Sashe 39
Me Kamar Sarki Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Yana gama fad'in haka taga gurin ya cika da dodannin masu jan ido da gashi ga babban nasu yana mata kallon nama a dafe a kwano hannunsa ya d'aga yana nuna Ramatu sai ji tayi anyi sama da ita suuu zuwa wani lokaci taji tayo kasa taffff sai gata zaune a gaban sa kan wani dutsi na tsafi an kewaye ta tana tsiyayar wuta mai ci sosai a wannan lokacin kasa kuka Ramatu tai ta 'kame guri daya kawai tana jiran mutuwarta.
"Meye ya kawo ki nan, me kika zoyi a gurin muuu? Fad'i muna sauraron ki".
Bakin Ramatu ne ya soma rawa ta kasa magana tsabar tsananin tsoro sai kakkarwa take.
"Kiyi maganaaa mu ba'ai mana shiru anan idan kuma ba haka ba zamuyi farfesun ki"😁.
Zaro ido Ramatu tai hawaye na zuba batasan lokacin data d'ora hannu aka ba tana cewa.
"Kuyi hakuri kada ku kashe ni dan Allah.................
Tsawa duk suka daka mata "rufe mana baki kafin mu cinye ki danya yanzun nan fad'i bukatar ki".
Da'kyar Ramatu ta iya saita kanta har lokacin muryarta bai daina rawa ba ta soma magana.
"Dama na kawo 'karar kishiya ta ne tayi wa d'ana Ilyah asiri ya daina sana'a duk kudinsa ya kare baya ta'buka abin arziki shine nace inaso itama yadda bata bari naji dad'i ba kar nata d'an ya jiyar da ita dad'i".
"Mun fahimce ki amma ba itace taiwa d'an ki asiri ba saidai dama mu ba'a neman mu da alkairi zalunci kadai muke sonyi yanzu me kike so ayi mata?.
Dan shiru Ramatu tayi tana tunanin muguntar da zata had'a mata kafin ta d'ago tana cewa.
"Boka so nake ayi mata abinda zaka kamu da jinyar kwanciya wacce har abada bazata 'kara tashi zaune ba dukiyar da take ta'kama d'anta yana dashi ta 'kare a wajen nema mata magani shine abinda nake so".
Dariya duk gurin suka kama sunayin wata wasu irin maganganu.
"Yadda zaki aikin ki bari sai 'kafa ta dauke cikin dare kowa yana barci zaki fito bayan gari da ruwa ki zuba magani a ciki saiki wanka da ruwan a gurin ga wani d'an gatari dashi zaki tonon da zaki binne maganin saiki kira sunan Salamatu sau uku kina kafta gatarin a kasa idan kin gama saiki mi'ke ki koma gida canma kije kiyi haka ki tababata babu wanda ya ganki to zaki nasara shikenan kin gama komai burin ki zai cika amma ki sani idan kika fara aikin mu babu dainawa duk randa wani ya kamaki zaki mutu idan kikai kuskure zaki mutu kuma ba'a mayar mana da aikin mu sannan abinda kika aikatawa wani ko wata rana zai dawo kanki".
Zaro ido Ramatu tai kamar zai fito waje tace "zai dawo kaina a'a boka na fasa na hakura zan canza wani guri...........
Marin da aka kifa mata ne ya hana ta karasa abinda take son cewa har ha'korin ta daya Saida ya fita cikin mamaki taga katon dodan ya dauka ya sashi a bakinsa ji kake karass kass yana taunawa kamar ya samu kwakwa yana ya bud'e bakinsa saiga wata tsuntsuwa ta fito ba'ka wuluk tazo ta sauka a gaban ta tana aje mata wasu abubuwa kafin ta koma wannan ha'korin nata daya fita.
Ihu Ramatu tai wanda hakan ya baiwa ha'korin dama komawa bakinta ya dasu a inda ya fito hannu tasa tana shirin d'id'oshi daga bakinta tsawar data sauka yasa a firgice ta matse jikin ta guri daya a bisa tsautsayi ta d'od'awa yatsarta cizo harda jini.
"Dauki kibar nan ladan aikin mu saiya ci zaki dawo nan da wata biyu idan kuma baki dawo ba mu zamu nemo ki har inda kike kada ki saki kiyi kuskure idan kin tafi ba waiwaye kada ki fad'awa wani koda d'anki ne".
