← Book details Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 145

Sashe 30

Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

MRS AL'AMEEN AHMAD CE 😘 MAI TAMBARIN YMA DUTSE 🏞️🏔️ JIGAWA STATE.

TYPING 📲 SAT, MAR 23/24 Yusrah Musa Abubakar 💞🌹 maman little Zaran aunty.

💫 ANNURI WRITER'S ASS💫 HOME OF HOSPITALITY AND HARMONY GIDAN KARBAR MUTANE HANNU BIYU 🌹🥀 DA ZAMAN LAFIYA ANNURI HASKE LEKA GIDAN KOWA KODA MAKIYA NA KALLON KA RAMIN KURA SAI 'YA'YAN TA KIRARIN MU KENAN.

Ya mai nasiha ga alumma muso juna mu rike gaskiya amana dan gudun kuna mu raya zuminci hanya ne na aljannah makiyin zumunci baya kusanci ceto ba ga wassu baitukan soyayya maula na daga masoyiyar ka Yusrah ta dumus yar Musa.
_______________________
Allahu dan isar bawan nan da ka Aiko shine Muhammad rasulullah daya sauko me sansa ka fad'i ba shakka zai karko albarcinsa bani basira me fad'i ka bani hikkimar sarrafa waka alhadi idan nayita bata ga buri aji dad'i a kara kankame soyayyar manzo na.

💋YUSRAH MS ABUBAKAR MUHAMMAD💋.

23~AR-RAFI'U
The exalter
24~AL-MU'IZZ
The giver of honour

12~Allahumma salli wa sallim ala sayyidina muhammadin sayyidil Khaidinah.

🌄THREAT ND TREASON🌄
Episode 23 nd 24
Bayan kwana biyar da faruwar haka Tanko ya dawo daga d'an yawon shashancin daya je ko hutawa baiyi ba Mudi ya munafirta masa cewa Lami fa ta dawo ya kamata suje su lallameta kafin wannan d'an birnin ya biyota idan sukai sa'a ta amince zata aure shi yarda yai da shawarar Mudi yace gobe zasuje.

Washe gari da magriba suka je kofar gidan Baffah suka sa aka yiyo musu magana da Lami tayi mamakin ganin Tanko har mamakin nata ya'ki boyuwa ranta a'bace tuna wulakancin dayai mata a dandali kwanan baya tace "meye ya kawo ka Tanko ko 'batan kai kayi tun wuri ka saitawa kan ka hanya".

Tanko na shirin yin magana Mudi yai gyaran murya yana cewa "haba Lami kamar baki le'ka birni ba zaki mana wulakanci sannan baki tsaya kinji abinda zan fad'a miki ba kawai kika yanke hukunci".

A fusace Lami tace "baka da wani abu da zaka fad'a min wanda zaisa na saurari Tanko kamar yadda ya tozarta ni a gaban kowa nima tun daga ranar na zubar dashi a rayuwa dan haka ka barni dan Allah naje nayi rayuwa ta".

Zata juya Tanko ya katse ta "haba Lami ki tsaya ki fahimce ni muyi maganar gaskiya nasan na aikata miki kuskure banyi dadai amma kiyi hakuri kinsan ina son ki".

"Na sani kuma na gode da soyayyarka gare ni saidai ka sani ka makara domin na riga na hakura dakai Tanko dan haka ka kyale ni nayi rayuwa ta".

"Bazan rabu dake ba Lami har sai kince zaki aure ni kin rabu da wancan shashashan tsigalallan birni".

"Kada ka sake zagin sa".

A hasale Tanko yace "na sake shi dambun uban sa wato kinje ya zuzzuga ki shine zaki min rashin mutunci" "ba rashin mutunci nayi maka ba Tanko kawai na nuna maka gaskiya ne kayi hakuri bazan iya aurenka ba na riga na hakura dakai dan Allah ka fahimta ka rabu dani".

