Sashe 9
Dan Mace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Baba yana kallonsa yace "Akan gida na..?"
Alhaji yace "K'warai kuwa,akan gidanka."
Baba yana binsa da wani irin kallon mamaki da rashin yarda ya sake daurewa yace
"Toh ina jinka.."
Alhaji zakar yana kallon Baba ya fara zayyana masa duk abubuwan dake faruwa a gidansa,da mugun mamakin yadda akayi ya sani Baba yake ta kallonsa,har ya gama magana Baba bai ce masa komai ba,Alhaji zakar yayi shiru yana ta kallon baba yaji ko zai yi magana amma yaji shiru,dole tasa shi tambayar baba
"Malam Baba baka ce komai ba..?"
Baba dai yana kallonsa har lokacin da kyar ya bud'e baki cikin kaushin kalami yace "toh Alhaji me zance.?? Tunda Allah yasa munafukai sun fara sawa gidana ido,har sun fara yawo suna yamad'id'i da ni a gari,da tona asirin gidana.. Zance ya lalace tunda har al'amarin gida na ya shiga gari.."
"A'a Malam Baba kada kace haka,wannan magana sam baka fahimci yadda take ba,,ni dai ka sanni kuma kasan ba mai shiga harkokin da ba'a sani bane,amma tunda kaga na tsayar da kai nayi maka magana kasan ba zai wuce na hango maka damuwa bane a cikin gidanka na sanar da kai. Toh amma tunda har Allah yasa magana ta batai maka ba,Allah ya huci zuciyarka kuma ya baka hak'uri idan har na b'ata maka rai.."
Ajiyar zuciya Baba yayi yace "ai Alhaji wannan batun tunda kazo da shi na san bazai wuce tsaigumi aka kai maka ba,kuma kaima ga shi ka tabbatar min,amma tunda haka abun yake,kafin a fara zagina akan maganar yarinyar nan,dole ne tunda yake nine mahaifinta na zartar da hukuncina akanta ta yadda babu wanda zai sake zuwa min da magana makamanciyar wannan,,zan aurar da ita kowa sai ya huta,da ta d'auko min maganar da zata fi k'arfi na gara na zartar da hukuncin da zan kashe bakin mutane.."
Alhaji yana kallon Baba da mamaki yace "Malam Baba aure kace.?" Baba yace "Haka nace",cikin muryar rarrashi Alhaji zakar yace "kada kayi haka malam Baba,yarinyar nan duka nawa take da zaka ce zaka aurar da ita.? Ko a k'auye yanzun tuni an waye an daina irin wannan auren,bare mu da muke cikin birni,,ya kamata kayi tunani dai kafin ka zartar da hukuncin da zai iya kaika ga yin dana sani a gaba."
"Alhaji ina ganin wannan hukuncin shi ne dai²,tunda har Allah yasa ka fad'i sak'on da ya kawo ka,kana iya tafiya na gode.."
Alhaji yaci gaba da kallon Baba da mamaki "Amma malam Baba ban tab'a tsammanin haka daga gareka ba,wannan al'amari idan har ka tsaya ka nazarce shi da kyau,na tabbata zaka gane gaskiyar da nake son ka fahimta."
"Alhaji maganar fahimta ya k'are,tunda har ka fad'i sak'on daya kawo ka,yanzun naka ido ne,,abunda nake fad'a maka a yanzun shi ne batun auren Hauwa na gama yanke hukunci,in sha Allah cikin satin nan zan d'aura mata aure,da ma hak'k'i na ne na aurar da ita ga wanda yayi min,yadda nayi niyya haka zanyi aure babu fashi.."
Cikin takaici Alhaji zakar yaci gaba da kallon Baba but bai sake ce masa komai ba ya mik'e da niyyar barin gurin tunda al'amarin yafi k'arfinsa,ya yiwa Baba sallama yana niyyar shiga gida,Baba dake zaune har lokacin yana kallonsa cikin d'aga murya kamar wanda aka bawa umarnin yin magana yace
"Yawwa Alhaji ina da wata y'ar maganar nima."
