Sashe 10
Dan Mace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Alhaji yace "haka ne kai ka bada dama,nima da naga ina buk'ata nazo da k'ok'on barata,kayi hak'uri ka yarda,kaga zumuncinmu ya sake k'arfi ko ba haka ba.?"
Baba dai yaga kamar Alhaji zakar na neman maida lamarin wasa duk da shi har zuciyarsa yake maganar,tsam ya tashi ya bar masa gurin ba tare da ya samu damar ce masa komai ba,Alhaji har lokacin yana dariya saboda yadda Baba yayi fushi akan y'ar maganar shima ya tashi ya bar wajen,sai dai wannan karon ko daya tashi maimakon ya shiga gida,kai tsaye ya nufi gidan mai unguwa dan yafi son ace manyan unguwa su shiga cikin lamarin yarinyar ko da Baba ba zai bawa Rafeek aurenta kamar yadda ya fad'a ba,yana so aja hankalinsa ya fasa aurar da ita a wannan lokacin,,anyi sa'a Alhaji ya samu mai unguwa a gida,suka yi magana ta fahimta,ba'a d'auki lokaci mai tsayi ba mai unguwa ya aika d'an sak'o ya kira masa Baba,yaje aka sake maimaita zancen kamar yadda tun farko suka yi tsakaninsu shi da Alhaji zakar a gaban mai unguwa da y'an majalisar mai unguwa,jama'a suka shaida yadda akayi,mai unguwa ya bawa Baba hak'uri akan ya janye batun aurar da Hauwa a matsayinta na karamar yarinya saboda matsalolin da ake fuskanta game da aurar da k'ananun yara,sai dai fa Baba ya kafe yace shi bai ga dalilin da zai sa ya canja ra'ayi ba,duk yadda za'ayi anyi akan ya sakko amma ya kafe kamar lalataccen k'arfe,bisa dole mai unguwa da sauran yan majalisarsa suka hak'ura suka kyale shi bcos y'arsa ce kuma shi yake da iko da abarsa,yana da damar yayi duk abunda yaga yayi masa dai²,a nan ko da suka ga an ciza an busa bai amince ba Alhaji zakar ya sake gabato da buk'atarsa ta son amincewar Baba da batun nemawa Rafeek auren Hauwa'r idan ya amince,Baba yaga da gaske Alhaji zakar yake babu batun wasa,nan take ya amince,mai unguwa suka shiga cikin maganar aka tsaida ranar jumu'ah ta zama ranar d'aurin auren Hauwa da Rafeek.
Anyi addu'o'i na neman sanyawar albarka kafin daga nan taron ya tashi,magulmata kuma suka samu na yi,aka tafi aka fara yad'a cewar Baba ya ga kud'i shi yasa ya amince ya bada y'arsa ga d'an Alhaji zakar ba tare da tunanin abunda zai faru gaba ba,,cikin k'ank'anin lokaci gari ya d'auka,duk inda ka zaga maganar auren ake,lungu da sak'o duk inda mutum baya tunani taje har ta wuce,,ranar jumu'ah bayan an sakko daga masallaci aka d'aura auren *Rafeek Zakar Labbo* da amaryarsa *Hauwa Baba Muhammad*,abisa mafi ingancin sadaki,d'aurin auren daya samu halartar manyan mutane daga b'angaren Alhaji zakar da Baba cikin har da manyan y'an siyasa na k'asa daya shiga ya fita ya gayyato duk da yake bai jima da fad'awa harkar bin y'an siyasar ba (kuji fa baba da k'arfin hali,mutumin da bai da wadataccen matsuguni shi ne ya fad'a siyasa).