Kai Tanko ya jinjina "shikenan na barki har abada kuwa jeki abinki" yana rufe baki Lami ta fad'a gida da sauri kai Tanko ya jinjina yana jan tsaki yace "lallai yarinyar nan ta kira ruwa saina gwada mata rashin imani na dan ko yayanta Ilyah bai isa jada niba balle ita" cikin zuga Mudi yace "to ai mutumi na kaine kayi sake taya zaka bari yar wannan yarinyar ta ri'ka kallon cikin idonka tana zazzaga maka rashin mutunci baka falleta da mari ba wanda saita ga wuta ba wallahi kada ka hakura ka dau fansar wannan abun da tayi maka" "fad'a batawa Mudi ai dole na sanyata bakin ciki kamar yadda ta sanya ni dole na rama cin fuskar da tai min kuma ta hanyar da kowa bazai ji dad'i ba muje kawai Mudi yau saina kora sosai kaina yadau zafi" wucewa sukai Mudi na sake zugashi da bashi shawarar yadda zaiyi.

Zaman Lami haka babu islamiya yana damunta tana son shiga tana tsoron masifar Ramatu ta kasa fad'awa Baffah gashi tun ranar da aka kawo ro'kon arzikin ta Ramatu ta sake bud'e mata wutar talla kamar jaka wai saita tara kud'in da zata sai mata kayan d'aki Baffah yayi fad'an har ya gaji ya 'kyale.

Lami na zaune a kofar d'aki tayi tagumi Baffah daya shigo cikin rashin jin dad'in ganin ta a haka yace "Lami lafiya meya faru"? Hawaye ne ya zubo mata tana kallon shi tace "dan Allah Baffah na rokeka ka sani a makaranta ko ta islamiya ce nima nayi karatu" sauke ajiyar zuciya yai yana rike hannunta yace "karki damu kinji share hawayen ki insha Allahu gobe da kaina zan raka ki har islamiya gurin malam Haruna yasa sunan ki cikin d'alibai ki fara zuwa daga baya saina dinka miki inifon tunda kinga Alpha din yace a 'kara masa lokaci bai 'karasa gini ba saiki fara islamiyar kafin lokacin ina haka kike so"? Kaita d'aga tana murmushi cikin jin dad'i tace "shima yace min zanci gaba da karatu na bayan bikin nagode Baffah Allah ya saka da alkairi" "Amin karki damu" Baffah na barin gurin Lami da murnarta ta tashi itama tana shiga daki tace.

"Babah gobe Baffah yace zai kaini islamiya" Ramatu dake daurin gyada soyayyiya sai tumurmusa take jin abinda Lami tace yasa zatai magana ta 'kwaru tari ta ri'ka jerawa har shid'ewa da'kyar tace "kawo min ruwa" fita Lami tai ta debo mata bayan tasha tana numfashi tace "Kika ce gobe Baffah zai kaiki islamiya? Heeeeh lallai kam yau ake yinta to bari kiji wallahi baki isa ki makaranta ba abinda na yanke kenan wacce kika je ki kai a wudil din ma ba'a son raina bane talle zaki min kowa na neman kud'i ni kuma saboda da mutuwar zuciya gaki nan rid'ad'a ina kallon ki saidai kici kisha kije makaranta? Tab garama kisawa kanki salama babu wata makaranta da zakiyi idan ba haka ba lokacin aurenki saidai a kaiki daki hororo ba kaya".

Cikin kuka Lami tace "dan Allah babah ki barni nayi wallahi ina son makarant.................duka Ramatu ta kawo mata tana cewa "ubanki yahau baro🙊 ina magana kina musa min bazaki makarantar ba talle zaki kuma na fad'a zaki tashi ki dauka ki fita ko saina miki shege dukan da zaki kasa tashi shima malam din ina nan daidai dashi" mi'kewa Lami tai tana kuka ta dau farantin gyad'a ta bita Ramatu data bita da kallo tace "kuma saura kije ki zauna a guri daya idan kika dawo min da saura saikin gane" Lami dai bata sake tofa koda alif ba ta fice ta nufi matallata.

