Sashe 23
Dan Mace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Na girgiza kai" yace "Daga yau na haramta miki zama ahalinta,na raba ku rabuwa ta har abada,idan ta sake zuwa ta aika a kira ki,kika kuskura kika tsaya magana da ita Allah ya isa ban yafe miki ba,kuma wollahi thumma billahi,kinji rantsuwa ko.!?" Na girgiza kai da sauri cikin tsoro yace "Sai kin bar min gidana,daga ranar ina so ki d'auka ni ba mahaifinki bane,tunda kin zama mara jin maganata"
Ina kuka ina kallon Hauwa da tausayawa,baba ya wuce ya barmu tsaye a nan kamar wad'anda aka sassak'a,kusan zan iya cewa gara ni na samu hawaye sun zubo min,amma ita Hauwa tunda ta kafe a nan Allah kad'ai ya barwa kansa sanin abunda ya faru da ita,tana raye,suma ta yi ko ta mutu Allah shi ne masani,,bayan tafiyar Babah da jimawa yayi tunanin ya aiko yaro ya duba masa na shiga gida ko ina nan,yaro yazo ya koma ya fad'a masa ban tafi ba,sai ganin Baba nayi ya dawo da kansa cikin fushi,ina ganinsa na matso da sauri ina kuka zanyi magana tun kafin na bud'e baki cikin fad'a kamar zai dake ni ya korani gida,ina tafiya ina waiwayen y'ar uwata kamar ba zan tafi ba haka har na shiga gida,baba ya koma kan Hauwa da fad'a ta inda ya shiga ba ta nan yake fita ba,sai daya tabbatar ko zuwa unguwar ba lallai ne ta sake yi ba,sannan ya juya ya barta,,cikin tsananin tashin hankali bayan dogon lokacin da ta d'auka cikin halin da bata san a wace duniyar take ba ta ja k'afafunta da kyar ta shiga shop d'in dake a nan line mu ta siya Biro da takarda,doguwar wasik'a ta rubuto min mai d'auke da duk wani abu daya faru da ita a zaman da tayi da Rafeek da ahalinsa,a k'arshe ta rok'i alfarmar na nema mata yafiyar Baba,,bayan ta tabbatar sak'onta ya iso gare ni ta juya ta bar unguwar zuciyarta cike da k'unci.
Ina cikin gida bak'in cikin abunda ya faru ya same ni,d'an sak'on data aiko ya kawo min wasik'a,na warware bayan na keb'e kaina na fara karantawa,tun ban yi nisa karantawa ba hawaye sun wanke min fuska,na daure na karanta,lokacin da Baba ya dawo na je masa da wasik'a,dana fad'a masa duk abunda yake faruwa ya nuna bai yarda ba,na karanta masa takardar da ta aiko min.
Baba ya kalle ni ya jinjina kai yace "Na ji wannan tatsuniyar,,sai dai abunda nake so ki gane Maryam ni ban amince haka ta faru ba,kuma ko na ce na yarda shin zancen ya wuce ko.?"
Na girgiza kai nace "Ehh.! Baba"
Ya kalle ni yace "To ban yarda ba.."
Na d'aga kaina nace "Saboda me ba zaka yarda ba Baba.!? Kai nefa ka haifemu dukan mu,ka san halin kowa a cikin mu,duk abunda za mu iya aikatawa ka san shi haka ma wanda ba za mu iya ba"
Baba yayi min kallon banza yace "Idan na yarda shin sauran mutanen gari za su yarda.!? Ko kuwa su d'inma za ki bisu da takarda ki karanta musu ne.!?"
Na girgiza kai cike da bak'in ciki,baba yace "Though tunda kin san da haka,ko da wasa kada ki sake nufo ni da irin wannan shirmen,na riga na yi muku shamaki da juna,idan har kin d'auke ni mahaifi ki bi maganata,idan kuma y'ar uwarki kike son bi,k'ofa a bud'e take dan na cire y'ay'a biyu daga cikin ahalina ba abune da zai tada min hankali ba,zab'i ya rage naki ni ko ita.!"
