Sashe 53
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kai Safyan ya d'aga yana mi'ka masa takardar hannunsa yace "eh yalla'bai gashi sa'ko daga commissioner daga can sama yace a kawo maka" jiki na 'bari yasa hannu ya kar'ba da sauri ya bud'e yana karantawa ganin abinda ke ciki an dakatar dashi aiki sam ba suspect ba balle yasa ran dawowa ba wani abu dazai samu nan gaba takardarsa bazata sake masa wani amfani ba saidai yai kasuwanci yasa ya mi'ke tsaye gumi na tsatstsafo masa yana kallon takardar idonsa yayi ja ransa a mugun'bace yana huci yace.
"What!!!? Ni commissioner zaiwa haka ni zai wulakanta Safyan kaine silar komai kai kaja min asarar rasa aikina wai shin ranar gidan uban wa kaje kabar bakin office d'in nan har wannan tsinannan commissioner ya shigo min office batare da izini naba"?.
Sunkuyar dakai Safyan yai yana cewa "yalla'bai kayi hakuri bada sona bane".
Cikin tsawa ya d'aga masa hannu "zancen banza kenan hakurin uwar wa? Ya zanyi bayan ka jamin masifa ai duk silarka ne komai ya faru munafiki mai ba'kin ido🙊 yanzu me zakace min shashashan banza shashashan wofi da nace ka tsaya a kofar da baka bar gurin ba taya commissioner zai shigo ya kama ni da wannan yarinyar saboda cin mutumci maimakon ya rufa min asiri mu rufe maganar a office d'ina amma dan ya muzanta ni ya nuna ni 'kwarto ne a gaban yarana ya tozartani ya nuna ni ba mutumin arziki bane eh me zakace akan haka"?.
Shi dai Safyan shiru yai yana sauraron sa dama yasan irin wannan ranar zata zo kullum mutum ka girma amma kana da budurwar zuciya da son lalata yaran mutane kawai ka basu kud'i da motoci dan jin dad'i kamar kai baka haifa ba.
"Safyan tunanin uban me kake ne? Wato ina magana ka mayar dani majnun ko? Yanzun ina commissionern yake"?.
"Ai yalla'bai ba shine yazo ba wani drivern sa ya baiwa shine kawo kuma bai zauna ba tafiya yai".
Komawa yai da baya takwash ya zauna akan kujerar yana sake kallon takardar dasa hannun Governor shikenan ya shiga uku ya fito rana gashi wasu ma'kudan miliyoyin kud'ad'e da yake jiran shigowar su 'karshen wannan watan ne ga bala'in daya same shi tonan asiri biyu babu wanda yasan yayi danniyar kud'in na al-umma ne da gwamna ya bayar ayi musu aiki ya 'boye amma yasan dole yanzu kowa ya sani har gidajen TV za'a yad'ashi dafe kai yayi ransa na 'kuna kansa ya d'au zafi yace.
"Zaka iya tafiya".
"To yalla'bai a huta lafiya" Safyan ya fad'a yana fita "uban na huta ina cikin masifar taya zan samu lokacin hutu" ya karasa maganar yana huci shiru yai yana tunani zuwa wani lokaci ya rasa abinda yake masa dad'i jin ana kiransa a waya yasa ya d'auka jikinsa har rawa yake ya d'aga yana cewa.
"Hello haba commissioner ya zakai min haka wannan wanne irin cin mutumci ne da cin fuska ka nuna min"?.
Daga can 'bangaren commissioner yace "Prof ya kake"? Haushi maganar ta bashi kamar zaice ban sani ba sai kuma yace "ina lafiya amma yanzu abinda kai min ka kyauta kenan commissioner"? Cikin basarwa commissioner yace "oh sa'kon ya iso gareka kenan? Jin yai shiru yaci gaba "idan ka duba zakaga from Governor ne bani ba nima dan aike ne kawai aka bani kuma na isar dan haka yace a fad'a maka babu kai babu 'kara yin aikin gomnati har abada bayan haka yace sisi bazaka samu ba sannan wannan miliyoyin kud'ad'e da kace sunyi 'batan dabo watan daya wuce yanzu yace a fad'a maka ya samesu ta asusun jarinka da yake Australia na kamfanin ka ta hannun Mr wiliyam Emmanuel ka gane gobe zai aika ayi masa 'kwakkwaran bincike acan da abubuwanka saiya tabbatar wannan kamfanin iya kud'in kane Babu na gwamnati a ciki".