A dai² lokacin da ake ta hidimar d'aurin aure,a b'angaren ango babu wanda ya sanar da shi badak'alar da ake a gidansu,bcos baya garin yana Zaria da yake a can yake karatu (A.B.U),kuma lokacin bai jima da komawa ba,wannan dalilin yasa Alhaji yace kada a sanar masa shi da kansa zai masa bayanin komai idan an gama hidimar,da yake ma duka ba a lokacin zasu tare ba,yafi so sai Hauwa sun kammala secondary zuwa lokacin ta k'ara girma sai ayi biki,shima Rafeek zuwa lokacin ya kammala degree d'insa na farko,akan haka Alhaji zakar ya bar batun but yace duk lokacin da Rafeek yazo hutu zai had'a su duka ya sanar da su matsayinsu ga juna,,bayan an yi d'aurin aure a ranar at that night Alhaji yasa aka d'auko Hauwa da y'an kayanta daga gidanmu aka mayar da ita gidansa,a cewarsa wannan lokacin it was his greatest right to take care of her and all her other needs kasancewarta matar d'ansa,daga ita har d'an nasa kuma duka k'ark'ashinsa zasu ci gaba da zama zuwa sanda za su kammala karatunsu,matan daya aiko d'aukan amarya suka isar da sak'o,da aka sanar da Baba buk'atar Alhaji zakar yace a basu ita su tafi,bcos shima yana ganin tunda har Allah yasa ya aurar da ita all her right to nourish,watered,dress and lodge fall off his neck a yanzun komai nata ya koma wuyan mijinta,shi yasa ana fad'a masa sak'on Alhaji zakar babu musu ya sallamawa matan ita,at that day she cries as if her life depends on it saboda rashin mahaifiya ko wani da zaiyi d'awainiya da kai a irin wannan lokacin abune da yake tab'a zuciya,,duk wani nau'in gata da y'a take samu a yayin barinta gida babu abunda aka mata,daga gurin mahaifi har y'an uwa babu wanda yayi tunanin siya mata wani abun arziki da idan taje gidan aurenta zai amfane ta,a haka matan da suka zo tafiya da ita suka tattarata suka nufi gidan alhaji zakar.
Zuwanta cikin gidan Alhaji zakar becomes such as the opening of a new page of life filled with light and peaceful,yadda Hajiya take kaffa² da kulawa da ita ta mayar da ita tsakaninta da Maimunatu babu bambanci,haka kowa na gidan ya d'auke ta,ma'aikatan gidan suna girmamata kamar yadda suke yiwa asalin masu gidan,Alhaji ya d'auketa tamkar y'ar cikinsa abunda zai yiwa Maimunatu haka yake yi mata,nutsuwa da kwanciyar hankali suka sake bak'untar ta,cikin lokaci kad'an tayi wani sauyawa na ban mamaki,kyaunta da nutsuwarta da suke b'oye suka sake bayyana.
Rafeek ya dawo hutu Alhaji ya had'a su yayi musu nasiha sannan ya gabatar da Hauwa a matsayin matar daya zab'a masa,cike da nuna biyayya Rafeek ya nuna amincewarsa da zab'in da suka yi masa,cos dama shi bai cika shiga harkar mata ba,yayi godiya ga zab'in mahaifinsa tare da alk'awarin zai rik'e amanarsu kamar yadda suka shaida masa amanace gare shi,,tun daga lokacin da Rafeek ya san matsayin Hauwa a gurinsa bisa ga umarnin mahaifiyarsa ya kasance yana kyautata mata da janta a jiki sama da yadda suke wasa da dariya da Maimunatu kanwarsa,duk da a bayan kafin zuwan wannan lokacin idan ta ganshi tana gaisheshi da bashi girma a matsayin yayan k'awarta,daya bayyanar mata a matsayin mijin aurenta hakan bai sa ta canja daga yadda take ba,sai k'arawa ma da tayi,cikin hukuncin ubangiji a hankali tun bata sake da shi ba,yanayin mu'amalarsa da barkwancinsa yasa ta fara sakewa da shi,kafin a d'auki lokaci shak'uwa mai k'arfi ta shiga tsakaninsu,har ya kasance idan yana gari,ya zo hutu duk inda zata je shi yake mata rakiya,ya zame mata kamar wani bodyguard,mutanen unguwa kuma duk lokacin da suka gansu tare nan zaka ji yan gulamammaki suna ci gaba da yad'uwa,but da yake Rafeek ba mutum ne shi mai yawan magana akan abunda babu ruwansa baya tab'a kulawa.
Alhaji ya maida Hauwa makaranta mai kyau tare da Maimunatu,aka ajiye su class d'aya,gurin zaman su da komai tare suke yinsa a gida ko a makaranta,their closeness to each other continued to grow as they were blood relatives before.