Nayi shiru ban iya cewa komai ba,Baba yace "Za ki iya tafiya idan maganar da ta kawo ki kenan" jiki a sanyaye na juya ina ci gaba da kukan zuci har na koma d'aki,babban abunda yafi damuna ya tayarmin da hankali a lokacin ba komai bane,illa rashin sanin address na inda Hauwa take,tunda ta kama hanya ta tafi kuma ko a labari banji wani mutum d'aya da ya zo yace ya san inda take ba,a haka kwanaki suka yita zuwa suna wucewa ba tare da na samu wani gamsashen labarin inda kuka nufa ba,,na ci gaba da rayuwa a gida amma fa tamkar mutum-mutumi na zamewa y'an gidanmu,idan aka yi min magana daga Umm sai um'um,na daina shiga maganar kowa,idan hayaniyar su ta tashi can suke yin abunsu su kad'ai,,kullum cikin jiran tsammani da tunani nake naji ko da wucewarta ne wani ya zo yace min ya gani,amma shiru tamkar an shuka dusa har muka cinye sama da sati biyu.
3 Month later...
Laying and rising is loss of living,haka nan a gurin ubangiji a year is like a day,cikin hukuncin ubangiji tun daga wannan tafiyar da Hauwa tayi sai ya zama bata sake tunanin waiwayar gida ba saboda abunda ya faru tsakaninta da Baba,bayan tafiyarta babu jimawa damuwa tayi mata yawa,har ya zama ciwo ya fara k'ok'arin kayar da ita,tun tana yi a tsaitsaye taba jurewa har lamarin ya so fin k'arfinta,damuwa da fargabar abunda zai iya faruwa da rayuwarta yak'i barin zuciyarta ta samu nutsuwar sake dawowa,ta ga al'amarin still ba mai k'arewa bane,duk da tsoron dake tare da ita ta sake yanke shawaran dawowa ko da zai kasance skasance wannan shi ne zuwanta na k'arshe,but ta gwammace zuwan da ace ciwo ya yi ajalinta ita kad'ai a gurin da babu wani cikin ahalinta,cikin y'an watannin ta yi wani irin ramewa ta yi duhu kamar ba ita ba,duk wanda ya santa idan ya ganta a wannan tak'aitaccen lokacin na tabbata zai yi wahala lokaci d'aya yayi saurin ganeta,ta kamo hanyar K'ofar Na'isa a karo na biyu cike da fargaba,but data tashi zuwa wannan lokacin sai bata yi k'ok'arin shiga gida ba ko nema na,ta sake aiko min wasik'a,ina zaune cikin d'aki jigum sak'on ta ya riske ni,na karanta naga fiye da rabin maganarta akan na nema mata yafiya ne a gurin Baba,sai sauran mutanen da nasan wani mu'amala ya tab'a had'a su,ina kuka ina karamtawa har na zo inda take barmin wasiyya tana sanar min ta jima ba ta da lafiya na taimaketa na nema mata alfarma gurin Baba na zo na ganta ko da sau d'aya ne kafin ta Allah ta kasance mata,a wannan wasik'ar nayi gamo da tsananin tashin hankalin da ya wuce tunani na
_"Kiyi hak'uri y'ar uwata.! Babu yadda zanyi,ya zame min wajibi na sanar miki,duk da na san kema ba laifinki bane da kika kasa zuwa inda muke,,a halin da nake ciki,bayan dawiwa ta ciwo ya ci k'arfina,ina jin kamar ba zan rayu ba,idan haka ya kasance ina rok'on za ki nema min alfarma a gurin Baba,idan ya barki ko da a shek'ara sau d'aya ne zan yi alfahari da hakan,kema ina fatan za ki je ki duba min yarona,ban san yadda rayuwa ta zata kasance ba,shi yasa na yanke shawaran sanar da ke tun yanzun,zan kai Nuraz orphanage,idan kin samu dama dan Allah Yaya ina rok'on ki kije ki ganshi,na san Yarona ba zai yi maraici ba idan kina raye,na san yana da wata mahaifiyar kamar ki kuma za ki kula da shi fiye da yadda zanyi masa,ni dai tawa ta zo k'arshe sai dai ina yi mana fatan mu kasance tare har a aljannah,idan na yi miki wani laifi ina neman afuwar tun daga yarinta har zuwa girma na,ki yafe min y'ar uwata... Allah ya k'addara saduwarmu.. BISSALAAM.!"_
Daga k'anwar ki mai k'aunar k'i har abada *HAUWA BABA MUHAMMAD...*
Tsananin firgici da tsoro na shiga lokacin dana gama karanta sak'on ta,ba tare da na jira neman izinin fita a gurin Baba ba na fito daga gida kamar zararriya nabi hanya ko zan ganta,ina tafiya ina tambayar mutanen unguwa ko sun ganta.!? Sai ace min yanzun babu jimawa ta wuce,da sauri nake wucewa na bar wajen na yi gaba,ina tafe ina sake tambaya,amma abun takaici har na fito titi na gama dubawa ko mai kama da ita ban samu ba,na koma gida cikin firgici na tarar Baba ya dawo,ina kuka na sake zuwa gurinsa da wasik'a ko zai tausaya min ya bari naje,still Baba ya sawa idanunsa toka kamar waccan ranar,ya nuna min sam baya ko son yin maganar,dana takura akan ya barni naje yace idan na sake na fita bada izinin sa ba Allah ya isa bai yafe min ba.
