ban ta'ba ganinsa ba sai yau Amma kaji tsabar 'karya danya had'amu harda wai sunje min ban gajiya a ina"? Ya fad'a yana hararar Tanko dake murmushi.
Caraf Mudi yace "ka tuna mana munje gurin ka washe garin da kuka dawo kodai sannan rad'ad'in ciwo bai sakeka ba baka gane su wayeba shiyasa ka saki baki ya layar uban tafiya ka fad'a mana sirrin ku"?.
Dafe kai Sadi yai jin zasu sashi a uku yace "Allah ya tsinewa mai 'karya indai abinda kuka fad'a a kaina haka yake gaskiya ne Allah ya tagayyara mai 'karya Allah yai d'ai d'ai dashi🙊".
Shiru su Tanko sukai yayin da Jama'ar gurin suka fara cewa Amin Amin kallon malam Habu yai yana cewa "wallahi Habubakar ba gaskiya bane abinda suka fad'a basuje gurina ba kuma ni bamu had'u dasu na fada musu komai ba ko a mafarki".
Ta'be baki Malam Habu yai yana mi'kewa ya kalleshi yana cewa "karka damu Sadi ba yauba na sanka koda kowa zaici amanata Banda kai sharesu kawai taso mu tafi idan isgili suke mana wanda ya jarrabe mu yana jinsu kuma babu wanda ya isa tsallake 'kaddararsa sannan garani iyalaina suna Sona suna alfahari dani sun fahimce ni basa guduna duk irin halin Dana shiga amma wani fa ba iya gidansa ko anguwarsa ba hatta dukkan mutanen gari tsine masa suke suna Allah wadai da tofin alatsine akansa saboda ya wadata kansa ya hana ahlinsa ga rashin yafiyar iyaye wai wanda yake da wannan ta'bon ne har ya samu bakin magana tsabar rashin hankali dayake shi laifi tudu ne ya take nasa ya hango na wani"? Malam Habu ya fad'a yana kallon Tanko dake dafe da kirji yace.
"Ko nayi 'karya ne Tanko"?.
Mi'kewa Tanko yai yana cewa "kaga malam Habu ka daina yi dani eh ban wadata iyalan nawa ba kai me zai hana ka d'ebo dukiyar gidanka ka wadata su sannan zansan ka damu dasu har haka in kuma zaka debesu ka had'a danaka ka ri'ke kofa a bud'e take nayi maka izini kaje ka d'iba na bar makasu duka mutum yana fama da ba'kin talauci yana sawa wani ido ban kula da iyalan nawaba da zama irin na gidanka cikin yunwa ba gara mutum ya mutu babu aure ba kaima me kake baiwa iyalan naka har zaka damu Dana wani kayi ta kanka"..
Kai Malam Habu ya d'aga yana kallon Tanko yace "kuma fa kaima kayi gaskiya da zama irin na gidanka gara mutum ya zauna babu aure na yarda da wannan shiyasa na'ki yin auren tsabar asaranci na zauna tuzuru sai iya kwartanci da 'kananan yara a guna Ina basu kud'i saboda jahilci gaskiya ne Tanko kayi magana anan da irin wannan mutumin gara kai da baka wadata iyalan naka".
Dariya guri ya rud'e kowa yana kallon Mudi Dan kaf gurin sunsan dashi malam Habu yake waye wanda ya'ki aure inba shiba kuma kullum 'yan iskan 'yan Mata daga wasu 'kauyukan suna zuwa masa ansha ganinsu Dan haka bashi da bakin magana balle ya musa kowa cewa yake "Allah dai ya biya Malam Habu gaskiya kana sanya mu nishad'i" Mudi kam sak yayi jikinsa yai la'asar kamar an jefa akuya a ruwan sanyi ransa na turiri gashi yana tsoron yai magana kada Malam Habun ya sake gasa masa wata maganar da zaizo yai dana sani yana kallo malam Habu da Sadi suka bar gurin mutane sai cagwada suke masa amma Saboda yasan halinsa ne tari dabai kamashi ba baiyi ba.
🌃 MARSHALL ISLANDS🌃
Asad yana zaune tare da Isham yana fad'a masa cewa akwai wanda ya gano 'kungiyar kuma mace ce saidai bai santa ba baisan a inda take ba ko 'yar waye Isham ya matukar kad'uwa kuma ya karaya dajin batun yana ganin kamar tunda haka ta faru shikenan Asad yayi losing komai kamar yadda shima Asad d'in a nasa 'bangaren yake jin hakan kallonsa Isham yai yana cewa.
"What do you do now bayan daka gano an samu wacce ta sani a ina take"?.
Kai Asad ya girgiza yana kallon laptop yace "I don't know Isham".
A damuwance Isham yace "amma Buddy mai zai hana kad'au hutu koda na wata d'aya ne ka zauna guri d'aya ka samu nutsuwa kayi bincike a hankali saikafi fahimtar komai".
'Dagowa Asad yai yana kallon sa jin abinda yace cikin nazari kuma yaga kamar hakan shine daidai ya kar'bi hutun ya tsaya guri guda ya samu yayi bincike akan koma wacece kuma dama yana son zuwa gida gurin Abba (mai martaba) daga nan saiya tsaya ya bincika sosai acan d'in ma zaifi samun nutsuwa fiye danan babu takurar Kiran wayar Clarah da damunsa akai akai.....
Muryar Isham ce ta katse shi "Buddy tunanin me kake ko shawaran dana baka batai ba"?.
Kai Asad ya girgiza "no tayi zuwa gobe zanje nayi magana da sir murtih Jonah Ina so zamu had'u da sir Jalalunddeen kafin na tafi domin wannan al'amarin babba ne inaso na tambaye shi ko akwai wanda yazo cikin jami'an mu yace an samu wanda ya gano abinda ake nema Kuma wai mace? Mace dai"? Asad ya karasa maganar da surprise sosai a fuskarsa wanda yasa Isham ya saki dariya yana cewa..
"Oh Asad kaifa yanzu baka shiri da mace tun daga abinda sister d'inka tai maka mine a ciki idan macen ce ka nemeta ka bincike ta ka samu abinda kake so shine magana aiba duka suka taru suka zama d'aya ba akwai matan da zasu saka kayi sanyi Asad".
Isham ya karasa maganar yana kallon yanayin da Asad zai shiga akan abinda yace aiko da qarfi Asad ya d'ago har yana zaro ido waje yace "me kace Isham mace tasa nayi sanyi amma dai ba mace wacce na sani ba"😠?.
'Dan murmushi Isham yai dan tsaf ya gano Asad son bijirewa maganar daya fad'a yakeyi yace "eh Asad mace dai wacce ka sani ba abinda mamaki bane kasan miyasa nace haka? Saboda macen suna ne amma kada kayi musu kud'in goro kowacce halinta daban akwai na musamman a cikinsu".
"Amma irinsu Mami kake fad'a ko? Ina nufin uwaye"?😛.
Dariya Isham yai "a'a ina nufin irin 'yan Mata nake fad'a maka kagane kamar.......
Katse shi Asad yai da cewa "eh na gane abar maganar haka muje inason zamuyi magana dasu a yau Isham gobe nake son tafiya gida".
Cike da tsokana Isham yace "kai Asad da wuri haka aina d'auka sai kamar zuwa qarshen watan nan ko"?.