Waiwayowa Alhaji zakar yayi yana kallon Baba duk da yaji haushinsa amma haka nan daga inda yake tsaye yace "fad'i maganarka ina sauraronka."
Shima Baba daga nan inda yake yace "Yawwa! Dama ina so ne na baka cigiya tunda har Allah yasa nace zan aurar da ita,ba tare da samun tsayyaye ba shi ne nake son shaida maka,ko da Allah zai sa ka samu wani mai rangwamen gata kamar ta da yake buk'atar auren,dan Allah ina rok'on alfarma ka sanar masa yazo gida na ina da matar da zan bashi sadaka.."
Cike da takaici Alhaji zakar ya bi Baba da kallon sakarci ba tare da ya ce komai ba ya juya zai shiga gida,baba yaga yayi masa magana bai tanka ba hakan tasa shi sake cewa
"Yawwa Alhaji,,nace tunda yake Allah yasa har kana ganin tayi k'arama da aure yanzun,kuma kai d'in kana da ma'aikata a gidanka,shin mai zai hana ko su ne ka nemawa d'aya daga cikinsu aurenta tunda kana tausayinta tayi k'arama da aure.. Ka ga dama jihadi kake son yi.. Shi ne sai naga zaifi kyau na sanar da kai,sadaki ma kad'ai idan ka biya ya wadatar a d'aura musu aure,daga nan sai ka ajiyeta a gidanka,kaci gaba da kulawa da ita ko itama ka bata aiki a gidan naka,tunda yake ni mahaifinta na yi ba dai² ba.."
Maganar ta yiwa Alhaji zakar zafi,still bai tanka ba ya wuce gida ransa a b'ace har yaji nadamar samun Baba da maganar,shigarsa gida a cikin wannan yanayin suka yi maganar da Hajiya,yadda suka yi duka da baba ya sanar da ita tunda ita ta sashi shiga maganar tun farko,,Hajiya ta lallab'a ta kwantar masa hankali,followed by maganar ta akan me zai hana tunda har Allah yasa al'amarin ya zo da haka kuma Baba da kansa ya bashi damar neman auren yarinyar ga hadiman gidansa,su nunawa masa cewa maganar da yayi cikin izgili a shirye suke su tabbatar da cikarta..??,Alhaji ya zuba mata ido yana kallo cikin rashin fahimta but yayi k'ok'arin yin magana
"Hajiya me kike son cewa..?"
Tace "so nake ka amince da batun neman auren yarinyar."
Yace "Hajiya wane irin batu kike yi haka.? Ni zan nemi auren k'aramar yarinya kamar wannan,sa'ar y'ata fa.?? Ita kike cewa na nemi aurenta..?? Yarinya y'ar shekara sha hud'u.? "
Tace "Alhaji nifa ba kai nake nufi ba."
Yace "to waye zan nemawa aurenta.? Kin san dai bani da ikon zartar da ko wane irin hukunci akan ma'aikatan gidan nan cos bani ke da su ba,mu kuma ba wani babban d'a namiji gare mu ba bayan Rafeek,idan munce shi,duka shekarunsa nawa suke.? Besides yanzun yake shekara ta biyu a jami'a."
Hajiya tace "ni dai alhaji kawai kayi hak'uri da batun shekarunsa,wannan al'amari ne da ya kamata ace munyi iya kar k'ok'arin mu wajen ganin mun taimakawa marainiyar nan,ina tausayin rayuwar yarinyar nan har zuciya ta,kallonta nake kamar Maimunatu na,idan a yanzun da muke da dama bamu taimaka mata ba,mu yaya zamu yi a gaba..?? Kada fa ka manta taimakon maraya abune mai kyau,kamar yadda annabi (S.A.W) yace a hadisi:"Ni da mai taimakon maraya,zamu kasance kamar haka ✌🏻a gidan aljannah,sai ya raba tsakaninsu da wani abu,maleek (R.A) yayi nuni da yatsunsa biyu manuni da na tsakiya,,idan ka duba duka nima bawai ina dagewa bane akan lallai sai munyi hakan zai nuna kulawarmu gare ta ba,sai dan ina ganin yin hakan shi ne zaifi bamu damar taimaka mata ba tare da anyi zarginmu ba,ni ina yi mana kwad'ayin matsayin ne kawai,wannan ne yasa nake sake tunatar da kai,,shin a lokacin da wani namu yake neman taimako mu baza mu nemi taimakon wasu bane..? Ya kamata ka duba maganata da kyau,tamkar jihadi ne zamu yi idan har munyi nasara..!"
