← Book details Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 107 OF 145

Sashe 107

Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Washe gari ya samu Alhaji Aminu ya fad'a masa yadda yayi da matansa duk basu goyi bsya ba saboda kirkin Hajiya Aisha bai kamata a saka mata da aure mata miji ba Alhaji Amanu yana barin gurin Malam Habu ya zarce ya sanar da su komai bsyanin da akai masa a take Hajiya Aisha tace su tashi haka suka sake zuwa duk su ukun gurin malam Habu yayi musu izinin shiga gidansa akai ta musayar magana dan suna nan akan bakarsu Asma'u bazata auri Alhaji Musa ba wannan butulci ne Hajiya Aisha ta nuna musu itace ma ta bashi shawarar da shine yayi tunanin hakan ba amma inaa babu wanda ya yarda da bukatar su karshen batu saida tasa musu kuka ta fad'a musu cewa tana so ya auri Asma'u ne dan ya samu Mai gadonsa ga matsalar dake faruwa dasu duk uwar dukiyar da suka tara babu Mai gadonta dan Allah kada su hana basu san me Allah ya 6oyeba watakila da rabo a tsakani dan Allah su duba al'amarin sai a sannan nefa jikinsu yayi sanyi da'kyar suka amince cewa sun bashi auren Asma'un sannan Jamila ita kuma Saleem yana ciki duk lokaci d'aya za'ai bikin Shima yana so xai koma Canada yaci gaba da school dinsa dama hutu yazo maimakon ace wanda aka baiwa auren 'ya ne zaiyi godiya saboda girmamawa da karamci malam Habu ne ke godiya kamar sunyi masa wata kyauta.

Da yake ba wani abun zafi bane sannan Alhaji Musa bayason maganganun mutane juma'a tana xuwa ya bada sadaki aka d'aura masa aure da Asma'u Jamila da Saleem shalele wai Allah sarki Malam Habu ranar harda kukan farin ciki yayi musamman tuna maganar Ilyah na cewa 'ya'yansa sun jibge sun tsufa a gidansa bazasu auru ba 'ya'ya mata ba'kin ciki ne da damuwa da maza ake tunkaho namiji ne komai in yayi ado ne hummm yau gashi Allah ya basu mazan auren masu daraja da kima wanda ba'ai tunani ba yana fata yadda Allah ya rufa masa asiri yayi auren su Allah ya kawowa sauran suma mazan aure na gari wanda zasu rikesu da mutunci.

A ranar juma'ar aka rakasu saidai Saude bataje ba A'i bataje ba iya Binta ce da Aisha da kuma Amatu zasuyi masu rakiya a junansu Hajiya Aisha da kanta tazo da mota har kofar gida aka fito da Asma'u dasu Binta suka shiga tace tana kunya Jamila surukarta ce zata turo mota a d'auketa bayan sun tafi ankai Asma'u Binta ta shigo motar driver da wasu dangin cikin yan uwan hajiya Aisha da Alhaji Musa suka zo taryan Jamilan itama aka rakata gidan part d'in Saleem shikenan bayan su Binta sun gama komai ta d'an yiwa kowaccensu nasiha ta fito parlor inda su Amatu ke jiranta zasu tafi Hajiya Aisha sai godiya take Mata kamar wanda ta bata kyautar wani gagarumin abu.

Tab su Saleem kam dama tuni anyi ciki ana can anaiwa Jamila shagwa'ba yau😀 Hajiya Aisha tana nan zaune a main parlor har Alhaji Musa ya shigo da mamaki ya kalleta yana cewa.

"Aisha ya naganki ke d'aya ina su Hajiya Hajaran suke ko harsun tafi bamuyi sallama ba"?.

Kaita d'aga tana murmushi tace "eh basu dad'e da tafiya ba nace su tsaya su kwana suka ce min a'a daga baya sa dawo su sake ganin amarya".

"Ok yayi kyau harda Hajiya Rabi'atun"?.

"Ai Alhaji duk sun tafi iya mune a gidan muje na raka ka d'akin amaryarka yau nice abokiyar ango" ta fad'a tana dariya tare da kar'ba kayan hannunsa ta wuce gaba murmushi yai yana bin bayanta uhm Asma'u tana zaune a tsakiya 'katon gado na alfarma ta lullu'ba da mayafi suna shiga kuwa ta nemi nutsuwarta ta rasa inda zatasa kanta domin kunyar Hajiya Aisha dama daya akai auren 'ki tayi itama tace bazata iyaba ta d'auka anbar maganar sai ji tayi wai an d'aura yau wuni ma tayi tana kukan kunya.

Zama Hajiya Aisha tayi a gefen gadon tana d'aga mayafin ta yayeshi zuwa saman kanta tace "uhm Masha Allah Asma'u gaskiya kinyi kyau dole a biya kud'in sayan baki Alhaji saika biya".

Shikam Alhaji Musa tsaye yayi kawai da murmushi a fuskarsa yace "ok nawa zan biya kenan"?.

Gyara zama Hajiya Aisha tai tana cewa "amarya dubu d'ari ni kuma qawarta dubu hamsin😃".

'Dan zaro ido yai cikin wasa yace "kai dama ke qawar amarya ce bayan yanzun nan a parlor kikace kece abokiyar ango kodai Kinga amaryar tafi angon kyau shine zaki koma 6angarenta"?.

Itama d'an zaro idon tai kamar ta manta d'in nan tace "kuma fa anyi haka ashe ni qawar ango ce ai shikenan a biya amaryar nata nice ma zan biya transfer ko cash wanne take so"?.

"Cash take so aje a kawo mata ko zamu samu bakin ya bud'u".