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un shine abinda Prof Jibril yake maimaitawa bayan jin jawabin commissioner muryarsa na rawa yace "commissioner ka taimaka min dan Allah ka roki Governor ya rufa min asiri karya sanar da mutane komai karyaje Australia bincike wallahi zan kar'bo kud'ad'en da kaina zan na dawo dashi amma dan Allah karya fitar da wannan maganar tunda babu wanda ya sani" kai commissioner ya girgiza "a'a prof aikin gama ya gama bazan iya taimakon kaba maganar gaskiya laifin ka babbane ba kowa zai iya gyara maka ba saidai kayi hakuri ka d'auka cewa kamar da bakai aikin gwamnati ba kuma bawai dan mun kama ka da wannan yarinyar bane ko d'aya kar kayi tunanin haka dama gwamna ya gano cewa wadannan kud'ad'en ba 'bata sukai ba kaine ka dannesu ka gane"? Tsaki Prof yaja mai karfi wanda yasa commissioner cewa "oh tsaki ma kake min? To ai shikenan bari na barka da gwamnan sai naga yadda zaka 'kwaci kanka tunda kaiba mutumin arziki bane" jin abinda commissioner ke cewa yasa Prof yace "a'a dan Allah commissioner kayi hakuri kar muyi haka dai kai kasan duk lokacin da akace rai ya 'baci hankali ya 'bata to hankali ne ke nemoshi kaine ka fusata ni shiyasa kaja nai maka tsaki" kai commissioner ya jinjina yana cewa "hakan yayi kyau ai gara dana fusata ka tunda har ka gane idan hankali ya bata hankali ne ke nemoshi kaga da kanka kace hankalin ka ya 'bata kana lalata yaran mutane kamar ka manta kai baka haifa ba amma idan akaiwa naka baza kaji haushi ba haka ne"? Muryar Prof da tsawa yace "enough is enough malam commissioner karka nemi fad'a min magana dan kaga ina kas da kai ina neman taimako a gurinka baka isa ka wulakanta niba" shiru commissioner yai cikin mamaki jin Prof yace "hello kana jina"? Yasa yace "bana jinka amma tunda kai kana jina ka huta gajiya sai anjima" a gigice prof ke cewa "hello hello commissioner please karka kashe min waya ka tsaya ka saurare ni" jin d'if yasa ya kalli secreen din wayar wato ya katse wani wawan tsaki yaja yana buga wayar a jikin bango a fusace ya fice daga office d'in yai hanyar gurin parking din motoci a miliyon ya d'ebi motar da gudu sosai ko lura da yanayin hanya bayai haka ya isa office d'in commissioner ido rufe ba neman izini yaje fakam fakam zai shiga securities suka tare shi kokarin 'kwacewa yake wani gurmujejen 'kato ya kinkime shi yana fita dashi daga gurin saida ya kaishi har waje zai ja kofa ya rufe sannan ya kalleshi yana cewa "commissioner ne ya bada umarni duk wanda yazo karmu barshi ya shiga domin yana aiki ne" yana fadin haka yaja kofar ya rufe.
Kallon kofar ya tsaya yi kamar zai fasa ihu dan ba'kin ciki kafin a fusace ya shiga mota hankali tashe ya nufi gida horn d'in daya sakarwa mai gadi har Saida ya tsoratashi aguje ya tashi yana bud'ewa ko a tsiyace ya danno kan motar wanda a d'ari mai gadin yai gefe cike da mamakin meya samu mai gidan nasa yau ko parking bai gama daidaitawa ba ya bud'e murfin motar cikin azama ya fito yana yin hanyar shiga ciki dan sauri har takalmansa ya zubar da hular kansa duk ya had'a gumi yana karasawa cikin falon ya soma zunduma kira.
"HALIMA KE HALIMA KINA INA FITO YAU MASIFA TA SAMENI😣" da gudu ta fito ta ganshi sai kaiwa da komowa yake ya cire babbar rigarsa yayi jifa da ita gefe cike da mamaki tace "alhaji lafiya na ganka a haka"?.
"Hummm Halima ina fa lafiya yau na shiga uku na fito rana dama na mutu kafin naga irin wannan 'bacin ran daya sameni yau".
"Tofa subahanallahi alhaji wani abu ne ya faru"?.
"Meye ma bai faru ba nida wannan tsinannan commissionern ne yasa gwamna ya dakatar dani aiki har abada indai na gwamnati ne ya 'bata takarduna".
Zaro ido tai "to duk meya kawo haka kaidin meya had'aku dashi har abin yai zafi haka"?.