Alhaji zakar yayi shiru bai ce komai ba tsayin lokaci yana nazarin maganarta,Hajiya ta sake yin amfani da wannan damar ta dunga kawo masa hujjoji da dalilan da take ganin idan har sun taimaki Hauwa zasu samu lada har gurin Allah,,hankalin hajiya bai kwanta ba,sai data tabbatar Alhaji ya amince zai nemawa Rafeek auren Hauwa.. Wannan shi ne mafarin lamari,ina nufin mafarin matsalolin rayuwar Hauwa da mu kanmu.....
#Share.
#Real Smasher.
💠💠💠💠💠
*©®2020.*
*'DAN MACE..*
(Tʜᴇ ᴘꜱʏᴄʜɪᴀᴛʀɪꜱᴛ)..💥
*WATTPAD:REAL-SMASHER898.*
https://my.w.tt/29u2S26SG2
*The gift u gave me was more than perfect in each and every way..Thank u so much for it Cweet Mammah (Manab). I will always preserve and keep it with me forever.*
Pᴀɢᴇ 5.
#Tᴜʀᴍᴏɪʟ
Bayan Alhaji zakar ya gama yanke hukunci,shawaran samun Baba yayi a washe garin ranar da nufin ya sanar da shi ya amince da maganar,but da nufin nemawa Rafeek auren Hauwa zai je kamar yadda Babanmu ya buk'ata,kamar wancan lokacin suka had'u a k'ofar gida,Alhaji zakar ya rattabawa Baba buk'atarsa,a nan Baba ya fututtuke fuska gani yake kamar cin fuska ya kawo Alhaji zakar,bud'ar bakin Baba a take yace
"Haba Alhaji,,kada ka mai dani wani shawaragi mana,banda kai ko k'aramin yaro na koma ai kasan babu yadda za'ayi na yarda da cewa kamar kai zaka amince ka nemawa dank'a auren y'ar wajena.. Sai dai kuma ban sani ba ko ka zo ne ka zolaye ni kaji an samu wanda ya taya,amma ba kai da kanka kace ka zo nemawa dank'a aurenta ba,,ina laifinma kace mai gadin ka ko y'an aiken gidanka..? Wannan kam ina iya yarda kuma na amincewa da kai."
Alhaji zakar yayi dariya da yake ya san iya gaskiyarsa ya fad'a yace "ko kad'an malam Baba ban zo da nufin na zolaye ka ba,,alal hak'ik'a kamar yadda ka ji na fad'a maka babu batun wasa a magana ta,wannan itace gaskiyar zuciyata kuma ita na fad'a maka,ko ka yarda ko kada ka yarda ni na san ban zo da nufin na yaudare ka ko na cutar da kai ba,kada ka manta tun farko kai ka bani dama kuma naga na yaba da tarbiyyar yarinyar ka,ina da buk'atar amfani da wannan damar daka bani,shi yasa na zo gare ka da batun,idan ka amince kamar yadda ka fad'a ranar jumu'ah idan Allah ya kaimu sai a d'aura auren,dama kace a cikin satin nan ka shirya aurar da ita ko ba haka ba.??"
Baba yace "haka nace,,amma batun kana neman aurenta wa dank'a na fasa,ni da kaina zan nemo wanda ya dace da ita na aura masa."
Alhaji ya sake yin dariya yana kallon Baba daya fututtuke fuska yace "amma malam Baba kasan ba haka muka yi da kai ba tun farko ko.?"
Baba yace "to yaya muka yi..?? Ina ce nina baka dama tun farkon.. Yanzun kuma naga hakan bai minba na canja.!?"