Mi'kewa Hajiya Aisha tai tana fita zuwa minta biyu ta dawo da kud'i d'aure a kyauro tana ajewa a gaban Asma'u da kanta ke sunkuye tace.

"To amarya na wakilci ango na saye bakin duka sai ayi masa magana nizan tafi Allah ya bada zaman lafiya Allah ya sanya alkairi Allah ya kawo mana arziki mai d'orewa wanda zamuyi farin ciki dashi".

Iya Alhaji Musa ne yace Amin a fili Asma'u ta fad'a a zuciyarta kafin Hajiya Aisha ta juya tana fita tsaye Alhaji Musa yai yana kallon Asma'u datai shiru zuwa wani lokaci yace.

"Husnah😁".

Ji Asma'u tai gabanta ya fad'i ta ma kasa amsawa sai numfashin ta dake fita da sauri kawai ta sake qasa da kanta.

"Husnah".

Ya fad'a a karo na biyu da'kyar ta amsa muryarta na rawa can kasa sosai yaji na'am d'in da tace yayi mamaki domin yasan ba haka take ba sau tari yana jin surunta ita da Hajiya idan sunzo aiki to yau d'in meyasa? Kodan yau rana ce musamman a gareta batai kama da sauran ranaku ba tayi dabam kaiya jinjina yana sake qare mata kallo gaskiya 'ya'yan malam Abubakar kyawawa ne kuma duk kama suke dashi gabadaya fuskarsa suka d'auko kyau iya kyau ya fad'a a ransa kafin yace.

"Kinga ki tashi kiyi alwala bari na dawo" yana fad'in haka ya fita dan ya bata sarari ta samu tayi tana ganin ya fita ta mi'ke tana sauka a gadon jiki a sanyaye ta nufi kofar toilet bud'e ta shiga tayo alwalar tana fitowa yana shigowa ya sako jallabiya coffee ya cire wancan shaddar gaba ya wuce ya musu sallar nafila ta godiya da addu'o'i masu tarin yawa na fatan zaman lafiya da alkairi a tsakaninsu sannan ya mi'ke zai sake fita har yaje ba'kin kofa ya juyo yana cewa.

"Ki tashi kici wannan abun sai kiyi wanka ki kwanta kinji"?.

Kai ta d'aga masa a hankali tace "to" yana juyawa ya fita ta mi'ke tana tana zama a gaban gadon gaban glass table din ta bud'e ledar humm d'irka d'irkan kaji ne guda biyu wanda sukaji kyakkyawan gashi da lafiyayyan kayan had'i da'kyar ta samu ta iya cinye cinya daya🍗 tasha fresh milk mai sanyi sosai sannan ta tashi tana cire doguwar rigar jikinta ta duba sabon towel ta d'auka tana cireshi a ledarsa ta d'aura ta shiga wanka tunda tasan ba dawowa zaiyi ba shiyasa ta sake tayi wankanta hankali kwance daidai ta fito d'aure towel kanta ko hula babu kitson da aka d'an'dasa mata sai she'ki yake gashi ba'ki mai santsi dama duk haka gashin kansu yake kuma akwai tsayi sosai da yawa asali gashin kan Baffah ne Malam Habu ya gada kuma shima ya gadar musu.

Tsayawa tai cak a kofar toilet din ko murfin ta kasa saki ta rufe balle ta karaso tsakiyar d'akin kamar yadda shima ya tsaya cak a kofar shigowa bedroom d'in ya zuba mata ido humm tabd'i masha Allah wai ammafa ya samu mace anan🙈 uhn inji mai ciwon baki karasa shigowa d'akin yai yana zama a bakin gadon yace.

"Husnah tsaiwar me kike anan kizo kisa kaya man ki kwanta".

Shiru tai ta kasa magana fahimtar dayai kamar tsoron sa take yasa ya girgiza kai yana murmushi dan ya tabbatar yace.

"Ko bakya jin barcin ne"?.

Da sauri yaga ta d'aga masa kai mamaki ne ya rufeshi amma sai bai sake ce mata komai ba yana dai dariya a cikin ransa ya mi'ke yana kashe wutar d'akin idan kallonta a haka ne ya hanata sakewa yana kashewa ta rutse ido da karfi tana rafka salati jinya d'agota sama ya fara tafiya da ita yasa tace.

"Innalillahi wa Inna ilaihi raji'un na shiga uku😂".

Kai jama'a ba arziki tasa Alhaji Musa ya kama dariya dole duk da yaso mazewa amma yadda ta furta kalma duk wanda yaji saiya mata dariya direta yai akan gadon bayan ya kunne bedside lamp blue da fari haske kad'an ne d'akin yayi kyau yai kala kallonta yai yana cewa.

"Husnah did something scare you"?.

Shiru tai jikinta na rawa hakan datai ya tabbatar tsorata tayi dashi sai kawai ya rungumota jikinsa aiko jiyai ta saka mai kuka😁 murmushi yayi kawai yana girgiza kai ai dama duk amarya sai tayi haka indai ta 'kwarai ce saidai fa ballagaza bazar-bazar itace ke d'oki kwanciya yai da ita a jikinsa yana d'orats akan kirjinsa sai shashshe'kar kuka take cikin tashin hankali ta'ki ta daina shiru yai yana shafa kitson kanta amma tsoron kada ta sanyawa jikinta zazza'bi da wannan kukan yasa ya matso da fuskarta yana had'a bakinsu ko ya samu tai shiru😘. Uhm uhmmm🙊 nikam bari na fece🏃🏃🏃.
Chapter 107 · 0% Book details