Shiru yai ya kasa bata amsa domin bazai iya ce mata kamashi commissioner yai tare da yarinya ba duk da dama tasan neman mata halinsa ne amma yana jin kunyar ce mata ga abinda ya faru................,...
"Alhaji magana nake menene ya had'a ku"?.
Zama yai cikin takaici yana kallon ta yace "akan baby ne".
Da mamaki Halima tace "baby kuma🙄😏😲? Humm tabdijam yau ake yinta wai tsakani da Allah dama alhaji baka daina mu'amala da yarinyar nan ba inace kayi alkawari ashe tuban ba'kin muzuru kai gaskiya ba ka kyautawa kaima ka haifa fa ya kamata ka daina abinda kakeyi ka roki ubangiji yafiya..........................
'Daga mata hannu yai "ya isa haka Halima ba wa'azi nace kimin ba I know abubuwan da nake aikatawa was improper saidai a halin yanzu ba wannan ne damuwata ba, ba wannan maganar nake bukatar jiba ki rufe min baki".
Dama tasan haka zai faru duk lokacin datai masa magana akan haka balbaleta yake da fad'an cewa babu ruwanta idone nata in duniya ce da more shagalin rayuwa yanzu ya fara".
Sauke ajiyar zuciya tai tana cewa "Allah ya baka hakuri" d'an tsaki yaja yana mi'kewa yace "yau zan tafi Australia zanje shima Mr Wiliyam d'in naci uban daya haifi ubansa mitsiyaci maci amana duk bashi kuka d'auka wallahil azim commissioner sai kunyi nadamar abinda kukai min bazan 'kyale kuba zaku sani".
Jin furucin da yake yasa Halima tace "a'a alhaji karkaje kayi abinda daga baya za'a zo ayi dana sani ka tsaya kayi nazari maybe kaine da laifi" tana rufe baki ya daka mata tsawa "Halima ya ishe ki kema tunda baki damu da damuwata ba kin goya musu baya to ki kyale ni nadau fansata" fuuuu ya wuce ta bishi da kallo tare da girgiza kai tace "tabdijan dama nasan koba dad'e koba jima sai wannan ranar tazo asirin ka zai tonu kullum ina tunatar maka amma ga irinta nan yanzu wa gari ya wayewa? Fatana Allah ya kyauta karka jawowa kanka wata masifar dan ko biyu bana rabawa idan kace zaka nunawa Wiliyam wani abu tofa za'ai babu kai mutumin da yake tsaface tsaface har kace zakaja dashi" mi'kewa tai tana bin bayansa da niyyar ta sake tausarsa ta hana shi zuwa Australia taga ko zata iya Allah yasa yaji maganar ta ya ha'kura.
"What!!!? Ni commissioner zaiwa haka ni zai wulakanta Safyan kaine silar komai kai kaja min asarar rasa aikina wai shin ranar gidan uban wa kaje kabar bakin office d'in nan har wannan tsinannan commissioner ya shigo min office batare da izini naba"?.
Sunkuyar dakai Safyan yai yana cewa "yalla'bai kayi hakuri bada sona bane".
Cikin tsawa ya d'aga masa hannu "zancen banza kenan hakurin uwar wa? Ya zanyi bayan ka jamin masifa ai duk silarka ne komai ya faru munafiki mai ba'kin ido🙊 yanzu me zakace min shashashan banza shashashan wofi da nace ka tsaya a kofar da baka bar gurin ba taya commissioner zai shigo ya kama ni da wannan yarinyar saboda cin mutumci maimakon ya rufa min asiri mu rufe maganar a office d'ina amma dan ya muzanta ni ya nuna ni 'kwarto ne a gaban yarana ya tozartani ya nuna ni ba mutumin arziki bane eh me zakace akan haka"?.
Shi dai Safyan shiru yai yana sauraron sa dama yasan irin wannan ranar zata zo kullum mutum ka girma amma kana da budurwar zuciya da son lalata yaran mutane kawai ka basu kud'i da motoci dan jin dad'i kamar kai baka haifa ba.
"Safyan tunanin uban me kake ne? Wato ina magana ka mayar dani majnun ko? Yanzun ina commissionern yake"?.
"Ai yalla'bai ba shine yazo ba wani drivern sa ya baiwa shine kawo kuma bai zauna ba tafiya yai".
Komawa yai da baya takwash ya zauna akan kujerar yana sake kallon takardar dasa hannun Governor shikenan ya shiga uku ya fito rana gashi wasu ma'kudan miliyoyin kud'ad'e da yake jiran shigowar su 'karshen wannan watan ne ga bala'in daya same shi tonan asiri biyu babu wanda yasan yayi danniyar kud'in na al-umma ne da gwamna ya bayar ayi musu aiki ya 'boye amma yasan dole yanzu kowa ya sani har gidajen TV za'a yad'ashi dafe kai yayi ransa na 'kuna kansa ya d'au zafi yace.