Laying and rising is kinda loss of living,haka nan a wajen ubangiji shekara is like a day,su Hauwa sun gama secondary school bayan wucewar shekaru uku masu kyau,yayin da Rafeek ya kammala degree d'insa har ya nemi wucewa masters but ba'a Nigeria ya nema ba,ya nema ne a k'asar Ghana,though har zuwa lokacin basu tura masa sun bashi admission ba,Alhaji zakar yayi deciding tunda Allah yasa duk suna zaune a gida,mai zai hana ayi bikinsu,zuwa lokacin da can k'asar za su kirashi sai ya d'auki matarsa ko ya barta a nan gurinsu,da ace suna ta zaune basu san matsayin auren nasu ba,da ya sanar musu hukuncin daya zartar sun yi farin ciki sosai,bayan y'an kwanaki aka tashi hidima,Alhaji zakar ya yiwa Hauwa akwatunan lefe guda bakwai kowanne cike taf da kaya na gani a yaba,aka tsaida ranar biki sati guda,,anyi hidima sosai a bikin auren su,yadda ya kashe dukiya babu wanda ba zai yi tunanin y'ar cikinsa yake aurar wa ba,tsayin kwanaki uku akayi biki bisa al'ada da tsari aka gama,aka kai amarya gidanta dake nan a cikin unguwar K'ofar Na'isan itama,tsakanin mu duka babu nisa sosai,tun da muka rakata muka dawo ake ta labarin gidanta,yadda aka kashe mata dukiya a d'akunanta,ko wata y'ar gatan ba zata nuna mata komai ba,a haka dai aka baro amarya a gidanta cikin rufin asirin Allah,,,a kowane dare kamar yadda ko wane ango da amarya suke kasancewa bayan sun kad'aita,a tarihin aure da ma'aurata suma gare su haka ce ta faru tsakanin su,lokacin da komai ya lafa sun samu nutsuwa cike da k'aunar juna da nuna kulawarsu ga juna Rafeek ya lallab'ata tayi bacci,but a gurinsa shi kuma baccin ya k'i zuwa masa,saboda tsananin farin cikin daya tsinci kansa a ciki,a haka ya ga wayewar gari lafiya wacce ta kasance musu mafari.
Baba dai yaga kamar Alhaji zakar na neman maida lamarin wasa duk da shi har zuciyarsa yake maganar,tsam ya tashi ya bar masa gurin ba tare da ya samu damar ce masa komai ba,Alhaji har lokacin yana dariya saboda yadda Baba yayi fushi akan y'ar maganar shima ya tashi ya bar wajen,sai dai wannan karon ko daya tashi maimakon ya shiga gida,kai tsaye ya nufi gidan mai unguwa dan yafi son ace manyan unguwa su shiga cikin lamarin yarinyar ko da Baba ba zai bawa Rafeek aurenta kamar yadda ya fad'a ba,yana so aja hankalinsa ya fasa aurar da ita a wannan lokacin,,anyi sa'a Alhaji ya samu mai unguwa a gida,suka yi magana ta fahimta,ba'a d'auki lokaci mai tsayi ba mai unguwa ya aika d'an sak'o ya kira masa Baba,yaje aka sake maimaita zancen kamar yadda tun farko suka yi tsakaninsu shi da Alhaji zakar a gaban mai unguwa da y'an majalisar mai unguwa,jama'a suka shaida yadda akayi,mai unguwa ya bawa Baba hak'uri akan ya janye batun aurar da Hauwa a matsayinta na karamar yarinya saboda matsalolin da ake fuskanta game da aurar da k'ananun yara,sai dai fa Baba ya kafe yace shi bai ga dalilin da zai sa ya canja ra'ayi ba,duk yadda za'ayi anyi akan ya sakko amma ya kafe kamar lalataccen k'arfe,bisa dole mai unguwa da sauran yan majalisarsa suka hak'ura suka kyale shi bcos y'arsa ce kuma shi yake da iko da abarsa,yana da damar yayi duk abunda yaga yayi masa dai²,a nan ko da suka ga an ciza an busa bai amince ba Alhaji zakar ya sake gabato da buk'atarsa ta son amincewar Baba da batun nemawa Rafeek auren Hauwa'r idan ya amince,Baba yaga da gaske Alhaji zakar yake babu batun wasa,nan take ya amince,mai unguwa suka shiga cikin maganar aka tsaida ranar jumu'ah ta zama ranar d'aurin auren Hauwa da Rafeek.