Mi'kewa Ramatu tai jiki na 'bari tabar gurin ba takalmi ba d'an kwali balle gyale duk ta zubar dasu haka ta ri'ka cin gudu har taje bayan gari tsayawa tai tana haki ganin babu kowa yasa tayi ta shiga wani gida dake farkon gari sunyi shanyar kaya ta zari hijab babu tambaya tai gaba abinta.
Da yake tunda Ilyah ya gama gidansa ta koma can da d'akin ta da komai nata yasa kai tsaye ta wuce gidan a gaban murhu taga Bara'atu zaune tana aikin abinci batare da tai mata sallama ba ta wuce d'aki a gajiye tsaki Bara'atu taja cikin takaici tace.
"Wannan mata sai nayi maganinki da ina zaune lafiya haka kawai ya wani kawo min ita wannan ai jaraba ce duk tazo ta addabi rayuwa ta wallahi bazai yuwu ba bari ya dawo koya sauya min gida ko kuma ya sakeni gara na hakura da aurensa"..........
Jitai Ramatu tace "ke me kike cewa dan uwarki"?.
Mamaki ne ya kama Bara'atu jin yadda babu mutunci Ramatu take kallon tsabar idonta tana zakin iyayen ta.......
Katse mata tunani Ramatu tai "dake fa nake yar matsiyata wato na lura saboda da dacan kin samu guri kin bararraje kina cutar d'ana kina d'ebe masa kud'i ki kaiwa matalautan iyayen ki yanzu kuma nazo na kafa na tsare akan dukiyar d'ana shine kike zagina ko dan an rufa miki asiri an aureki shekara uku baki haihu ba amma keda za'a kora har kike batun a raba gida dan gwafar ubanki bari Ilyan ya dawo sai naga wanda zai za'ba tsanani na dake shed'aniya".
Ta karasa maganar tana daukar kwano taje ta dauko d'umamen tuwo ta koma d'aki tagumi Bara'atu tai cike da bacin rai wannan wacce irin masifa ce dan iyayenka basu dashi sai aita goranta maka harda haihuwa cigaba tayi da aikinta Ramatu dake d'aki sai aiko mata da zagi take ta tafar sauke bata ce mata ba.
Sai aikin sharar hawaye kawai take shigowar Ilyah kenan ganin tana kuka yace "ke kuma fa lafiya"?.
Daga d'aki Ramatu tace "dani ne ka saki wannan matsiyaciyar matar taka saina yi maganin ta zatasan wace Ramatu" d'an tsaki Ilyah yaja yana cewa "na saketa kamarya meye kuma ya faru"?.
"Au meye ya faru ma kake tambaya"? Jin yayi shiru yasa ta fitowa ganin ya juya zai fice daga gidan ga kuma ba'kar leda ya aje a kusa da Bara'atun yasa da gudu taje ta dauke har zaninta na neman fad'uwa kasa tace.
"Kai Ilyah zonan so'ko'kon banza so'ko'kon wofi har dan nayi maka magana akan wannan figaggiyar matar taka zaka wani fice ka barni ina 'ba'batu kamar zakar da take 'kwai wannan abun cikin ledar uban me ka sayo mata".
Dakatawa yai batare daya juyo ba yace "kifi ne zatai mana abinci dashi" yana fad'in haka yai waje.
"Kifii🦈🐠" Ramatu ta fad'a harda zaro ido tana bud'e ledar ganin su tayi da yawa kai ta jinjina "ah lallai kam yanzu wannan uban kifi daya sayo da bana nan shikenan saidai kici naci sauran ki tattara ki kaiwa almajiran gyatumin ki ko? To Allah ya tuno asirin ki yau ina nan za'a gama girki sai an zuba min nawa ina kallo dan baza'a ri'ka cuta taba haka kawai nida haihuwa keda morewa".
Ita dai Bara'atu tana shiru batace mata komai ba cikin hararrami Ramatu tace "ke ba dake nake magana ba dan 'kwanjin ubanki nace ki dauko kwano na juye" mi'kewa Bara'atu tai takaici fal ranta taje ta dauko tana kawo mata kad'an ta zuba tana cewa "wannan ya isa abincin wannan kuma nawa ne nan da gobe ina ci a hankali zan cinye kayana dauki kije".