"Zaka iya tafiya".
"To yalla'bai a huta lafiya" Safyan ya fad'a yana fita "uban na huta ina cikin masifar taya zan samu lokacin hutu" ya karasa maganar yana huci shiru yai yana tunani zuwa wani lokaci ya rasa abinda yake masa dad'i jin ana kiransa a waya yasa ya d'auka jikinsa har rawa yake ya d'aga yana cewa.
"Hello haba commissioner ya zakai min haka wannan wanne irin cin mutumci ne da cin fuska ka nuna min"?.
Daga can 'bangaren commissioner yace "Prof ya kake"? Haushi maganar ta bashi kamar zaice ban sani ba sai kuma yace "ina lafiya amma yanzu abinda kai min ka kyauta kenan commissioner"? Cikin basarwa commissioner yace "oh sa'kon ya iso gareka kenan? Jin yai shiru yaci gaba "idan ka duba zakaga from Governor ne bani ba nima dan aike ne kawai aka bani kuma na isar dan haka yace a fad'a maka babu kai babu 'kara yin aikin gomnati har abada bayan haka yace sisi bazaka samu ba sannan wannan miliyoyin kud'ad'e da kace sunyi 'batan dabo watan daya wuce yanzu yace a fad'a maka ya samesu ta asusun jarinka da yake Australia na kamfanin ka ta hannun Mr wiliyam Emmanuel ka gane gobe zai aika ayi masa 'kwakkwaran bincike acan da abubuwanka saiya tabbatar wannan kamfanin iya kud'in kane Babu na gwamnati a ciki".
Innalillahi wa inna ilaihi raji'un shine abinda Prof Jibril yake maimaitawa bayan jin jawabin commissioner muryarsa na rawa yace "commissioner ka taimaka min dan Allah ka roki Governor ya rufa min asiri karya sanar da mutane komai karyaje Australia bincike wallahi zan kar'bo kud'ad'en da kaina zan na dawo dashi amma dan Allah karya fitar da wannan maganar tunda babu wanda ya sani" kai commissioner ya girgiza "a'a prof aikin gama ya gama bazan iya taimakon kaba maganar gaskiya laifin ka babbane ba kowa zai iya gyara maka ba saidai kayi hakuri ka d'auka cewa kamar da bakai aikin gwamnati ba kuma bawai dan mun kama ka da wannan yarinyar bane ko d'aya kar kayi tunanin haka dama gwamna ya gano cewa wadannan kud'ad'en ba 'bata sukai ba kaine ka dannesu ka gane"? Tsaki Prof yaja mai karfi wanda yasa commissioner cewa "oh tsaki ma kake min? To ai shikenan bari na barka da gwamnan sai naga yadda zaka 'kwaci kanka tunda kaiba mutumin arziki bane" jin abinda commissioner ke cewa yasa Prof yace "a'a dan Allah commissioner kayi hakuri kar muyi haka dai kai kasan duk lokacin da akace rai ya 'baci hankali ya 'bata to hankali ne ke nemoshi kaine ka fusata ni shiyasa kaja nai maka tsaki" kai commissioner ya jinjina yana cewa "hakan yayi kyau ai gara dana fusata ka tunda har ka gane idan hankali ya bata hankali ne ke nemoshi kaga da kanka kace hankalin ka ya 'bata kana lalata yaran mutane kamar ka manta kai baka haifa ba amma idan akaiwa naka baza kaji haushi ba haka ne"? Muryar Prof da tsawa yace "enough is enough malam commissioner karka nemi fad'a min magana dan kaga ina kas da kai ina neman taimako a gurinka baka isa ka wulakanta niba" shiru commissioner yai cikin mamaki jin Prof yace "hello kana jina"? Yasa yace "bana jinka amma tunda kai kana jina ka huta gajiya sai anjima" a gigice prof ke cewa "hello hello commissioner please karka kashe min waya ka tsaya ka saurare ni" jin d'if yasa ya kalli secreen din wayar wato ya katse wani wawan tsaki yaja yana buga wayar a jikin bango a fusace ya fice daga office d'in yai hanyar gurin parking din motoci a miliyon ya d'ebi motar da gudu sosai ko lura da yanayin hanya bayai haka ya isa office d'in commissioner ido rufe ba neman izini yaje fakam fakam zai shiga securities suka tare shi kokarin 'kwacewa yake wani gurmujejen 'kato ya kinkime shi yana fita dashi daga gurin saida ya kaishi har waje zai ja kofa ya rufe sannan ya kalleshi yana cewa "commissioner ne ya bada umarni duk wanda yazo karmu barshi ya shiga domin yana aiki ne" yana fadin haka yaja kofar ya rufe.