Anyi addu'o'i na neman sanyawar albarka kafin daga nan taron ya tashi,magulmata kuma suka samu na yi,aka tafi aka fara yad'a cewar Baba ya ga kud'i shi yasa ya amince ya bada y'arsa ga d'an Alhaji zakar ba tare da tunanin abunda zai faru gaba ba,,cikin k'ank'anin lokaci gari ya d'auka,duk inda ka zaga maganar auren ake,lungu da sak'o duk inda mutum baya tunani taje har ta wuce,,ranar jumu'ah bayan an sakko daga masallaci aka d'aura auren *Rafeek Zakar Labbo* da amaryarsa *Hauwa Baba Muhammad*,abisa mafi ingancin sadaki,d'aurin auren daya samu halartar manyan mutane daga b'angaren Alhaji zakar da Baba cikin har da manyan y'an siyasa na k'asa daya shiga ya fita ya gayyato duk da yake bai jima da fad'awa harkar bin y'an siyasar ba (kuji fa baba da k'arfin hali,mutumin da bai da wadataccen matsuguni shi ne ya fad'a siyasa).
A dai² lokacin da ake ta hidimar d'aurin aure,a b'angaren ango babu wanda ya sanar da shi badak'alar da ake a gidansu,bcos baya garin yana Zaria da yake a can yake karatu (A.B.U),kuma lokacin bai jima da komawa ba,wannan dalilin yasa Alhaji yace kada a sanar masa shi da kansa zai masa bayanin komai idan an gama hidimar,da yake ma duka ba a lokacin zasu tare ba,yafi so sai Hauwa sun kammala secondary zuwa lokacin ta k'ara girma sai ayi biki,shima Rafeek zuwa lokacin ya kammala degree d'insa na farko,akan haka Alhaji zakar ya bar batun but yace duk lokacin da Rafeek yazo hutu zai had'a su duka ya sanar da su matsayinsu ga juna,,bayan an yi d'aurin aure a ranar at that night Alhaji yasa aka d'auko Hauwa da y'an kayanta daga gidanmu aka mayar da ita gidansa,a cewarsa wannan lokacin it was his greatest right to take care of her and all her other needs kasancewarta matar d'ansa,daga ita har d'an nasa kuma duka k'ark'ashinsa zasu ci gaba da zama zuwa sanda za su kammala karatunsu,matan daya aiko d'aukan amarya suka isar da sak'o,da aka sanar da Baba buk'atar Alhaji zakar yace a basu ita su tafi,bcos shima yana ganin tunda har Allah yasa ya aurar da ita all her right to nourish,watered,dress and lodge fall off his neck a yanzun komai nata ya koma wuyan mijinta,shi yasa ana fad'a masa sak'on Alhaji zakar babu musu ya sallamawa matan ita,at that day she cries as if her life depends on it saboda rashin mahaifiya ko wani da zaiyi d'awainiya da kai a irin wannan lokacin abune da yake tab'a zuciya,,duk wani nau'in gata da y'a take samu a yayin barinta gida babu abunda aka mata,daga gurin mahaifi har y'an uwa babu wanda yayi tunanin siya mata wani abun arziki da idan taje gidan aurenta zai amfane ta,a haka matan da suka zo tafiya da ita suka tattarata suka nufi gidan alhaji zakar.
Zuwanta cikin gidan Alhaji zakar becomes such as the opening of a new page of life filled with light and peaceful,yadda Hajiya take kaffa² da kulawa da ita ta mayar da ita tsakaninta da Maimunatu babu bambanci,haka kowa na gidan ya d'auke ta,ma'aikatan gidan suna girmamata kamar yadda suke yiwa asalin masu gidan,Alhaji ya d'auketa tamkar y'ar cikinsa abunda zai yiwa Maimunatu haka yake yi mata,nutsuwa da kwanciyar hankali suka sake bak'untar ta,cikin lokaci kad'an tayi wani sauyawa na ban mamaki,kyaunta da nutsuwarta da suke b'oye suka sake bayyana.