Saida ta bari ta d'auke ta koma gaban murhun tana gyarawa da cire 'kaya saboda soyayye ne farat Ramatu tace "ke Barah tashi anan yau nice zanyi girkin bake ba daga yau bi da bi za munayi" tsananin mamaki ne ya kama Bara'atu har batasan lokacin da tace "bi da bi kuma? Sai kace kishiya ta".
Mi'kewa Ramatu tai daga inda take zaune tare da cewa "au sai kace kishiyar ki? Dan malafar ubanki nice kikewa haka dan darar ubanki shigiya tsinanniya mai siffar angulu zaki ban guri ko saina karya miki kafa kika tsaya ina magana kina kallo na da baka'ken idanu kamar kwallon d'inya ko nayi mike kama da tamilalliyar uwartaki ne me zubin itacen rimi da siraran kafafu kamar na sauro ai indai bala'i ne yanzu kika fara sha a gidan nan dan darar ubanki" ganin zata bangaje ta yasa da sauri Bara'atu ta matsa gefe ta bata gurin.
Zama Ramatu tai tana kallon yadda mai yake yawo a saman abincin tace "humm yo abune ga d'an talaka ba'a saba ba ansha fura an mutu idan ba tsabar ke ba'kar gidahuma bace taya zaki kwarar irin wannan man a cikin abinci sai kinsa mun harbu da ciwon bayamma au wato so kike Ilyasu ya sha mai da yawa ya mutu dan ki samu gado tunda baki haihu ba ko? Tab tirrr da halinki in Allah ya yarda saikin riga Ilyah mutuwa gadon da kike kwad'ayi baza ki samu ba balle har kiyi tunani gyarawa fatararrun iyayen naki ru'babben gidan su".
Ko bari abincin ya dahu Ramatu batai ba ta d'iba tare da zubawa akan kifin data baiwa Bara'atu asa a girki kawai ta koma d'aki tana cewa "na d'ebi rabo na sai kije kiyita cin kasa inda babu mai ba maggi muguwar mace wai ni zata asirce dama ai naji ance har rubutu kandiya take kawo miki kina mana abinci dashi dan ki mallake mu to bari kiji wallahi munfi karfin ki nan gani nan bari d'umamen maiya".
Shiru Bara'atu tai tana kallon kofar d'akin Ramatu kafin ta d'an girgiza kai tana daukar tukunyar tayi taku daya biyu taji sallamar 'kanwarta d'an waigawa tai cikin danne d'aci da takaicin da ta kwasa tace.
"Lawisa kece shigo mana ya kika tsaya anan"?.
Bata karaso ba tace "eh babah ce ta aiko ni wai......................
"Meye ya kawo ki nan, me kika zoyi a gurin muuu? Fad'i muna sauraron ki".
Bakin Ramatu ne ya soma rawa ta kasa magana tsabar tsananin tsoro sai kakkarwa take.
"Kiyi maganaaa mu ba'ai mana shiru anan idan kuma ba haka ba zamuyi farfesun ki"😁.
Zaro ido Ramatu tai hawaye na zuba batasan lokacin data d'ora hannu aka ba tana cewa.
"Kuyi hakuri kada ku kashe ni dan Allah.................
Tsawa duk suka daka mata "rufe mana baki kafin mu cinye ki danya yanzun nan fad'i bukatar ki".
Da'kyar Ramatu ta iya saita kanta har lokacin muryarta bai daina rawa ba ta soma magana.
"Dama na kawo 'karar kishiya ta ne tayi wa d'ana Ilyah asiri ya daina sana'a duk kudinsa ya kare baya ta'buka abin arziki shine nace inaso itama yadda bata bari naji dad'i ba kar nata d'an ya jiyar da ita dad'i".
"Mun fahimce ki amma ba itace taiwa d'an ki asiri ba saidai dama mu ba'a neman mu da alkairi zalunci kadai muke sonyi yanzu me kike so ayi mata?.
Dan shiru Ramatu tayi tana tunanin muguntar da zata had'a mata kafin ta d'ago tana cewa.
"Boka so nake ayi mata abinda zaka kamu da jinyar kwanciya wacce har abada bazata 'kara tashi zaune ba dukiyar da take ta'kama d'anta yana dashi ta 'kare a wajen nema mata magani shine abinda nake so".
Dariya duk gurin suka kama sunayin wata wasu irin maganganu.