Alhaji yace "K'warai kuwa,akan gidanka."
Baba yana binsa da wani irin kallon mamaki da rashin yarda ya sake daurewa yace
"Toh ina jinka.."
Alhaji zakar yana kallon Baba ya fara zayyana masa duk abubuwan dake faruwa a gidansa,da mugun mamakin yadda akayi ya sani Baba yake ta kallonsa,har ya gama magana Baba bai ce masa komai ba,Alhaji zakar yayi shiru yana ta kallon baba yaji ko zai yi magana amma yaji shiru,dole tasa shi tambayar baba
"Malam Baba baka ce komai ba..?"
Baba dai yana kallonsa har lokacin da kyar ya bud'e baki cikin kaushin kalami yace "toh Alhaji me zance.?? Tunda Allah yasa munafukai sun fara sawa gidana ido,har sun fara yawo suna yamad'id'i da ni a gari,da tona asirin gidana.. Zance ya lalace tunda har al'amarin gida na ya shiga gari.."
"A'a Malam Baba kada kace haka,wannan magana sam baka fahimci yadda take ba,,ni dai ka sanni kuma kasan ba mai shiga harkokin da ba'a sani bane,amma tunda kaga na tsayar da kai nayi maka magana kasan ba zai wuce na hango maka damuwa bane a cikin gidanka na sanar da kai. Toh amma tunda har Allah yasa magana ta batai maka ba,Allah ya huci zuciyarka kuma ya baka hak'uri idan har na b'ata maka rai.."
Ajiyar zuciya Baba yayi yace "ai Alhaji wannan batun tunda kazo da shi na san bazai wuce tsaigumi aka kai maka ba,kuma kaima ga shi ka tabbatar min,amma tunda haka abun yake,kafin a fara zagina akan maganar yarinyar nan,dole ne tunda yake nine mahaifinta na zartar da hukuncina akanta ta yadda babu wanda zai sake zuwa min da magana makamanciyar wannan,,zan aurar da ita kowa sai ya huta,da ta d'auko min maganar da zata fi k'arfi na gara na zartar da hukuncin da zan kashe bakin mutane.."
Alhaji yana kallon Baba da mamaki yace "Malam Baba aure kace.?" Baba yace "Haka nace",cikin muryar rarrashi Alhaji zakar yace "kada kayi haka malam Baba,yarinyar nan duka nawa take da zaka ce zaka aurar da ita.? Ko a k'auye yanzun tuni an waye an daina irin wannan auren,bare mu da muke cikin birni,,ya kamata kayi tunani dai kafin ka zartar da hukuncin da zai iya kaika ga yin dana sani a gaba."
"Alhaji ina ganin wannan hukuncin shi ne dai²,tunda har Allah yasa ka fad'i sak'on da ya kawo ka,kana iya tafiya na gode.."
Alhaji yaci gaba da kallon Baba da mamaki "Amma malam Baba ban tab'a tsammanin haka daga gareka ba,wannan al'amari idan har ka tsaya ka nazarce shi da kyau,na tabbata zaka gane gaskiyar da nake son ka fahimta."
"Alhaji maganar fahimta ya k'are,tunda har ka fad'i sak'on daya kawo ka,yanzun naka ido ne,,abunda nake fad'a maka a yanzun shi ne batun auren Hauwa na gama yanke hukunci,in sha Allah cikin satin nan zan d'aura mata aure,da ma hak'k'i na ne na aurar da ita ga wanda yayi min,yadda nayi niyya haka zanyi aure babu fashi.."
Cikin takaici Alhaji zakar yaci gaba da kallon Baba but bai sake ce masa komai ba ya mik'e da niyyar barin gurin tunda al'amarin yafi k'arfinsa,ya yiwa Baba sallama yana niyyar shiga gida,Baba dake zaune har lokacin yana kallonsa cikin d'aga murya kamar wanda aka bawa umarnin yin magana yace
"Yawwa Alhaji ina da wata y'ar maganar nima."