Kallon kofar ya tsaya yi kamar zai fasa ihu dan ba'kin ciki kafin a fusace ya shiga mota hankali tashe ya nufi gida horn d'in daya sakarwa mai gadi har Saida ya tsoratashi aguje ya tashi yana bud'ewa ko a tsiyace ya danno kan motar wanda a d'ari mai gadin yai gefe cike da mamakin meya samu mai gidan nasa yau ko parking bai gama daidaitawa ba ya bud'e murfin motar cikin azama ya fito yana yin hanyar shiga ciki dan sauri har takalmansa ya zubar da hular kansa duk ya had'a gumi yana karasawa cikin falon ya soma zunduma kira.
"HALIMA KE HALIMA KINA INA FITO YAU MASIFA TA SAMENI😣" da gudu ta fito ta ganshi sai kaiwa da komowa yake ya cire babbar rigarsa yayi jifa da ita gefe cike da mamaki tace "alhaji lafiya na ganka a haka"?.
"Hummm Halima ina fa lafiya yau na shiga uku na fito rana dama na mutu kafin naga irin wannan 'bacin ran daya sameni yau".
"Tofa subahanallahi alhaji wani abu ne ya faru"?.
"Meye ma bai faru ba nida wannan tsinannan commissionern ne yasa gwamna ya dakatar dani aiki har abada indai na gwamnati ne ya 'bata takarduna".
Zaro ido tai "to duk meya kawo haka kaidin meya had'aku dashi har abin yai zafi haka"?.
Shiru yai ya kasa bata amsa domin bazai iya ce mata kamashi commissioner yai tare da yarinya ba duk da dama tasan neman mata halinsa ne amma yana jin kunyar ce mata ga abinda ya faru................,...
"Alhaji magana nake menene ya had'a ku"?.
Zama yai cikin takaici yana kallon ta yace "akan baby ne".
Da mamaki Halima tace "baby kuma🙄😏😲? Humm tabdijam yau ake yinta wai tsakani da Allah dama alhaji baka daina mu'amala da yarinyar nan ba inace kayi alkawari ashe tuban ba'kin muzuru kai gaskiya ba ka kyautawa kaima ka haifa fa ya kamata ka daina abinda kakeyi ka roki ubangiji yafiya..........................
'Daga mata hannu yai "ya isa haka Halima ba wa'azi nace kimin ba I know abubuwan da nake aikatawa was improper saidai a halin yanzu ba wannan ne damuwata ba, ba wannan maganar nake bukatar jiba ki rufe min baki".
Dama tasan haka zai faru duk lokacin datai masa magana akan haka balbaleta yake da fad'an cewa babu ruwanta idone nata in duniya ce da more shagalin rayuwa yanzu ya fara".
Sauke ajiyar zuciya tai tana cewa "Allah ya baka hakuri" d'an tsaki yaja yana mi'kewa yace "yau zan tafi Australia zanje shima Mr Wiliyam d'in naci uban daya haifi ubansa mitsiyaci maci amana duk bashi kuka d'auka wallahil azim commissioner sai kunyi nadamar abinda kukai min bazan 'kyale kuba zaku sani".
Jin furucin da yake yasa Halima tace "a'a alhaji karkaje kayi abinda daga baya za'a zo ayi dana sani ka tsaya kayi nazari maybe kaine da laifi" tana rufe baki ya daka mata tsawa "Halima ya ishe ki kema tunda baki damu da damuwata ba kin goya musu baya to ki kyale ni nadau fansata" fuuuu ya wuce ta bishi da kallo tare da girgiza kai tace "tabdijan dama nasan koba dad'e koba jima sai wannan ranar tazo asirin ka zai tonu kullum ina tunatar maka amma ga irinta nan yanzu wa gari ya wayewa? Fatana Allah ya kyauta karka jawowa kanka wata masifar dan ko biyu bana rabawa idan kace zaka nunawa Wiliyam wani abu tofa za'ai babu kai mutumin da yake tsaface tsaface har kace zakaja dashi" mi'kewa tai tana bin bayansa da niyyar ta sake tausarsa ta hana shi zuwa Australia taga ko zata iya Allah yasa yaji maganar ta ya ha'kura.