"Yadda zaki aikin ki bari sai 'kafa ta dauke cikin dare kowa yana barci zaki fito bayan gari da ruwa ki zuba magani a ciki saiki wanka da ruwan a gurin ga wani d'an gatari dashi zaki tonon da zaki binne maganin saiki kira sunan Salamatu sau uku kina kafta gatarin a kasa idan kin gama saiki mi'ke ki koma gida canma kije kiyi haka ki tababata babu wanda ya ganki to zaki nasara shikenan kin gama komai burin ki zai cika amma ki sani idan kika fara aikin mu babu dainawa duk randa wani ya kamaki zaki mutu idan kikai kuskure zaki mutu kuma ba'a mayar mana da aikin mu sannan abinda kika aikatawa wani ko wata rana zai dawo kanki".
Zaro ido Ramatu tai kamar zai fito waje tace "zai dawo kaina a'a boka na fasa na hakura zan canza wani guri...........
Marin da aka kifa mata ne ya hana ta karasa abinda take son cewa har ha'korin ta daya Saida ya fita cikin mamaki taga katon dodan ya dauka ya sashi a bakinsa ji kake karass kass yana taunawa kamar ya samu kwakwa yana ya bud'e bakinsa saiga wata tsuntsuwa ta fito ba'ka wuluk tazo ta sauka a gaban ta tana aje mata wasu abubuwa kafin ta koma wannan ha'korin nata daya fita.
Ihu Ramatu tai wanda hakan ya baiwa ha'korin dama komawa bakinta ya dasu a inda ya fito hannu tasa tana shirin d'id'oshi daga bakinta tsawar data sauka yasa a firgice ta matse jikin ta guri daya a bisa tsautsayi ta d'od'awa yatsarta cizo harda jini.
"Dauki kibar nan ladan aikin mu saiya ci zaki dawo nan da wata biyu idan kuma baki dawo ba mu zamu nemo ki har inda kike kada ki saki kiyi kuskure idan kin tafi ba waiwaye kada ki fad'awa wani koda d'anki ne".
Mi'kewa Ramatu tai jiki na 'bari tabar gurin ba takalmi ba d'an kwali balle gyale duk ta zubar dasu haka ta ri'ka cin gudu har taje bayan gari tsayawa tai tana haki ganin babu kowa yasa tayi ta shiga wani gida dake farkon gari sunyi shanyar kaya ta zari hijab babu tambaya tai gaba abinta.
Da yake tunda Ilyah ya gama gidansa ta koma can da d'akin ta da komai nata yasa kai tsaye ta wuce gidan a gaban murhu taga Bara'atu zaune tana aikin abinci batare da tai mata sallama ba ta wuce d'aki a gajiye tsaki Bara'atu taja cikin takaici tace.
"Wannan mata sai nayi maganinki da ina zaune lafiya haka kawai ya wani kawo min ita wannan ai jaraba ce duk tazo ta addabi rayuwa ta wallahi bazai yuwu ba bari ya dawo koya sauya min gida ko kuma ya sakeni gara na hakura da aurensa"..........
Jitai Ramatu tace "ke me kike cewa dan uwarki"?.
Mamaki ne ya kama Bara'atu jin yadda babu mutunci Ramatu take kallon tsabar idonta tana zakin iyayen ta.......
Katse mata tunani Ramatu tai "dake fa nake yar matsiyata wato na lura saboda da dacan kin samu guri kin bararraje kina cutar d'ana kina d'ebe masa kud'i ki kaiwa matalautan iyayen ki yanzu kuma nazo na kafa na tsare akan dukiyar d'ana shine kike zagina ko dan an rufa miki asiri an aureki shekara uku baki haihu ba amma keda za'a kora har kike batun a raba gida dan gwafar ubanki bari Ilyan ya dawo sai naga wanda zai za'ba tsanani na dake shed'aniya".
Ta karasa maganar tana daukar kwano taje ta dauko d'umamen tuwo ta koma d'aki tagumi Bara'atu tai cike da bacin rai wannan wacce irin masifa ce dan iyayenka basu dashi sai aita goranta maka harda haihuwa cigaba tayi da aikinta Ramatu dake d'aki sai aiko mata da zagi take ta tafar sauke bata ce mata ba.
Sai aikin sharar hawaye kawai take shigowar Ilyah kenan ganin tana kuka yace "ke kuma fa lafiya"?.
Daga d'aki Ramatu tace "dani ne ka saki wannan matsiyaciyar matar taka saina yi maganin ta zatasan wace Ramatu" d'an tsaki Ilyah yaja yana cewa "na saketa kamarya meye kuma ya faru"?.