Bata fara ciniki da wuri ba sai jikin magriba kasuwa ta bud'e bayan sallar isha Lami ta baro dandali ta sayar gyad'ar tas sai farantin kawai a hannun ta jin taku ana bin bayanta yasa da sauri ta waiga ganin mutum yasa tace.

"Waye"? Shiru ba amsa a tsorace tasa gudu wanda shima ya rufa mata baya ga duhu ga matsatstsan layi tuntu'be tayi da dutse ta fad'i 'kara ta saki daidai ya iso waje da sauri ya toshe mata baki tare da kinkimar ta ya shiga wani kango da ita.

A tsautsayi ya daka mata tsawar cewa ta masa shiru cikin mamaki Lami tace "Tanko kaine me nai maka ka sake ni" kallon ta yayi "oh kin gane ni ashe aiko saina tabbatar ban barki kin kai labari ba yau babu me cetar ki a hannu na yadda kika haramta min auren ki shima wancan mayen da kika wulakanta ni akan sa saina tabbatar bazai same ki ba".

Cikin karfin hali Lami tace "Tanko wulakancin ya isa haka ka sake ni kuma wallahi bazan yarda ba gobe saina kai kararka gurin me gari" dariya yayi "ki kai karata gun wanne me garin? Basai na barki da rai ba balle ki kai labarin" jin abinda yace yasa ta fasa kara tana kai masa duka ta ko'ina shi kuma yana 'ba'bbaka dariya kamar zararre.

Ramatu na zaune lokaci zuwa lokaci ta kalli hanyar kofar shigowa ganin shiru babu alamar ta yasa ta mi'ke tana daukar hijab tace "a'a ni kalau kuwa Lami yau bata dawo ba bata irin wannan daren a dandali bari muga" fita tai ganin yar ma'kotansu abasiyya ta taho yasa Ramatu cewa "ina kika baro lami ko tana can"? Kai abasiyya ta girgiza "a'a ta ma riga ni tahowa saidai in a wani gun ta tsaya" jin haka yasa Ramatu wucewa ta nufi dandalin tana zuwa layin taga farantin da kud'i a baje a gurin salati tayi tana tattare kud'in tare da daukar farantin cikin mamaki ta kalli gabas ta kalli yamma babu alamar kowa da sauri ta fito a layin kamar zata kifa ta koma gida hankali tashe tan kururuwa azo a cece ina Lami tai nan gari ya hargitse aka d'ebo fitilu ana haska ko'ina tace ga inda taga farantin gurin suka je suka fara haskawa har cikin kangon gidan aiko sai gata kwance sharkaf bata motsi jikin ta harda jini da alama fayde akai mata innalillahi wa inna ilaihi raji'un guri ya kaure da salati Ramatu dake waje jiki na rawa tace "meya faru an ganta ne"?..........

Tana rufe baki taga Sabi'u da Habu sun fito dauke da ita ihu ta saki tana cewa "na shiga uku na lalace yau ranar tonon asiri tazo Lami wanne d'an diban albarkar wanda bazai gama da duniya lafiya bane ya miki wannan aika la'ilaha illallahu kaito na dama banga wannan rana ba wannan wanne irin masifa ne da bala'i" hakuri su Salamatu ke bata duk da kowa jikin sa rawa yake aka nufo gida wasu na cewa a kaita asibiti wasu na cewa bata da rai.

Kwantar da ita akai Baffah dake durkushe gabanta yana kallon fuskarta abubuwa da na masa yawo cikin kwakwalwa musamman maganar da sukai na zai kaita makaranta gobe ashe yarinyar nan burin ta nason ganin tayi karatu ta samu ilimi bazai cika ba hawaye ne masu zafi ke zuma daga idon Baffah wanda suke sauka saman goshinta gida kam ya cika da jama'a ya kaure da koke koke mi'kewa Baffah yai da'kyar yabar gurin yayin da masu wankan gawa suka dauketa domin mata sutura bayan su kammala akace ba damar kaita dare yayi saida safe haka tai kwanan keso.
Chapter 30 · 0% Book details