Waiwayowa Alhaji zakar yayi yana kallon Baba duk da yaji haushinsa amma haka nan daga inda yake tsaye yace "fad'i maganarka ina sauraronka."
Shima Baba daga nan inda yake yace "Yawwa! Dama ina so ne na baka cigiya tunda har Allah yasa nace zan aurar da ita,ba tare da samun tsayyaye ba shi ne nake son shaida maka,ko da Allah zai sa ka samu wani mai rangwamen gata kamar ta da yake buk'atar auren,dan Allah ina rok'on alfarma ka sanar masa yazo gida na ina da matar da zan bashi sadaka.."
Cike da takaici Alhaji zakar ya bi Baba da kallon sakarci ba tare da ya ce komai ba ya juya zai shiga gida,baba yaga yayi masa magana bai tanka ba hakan tasa shi sake cewa
"Yawwa Alhaji,,nace tunda yake Allah yasa har kana ganin tayi k'arama da aure yanzun,kuma kai d'in kana da ma'aikata a gidanka,shin mai zai hana ko su ne ka nemawa d'aya daga cikinsu aurenta tunda kana tausayinta tayi k'arama da aure.. Ka ga dama jihadi kake son yi.. Shi ne sai naga zaifi kyau na sanar da kai,sadaki ma kad'ai idan ka biya ya wadatar a d'aura musu aure,daga nan sai ka ajiyeta a gidanka,kaci gaba da kulawa da ita ko itama ka bata aiki a gidan naka,tunda yake ni mahaifinta na yi ba dai² ba.."
Maganar ta yiwa Alhaji zakar zafi,still bai tanka ba ya wuce gida ransa a b'ace har yaji nadamar samun Baba da maganar,shigarsa gida a cikin wannan yanayin suka yi maganar da Hajiya,yadda suka yi duka da baba ya sanar da ita tunda ita ta sashi shiga maganar tun farko,,Hajiya ta lallab'a ta kwantar masa hankali,followed by maganar ta akan me zai hana tunda har Allah yasa al'amarin ya zo da haka kuma Baba da kansa ya bashi damar neman auren yarinyar ga hadiman gidansa,su nunawa masa cewa maganar da yayi cikin izgili a shirye suke su tabbatar da cikarta..??,Alhaji ya zuba mata ido yana kallo cikin rashin fahimta but yayi k'ok'arin yin magana
"Hajiya me kike son cewa..?"
Tace "so nake ka amince da batun neman auren yarinyar."
Yace "Hajiya wane irin batu kike yi haka.? Ni zan nemi auren k'aramar yarinya kamar wannan,sa'ar y'ata fa.?? Ita kike cewa na nemi aurenta..?? Yarinya y'ar shekara sha hud'u.? "
Tace "Alhaji nifa ba kai nake nufi ba."
Yace "to waye zan nemawa aurenta.? Kin san dai bani da ikon zartar da ko wane irin hukunci akan ma'aikatan gidan nan cos bani ke da su ba,mu kuma ba wani babban d'a namiji gare mu ba bayan Rafeek,idan munce shi,duka shekarunsa nawa suke.? Besides yanzun yake shekara ta biyu a jami'a."
Hajiya tace "ni dai alhaji kawai kayi hak'uri da batun shekarunsa,wannan al'amari ne da ya kamata ace munyi iya kar k'ok'arin mu wajen ganin mun taimakawa marainiyar nan,ina tausayin rayuwar yarinyar nan har zuciya ta,kallonta nake kamar Maimunatu na,idan a yanzun da muke da dama bamu taimaka mata ba,mu yaya zamu yi a gaba..?? Kada fa ka manta taimakon maraya abune mai kyau,kamar yadda annabi (S.A.W) yace a hadisi:"Ni da mai taimakon maraya,zamu kasance kamar haka ✌🏻a gidan aljannah,sai ya raba tsakaninsu da wani abu,maleek (R.A) yayi nuni da yatsunsa biyu manuni da na tsakiya,,idan ka duba duka nima bawai ina dagewa bane akan lallai sai munyi hakan zai nuna kulawarmu gare ta ba,sai dan ina ganin yin hakan shi ne zaifi bamu damar taimaka mata ba tare da anyi zarginmu ba,ni ina yi mana kwad'ayin matsayin ne kawai,wannan ne yasa nake sake tunatar da kai,,shin a lokacin da wani namu yake neman taimako mu baza mu nemi taimakon wasu bane..? Ya kamata ka duba maganata da kyau,tamkar jihadi ne zamu yi idan har munyi nasara..!"