"Au meye ya faru ma kake tambaya"? Jin yayi shiru yasa ta fitowa ganin ya juya zai fice daga gidan ga kuma ba'kar leda ya aje a kusa da Bara'atun yasa da gudu taje ta dauke har zaninta na neman fad'uwa kasa tace.
"Kai Ilyah zonan so'ko'kon banza so'ko'kon wofi har dan nayi maka magana akan wannan figaggiyar matar taka zaka wani fice ka barni ina 'ba'batu kamar zakar da take 'kwai wannan abun cikin ledar uban me ka sayo mata".
Dakatawa yai batare daya juyo ba yace "kifi ne zatai mana abinci dashi" yana fad'in haka yai waje.
"Kifii🦈🐠" Ramatu ta fad'a harda zaro ido tana bud'e ledar ganin su tayi da yawa kai ta jinjina "ah lallai kam yanzu wannan uban kifi daya sayo da bana nan shikenan saidai kici naci sauran ki tattara ki kaiwa almajiran gyatumin ki ko? To Allah ya tuno asirin ki yau ina nan za'a gama girki sai an zuba min nawa ina kallo dan baza'a ri'ka cuta taba haka kawai nida haihuwa keda morewa".
Ita dai Bara'atu tana shiru batace mata komai ba cikin hararrami Ramatu tace "ke ba dake nake magana ba dan 'kwanjin ubanki nace ki dauko kwano na juye" mi'kewa Bara'atu tai takaici fal ranta taje ta dauko tana kawo mata kad'an ta zuba tana cewa "wannan ya isa abincin wannan kuma nawa ne nan da gobe ina ci a hankali zan cinye kayana dauki kije".
Saida ta bari ta d'auke ta koma gaban murhun tana gyarawa da cire 'kaya saboda soyayye ne farat Ramatu tace "ke Barah tashi anan yau nice zanyi girkin bake ba daga yau bi da bi za munayi" tsananin mamaki ne ya kama Bara'atu har batasan lokacin da tace "bi da bi kuma? Sai kace kishiya ta".
Mi'kewa Ramatu tai daga inda take zaune tare da cewa "au sai kace kishiyar ki? Dan malafar ubanki nice kikewa haka dan darar ubanki shigiya tsinanniya mai siffar angulu zaki ban guri ko saina karya miki kafa kika tsaya ina magana kina kallo na da baka'ken idanu kamar kwallon d'inya ko nayi mike kama da tamilalliyar uwartaki ne me zubin itacen rimi da siraran kafafu kamar na sauro ai indai bala'i ne yanzu kika fara sha a gidan nan dan darar ubanki" ganin zata bangaje ta yasa da sauri Bara'atu ta matsa gefe ta bata gurin.
Zama Ramatu tai tana kallon yadda mai yake yawo a saman abincin tace "humm yo abune ga d'an talaka ba'a saba ba ansha fura an mutu idan ba tsabar ke ba'kar gidahuma bace taya zaki kwarar irin wannan man a cikin abinci sai kinsa mun harbu da ciwon bayamma au wato so kike Ilyasu ya sha mai da yawa ya mutu dan ki samu gado tunda baki haihu ba ko? Tab tirrr da halinki in Allah ya yarda saikin riga Ilyah mutuwa gadon da kike kwad'ayi baza ki samu ba balle har kiyi tunani gyarawa fatararrun iyayen naki ru'babben gidan su".
Ko bari abincin ya dahu Ramatu batai ba ta d'iba tare da zubawa akan kifin data baiwa Bara'atu asa a girki kawai ta koma d'aki tana cewa "na d'ebi rabo na sai kije kiyita cin kasa inda babu mai ba maggi muguwar mace wai ni zata asirce dama ai naji ance har rubutu kandiya take kawo miki kina mana abinci dashi dan ki mallake mu to bari kiji wallahi munfi karfin ki nan gani nan bari d'umamen maiya".
Shiru Bara'atu tai tana kallon kofar d'akin Ramatu kafin ta d'an girgiza kai tana daukar tukunyar tayi taku daya biyu taji sallamar 'kanwarta d'an waigawa tai cikin danne d'aci da takaicin da ta kwasa tace.
"Lawisa kece shigo mana ya kika tsaya anan"?.
Bata karaso ba tace "eh babah ce ta aiko ni wai......................