Tsoro da tashin hankali suka sake shigata,rashin sanin matsayin Allah ya isa da Baba yayi min,da tsoron halin da y'ar uwata take ciki suka sa na kasa ko magana,ina ji ina gani ga address d'in inda take amma zuwa na dubata ya gagare ni,ban san mene ne zai faru ba idan na fita ba da izininsa Bana ba,sannan mene ne makomata idan na sab'awa umarninsa,,sati guda da zuwanta kullum da ciwon kai nake yini saboda damuwa ga yawan mafarkai da nake yi marasa dad'i,zuciyata kullum cikin yi min khud'ubar naje na duba ku take,na daure na ci gaba da zama ina jiran tsammani,,a cikin satin wani abu daya faru ya sake sawa jiki na yayi sanyi,ko wane lokaci na kwanta bacci da rana ko dare mafarkin Hauwa nake yi,a ko wane lokaci da zan ganta tana kuka tana sake rok'ona kada na manta da kai na kula mata da kai,,kwana biyu tsakani na sake yin mafarki da Innarmu,tun bayan rasuwarta da nayi ta mafarkai da ita,na jima sosai ban sake ganinta ba,ranar na kwanta bacci kenan tazo min cikin wani irin fuska mai ban tsoro,ina murna na nufi inda take zaune da niyyar na rik'e ta sai na ga ta yi tafiyarta,na dunga binta ina rok'on ta tsaya amma bata sake waiwayowa ba,sai dana gaji na fad'i a k'asa,ina kuka ina kiranta da rok'on ta tsaya,sannan naga ta juyo tana kallona tana kuka,hankali na a tashe nace "Inna mene ne ya saki kuka.??" Bud'ar bakinta tace "Ban san haka za kuyi min ba Maryam.. Ke da mahaifinki kun tozarta ni,kun wulakanta ni.. Laifin me nayi muku haka.!?"
Nace "Inna laifin me muka yi miki ne.!? Ban gane abunda kike magana ba.!"
Ina kuka ina kallon Hauwa da tausayawa,baba ya wuce ya barmu tsaye a nan kamar wad'anda aka sassak'a,kusan zan iya cewa gara ni na samu hawaye sun zubo min,amma ita Hauwa tunda ta kafe a nan Allah kad'ai ya barwa kansa sanin abunda ya faru da ita,tana raye,suma ta yi ko ta mutu Allah shi ne masani,,bayan tafiyar Babah da jimawa yayi tunanin ya aiko yaro ya duba masa na shiga gida ko ina nan,yaro yazo ya koma ya fad'a masa ban tafi ba,sai ganin Baba nayi ya dawo da kansa cikin fushi,ina ganinsa na matso da sauri ina kuka zanyi magana tun kafin na bud'e baki cikin fad'a kamar zai dake ni ya korani gida,ina tafiya ina waiwayen y'ar uwata kamar ba zan tafi ba haka har na shiga gida,baba ya koma kan Hauwa da fad'a ta inda ya shiga ba ta nan yake fita ba,sai daya tabbatar ko zuwa unguwar ba lallai ne ta sake yi ba,sannan ya juya ya barta,,cikin tsananin tashin hankali bayan dogon lokacin da ta d'auka cikin halin da bata san a wace duniyar take ba ta ja k'afafunta da kyar ta shiga shop d'in dake a nan line mu ta siya Biro da takarda,doguwar wasik'a ta rubuto min mai d'auke da duk wani abu daya faru da ita a zaman da tayi da Rafeek da ahalinsa,a k'arshe ta rok'i alfarmar na nema mata yafiyar Baba,,bayan ta tabbatar sak'onta ya iso gare ni ta juya ta bar unguwar zuciyarta cike da k'unci.