Rafeek ya dawo hutu Alhaji ya had'a su yayi musu nasiha sannan ya gabatar da Hauwa a matsayin matar daya zab'a masa,cike da nuna biyayya Rafeek ya nuna amincewarsa da zab'in da suka yi masa,cos dama shi bai cika shiga harkar mata ba,yayi godiya ga zab'in mahaifinsa tare da alk'awarin zai rik'e amanarsu kamar yadda suka shaida masa amanace gare shi,,tun daga lokacin da Rafeek ya san matsayin Hauwa a gurinsa bisa ga umarnin mahaifiyarsa ya kasance yana kyautata mata da janta a jiki sama da yadda suke wasa da dariya da Maimunatu kanwarsa,duk da a bayan kafin zuwan wannan lokacin idan ta ganshi tana gaisheshi da bashi girma a matsayin yayan k'awarta,daya bayyanar mata a matsayin mijin aurenta hakan bai sa ta canja daga yadda take ba,sai k'arawa ma da tayi,cikin hukuncin ubangiji a hankali tun bata sake da shi ba,yanayin mu'amalarsa da barkwancinsa yasa ta fara sakewa da shi,kafin a d'auki lokaci shak'uwa mai k'arfi ta shiga tsakaninsu,har ya kasance idan yana gari,ya zo hutu duk inda zata je shi yake mata rakiya,ya zame mata kamar wani bodyguard,mutanen unguwa kuma duk lokacin da suka gansu tare nan zaka ji yan gulamammaki suna ci gaba da yad'uwa,but da yake Rafeek ba mutum ne shi mai yawan magana akan abunda babu ruwansa baya tab'a kulawa.
Alhaji ya maida Hauwa makaranta mai kyau tare da Maimunatu,aka ajiye su class d'aya,gurin zaman su da komai tare suke yinsa a gida ko a makaranta,their closeness to each other continued to grow as they were blood relatives before.
Laying and rising is kinda loss of living,haka nan a wajen ubangiji shekara is like a day,su Hauwa sun gama secondary school bayan wucewar shekaru uku masu kyau,yayin da Rafeek ya kammala degree d'insa har ya nemi wucewa masters but ba'a Nigeria ya nema ba,ya nema ne a k'asar Ghana,though har zuwa lokacin basu tura masa sun bashi admission ba,Alhaji zakar yayi deciding tunda Allah yasa duk suna zaune a gida,mai zai hana ayi bikinsu,zuwa lokacin da can k'asar za su kirashi sai ya d'auki matarsa ko ya barta a nan gurinsu,da ace suna ta zaune basu san matsayin auren nasu ba,da ya sanar musu hukuncin daya zartar sun yi farin ciki sosai,bayan y'an kwanaki aka tashi hidima,Alhaji zakar ya yiwa Hauwa akwatunan lefe guda bakwai kowanne cike taf da kaya na gani a yaba,aka tsaida ranar biki sati guda,,anyi hidima sosai a bikin auren su,yadda ya kashe dukiya babu wanda ba zai yi tunanin y'ar cikinsa yake aurar wa ba,tsayin kwanaki uku akayi biki bisa al'ada da tsari aka gama,aka kai amarya gidanta dake nan a cikin unguwar K'ofar Na'isan itama,tsakanin mu duka babu nisa sosai,tun da muka rakata muka dawo ake ta labarin gidanta,yadda aka kashe mata dukiya a d'akunanta,ko wata y'ar gatan ba zata nuna mata komai ba,a haka dai aka baro amarya a gidanta cikin rufin asirin Allah,,,a kowane dare kamar yadda ko wane ango da amarya suke kasancewa bayan sun kad'aita,a tarihin aure da ma'aurata suma gare su haka ce ta faru tsakanin su,lokacin da komai ya lafa sun samu nutsuwa cike da k'aunar juna da nuna kulawarsu ga juna Rafeek ya lallab'ata tayi bacci,but a gurinsa shi kuma baccin ya k'i zuwa masa,saboda tsananin farin cikin daya tsinci kansa a ciki,a haka ya ga wayewar gari lafiya wacce ta kasance musu mafari.