Alhaji zakar yayi shiru bai ce komai ba tsayin lokaci yana nazarin maganarta,Hajiya ta sake yin amfani da wannan damar ta dunga kawo masa hujjoji da dalilan da take ganin idan har sun taimaki Hauwa zasu samu lada har gurin Allah,,hankalin hajiya bai kwanta ba,sai data tabbatar Alhaji ya amince zai nemawa Rafeek auren Hauwa.. Wannan shi ne mafarin lamari,ina nufin mafarin matsalolin rayuwar Hauwa da mu kanmu.....
#Share.
#Real Smasher.
💠💠💠💠💠
*©®2020.*
*'DAN MACE..*
(Tʜᴇ ᴘꜱʏᴄʜɪᴀᴛʀɪꜱᴛ)..💥
*WATTPAD:REAL-SMASHER898.*
https://my.w.tt/29u2S26SG2
*The gift u gave me was more than perfect in each and every way..Thank u so much for it Cweet Mammah (Manab). I will always preserve and keep it with me forever.*
Pᴀɢᴇ 5.
#Tᴜʀᴍᴏɪʟ
Bayan Alhaji zakar ya gama yanke hukunci,shawaran samun Baba yayi a washe garin ranar da nufin ya sanar da shi ya amince da maganar,but da nufin nemawa Rafeek auren Hauwa zai je kamar yadda Babanmu ya buk'ata,kamar wancan lokacin suka had'u a k'ofar gida,Alhaji zakar ya rattabawa Baba buk'atarsa,a nan Baba ya fututtuke fuska gani yake kamar cin fuska ya kawo Alhaji zakar,bud'ar bakin Baba a take yace
"Haba Alhaji,,kada ka mai dani wani shawaragi mana,banda kai ko k'aramin yaro na koma ai kasan babu yadda za'ayi na yarda da cewa kamar kai zaka amince ka nemawa dank'a auren y'ar wajena.. Sai dai kuma ban sani ba ko ka zo ne ka zolaye ni kaji an samu wanda ya taya,amma ba kai da kanka kace ka zo nemawa dank'a aurenta ba,,ina laifinma kace mai gadin ka ko y'an aiken gidanka..? Wannan kam ina iya yarda kuma na amincewa da kai."
Alhaji zakar yayi dariya da yake ya san iya gaskiyarsa ya fad'a yace "ko kad'an malam Baba ban zo da nufin na zolaye ka ba,,alal hak'ik'a kamar yadda ka ji na fad'a maka babu batun wasa a magana ta,wannan itace gaskiyar zuciyata kuma ita na fad'a maka,ko ka yarda ko kada ka yarda ni na san ban zo da nufin na yaudare ka ko na cutar da kai ba,kada ka manta tun farko kai ka bani dama kuma naga na yaba da tarbiyyar yarinyar ka,ina da buk'atar amfani da wannan damar daka bani,shi yasa na zo gare ka da batun,idan ka amince kamar yadda ka fad'a ranar jumu'ah idan Allah ya kaimu sai a d'aura auren,dama kace a cikin satin nan ka shirya aurar da ita ko ba haka ba.??"
Baba yace "haka nace,,amma batun kana neman aurenta wa dank'a na fasa,ni da kaina zan nemo wanda ya dace da ita na aura masa."
Alhaji ya sake yin dariya yana kallon Baba daya fututtuke fuska yace "amma malam Baba kasan ba haka muka yi da kai ba tun farko ko.?"
Baba yace "to yaya muka yi..?? Ina ce nina baka dama tun farkon.. Yanzun kuma naga hakan bai minba na canja.!?"