Ina cikin gida bak'in cikin abunda ya faru ya same ni,d'an sak'on data aiko ya kawo min wasik'a,na warware bayan na keb'e kaina na fara karantawa,tun ban yi nisa karantawa ba hawaye sun wanke min fuska,na daure na karanta,lokacin da Baba ya dawo na je masa da wasik'a,dana fad'a masa duk abunda yake faruwa ya nuna bai yarda ba,na karanta masa takardar da ta aiko min.
Baba ya kalle ni ya jinjina kai yace "Na ji wannan tatsuniyar,,sai dai abunda nake so ki gane Maryam ni ban amince haka ta faru ba,kuma ko na ce na yarda shin zancen ya wuce ko.?"
Na girgiza kai nace "Ehh.! Baba"
Ya kalle ni yace "To ban yarda ba.."
Na d'aga kaina nace "Saboda me ba zaka yarda ba Baba.!? Kai nefa ka haifemu dukan mu,ka san halin kowa a cikin mu,duk abunda za mu iya aikatawa ka san shi haka ma wanda ba za mu iya ba"
Baba yayi min kallon banza yace "Idan na yarda shin sauran mutanen gari za su yarda.!? Ko kuwa su d'inma za ki bisu da takarda ki karanta musu ne.!?"
Na girgiza kai cike da bak'in ciki,baba yace "Though tunda kin san da haka,ko da wasa kada ki sake nufo ni da irin wannan shirmen,na riga na yi muku shamaki da juna,idan har kin d'auke ni mahaifi ki bi maganata,idan kuma y'ar uwarki kike son bi,k'ofa a bud'e take dan na cire y'ay'a biyu daga cikin ahalina ba abune da zai tada min hankali ba,zab'i ya rage naki ni ko ita.!"
Nayi shiru ban iya cewa komai ba,Baba yace "Za ki iya tafiya idan maganar da ta kawo ki kenan" jiki a sanyaye na juya ina ci gaba da kukan zuci har na koma d'aki,babban abunda yafi damuna ya tayarmin da hankali a lokacin ba komai bane,illa rashin sanin address na inda Hauwa take,tunda ta kama hanya ta tafi kuma ko a labari banji wani mutum d'aya da ya zo yace ya san inda take ba,a haka kwanaki suka yita zuwa suna wucewa ba tare da na samu wani gamsashen labarin inda kuka nufa ba,,na ci gaba da rayuwa a gida amma fa tamkar mutum-mutumi na zamewa y'an gidanmu,idan aka yi min magana daga Umm sai um'um,na daina shiga maganar kowa,idan hayaniyar su ta tashi can suke yin abunsu su kad'ai,,kullum cikin jiran tsammani da tunani nake naji ko da wucewarta ne wani ya zo yace min ya gani,amma shiru tamkar an shuka dusa har muka cinye sama da sati biyu.
3 Month later...
Laying and rising is loss of living,haka nan a gurin ubangiji a year is like a day,cikin hukuncin ubangiji tun daga wannan tafiyar da Hauwa tayi sai ya zama bata sake tunanin waiwayar gida ba saboda abunda ya faru tsakaninta da Baba,bayan tafiyarta babu jimawa damuwa tayi mata yawa,har ya zama ciwo ya fara k'ok'arin kayar da ita,tun tana yi a tsaitsaye taba jurewa har lamarin ya so fin k'arfinta,damuwa da fargabar abunda zai iya faruwa da rayuwarta yak'i barin zuciyarta ta samu nutsuwar sake dawowa,ta ga al'amarin still ba mai k'arewa bane,duk da tsoron dake tare da ita ta sake yanke shawaran dawowa ko da zai kasance skasance wannan shi ne zuwanta na k'arshe,but ta gwammace zuwan da ace ciwo ya yi ajalinta ita kad'ai a gurin da babu wani cikin ahalinta,cikin y'an watannin ta yi wani irin ramewa ta yi duhu kamar ba ita ba,duk wanda ya santa idan ya ganta a wannan tak'aitaccen lokacin na tabbata zai yi wahala lokaci d'aya yayi saurin ganeta,ta kamo hanyar K'ofar Na'isa a karo na biyu cike da fargaba,but data tashi zuwa wannan lokacin sai bata yi k'ok'arin shiga gida ba ko nema na,ta sake aiko min wasik'a,ina zaune cikin d'aki jigum sak'on ta ya riske ni,na karanta naga fiye da rabin maganarta akan na nema mata yafiya ne a gurin Baba,sai sauran mutanen da nasan wani mu'amala ya tab'a had'a su,ina kuka ina karamtawa har na zo inda take barmin wasiyya tana sanar min ta jima ba ta da lafiya na taimaketa na nema mata alfarma gurin Baba na zo na ganta ko da sau d'aya ne kafin ta Allah ta kasance mata,a wannan wasik'ar nayi gamo da tsananin tashin hankalin da ya wuce tunani na
_"Kiyi hak'uri y'ar uwata.! Babu yadda zanyi,ya zame min wajibi na sanar miki,duk da na san kema ba laifinki bane da kika kasa zuwa inda muke,,a halin da nake ciki,bayan dawiwa ta ciwo ya ci k'arfina,ina jin kamar ba zan rayu ba,idan haka ya kasance ina rok'on za ki nema min alfarma a gurin Baba,idan ya barki ko da a shek'ara sau d'aya ne zan yi alfahari da hakan,kema ina fatan za ki je ki duba min yarona,ban san yadda rayuwa ta zata kasance ba,shi yasa na yanke shawaran sanar da ke tun yanzun,zan kai Nuraz orphanage,idan kin samu dama dan Allah Yaya ina rok'on ki kije ki ganshi,na san Yarona ba zai yi maraici ba idan kina raye,na san yana da wata mahaifiyar kamar ki kuma za ki kula da shi fiye da yadda zanyi masa,ni dai tawa ta zo k'arshe sai dai ina yi mana fatan mu kasance tare har a aljannah,idan na yi miki wani laifi ina neman afuwar tun daga yarinta har zuwa girma na,ki yafe min y'ar uwata... Allah ya k'addara saduwarmu.. BISSALAAM.!"_
Daga k'anwar ki mai k'aunar k'i har abada *HAUWA BABA MUHAMMAD...*
Tsananin firgici da tsoro na shiga lokacin dana gama karanta sak'on ta,ba tare da na jira neman izinin fita a gurin Baba ba na fito daga gida kamar zararriya nabi hanya ko zan ganta,ina tafiya ina tambayar mutanen unguwa ko sun ganta.!? Sai ace min yanzun babu jimawa ta wuce,da sauri nake wucewa na bar wajen na yi gaba,ina tafe ina sake tambaya,amma abun takaici har na fito titi na gama dubawa ko mai kama da ita ban samu ba,na koma gida cikin firgici na tarar Baba ya dawo,ina kuka na sake zuwa gurinsa da wasik'a ko zai tausaya min ya bari naje,still Baba ya sawa idanunsa toka kamar waccan ranar,ya nuna min sam baya ko son yin maganar,dana takura akan ya barni naje yace idan na sake na fita bada izinin sa ba Allah ya isa bai yafe min ba.
Tsoro da tashin hankali suka sake shigata,rashin sanin matsayin Allah ya isa da Baba yayi min,da tsoron halin da y'ar uwata take ciki suka sa na kasa ko magana,ina ji ina gani ga address d'in inda take amma zuwa na dubata ya gagare ni,ban san mene ne zai faru ba idan na fita ba da izininsa Bana ba,sannan mene ne makomata idan na sab'awa umarninsa,,sati guda da zuwanta kullum da ciwon kai nake yini saboda damuwa ga yawan mafarkai da nake yi marasa dad'i,zuciyata kullum cikin yi min khud'ubar naje na duba ku take,na daure na ci gaba da zama ina jiran tsammani,,a cikin satin wani abu daya faru ya sake sawa jiki na yayi sanyi,ko wane lokaci na kwanta bacci da rana ko dare mafarkin Hauwa nake yi,a ko wane lokaci da zan ganta tana kuka tana sake rok'ona kada na manta da kai na kula mata da kai,,kwana biyu tsakani na sake yin mafarki da Innarmu,tun bayan rasuwarta da nayi ta mafarkai da ita,na jima sosai ban sake ganinta ba,ranar na kwanta bacci kenan tazo min cikin wani irin fuska mai ban tsoro,ina murna na nufi inda take zaune da niyyar na rik'e ta sai na ga ta yi tafiyarta,na dunga binta ina rok'on ta tsaya amma bata sake waiwayowa ba,sai dana gaji na fad'i a k'asa,ina kuka ina kiranta da rok'on ta tsaya,sannan naga ta juyo tana kallona tana kuka,hankali na a tashe nace "Inna mene ne ya saki kuka.??" Bud'ar bakinta tace "Ban san haka za kuyi min ba Maryam.. Ke da mahaifinki kun tozarta ni,kun wulakanta ni.. Laifin me nayi muku haka.!?"
Nace "Inna laifin me muka yi miki ne.!? Ban gane abunda kike magana ba.!"