Sashe 4
Dan Mace Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Lokacin daya shiga d'akin a kwance ya isketa tana bacci,da alamun kamar bata farka ba har lokacin,gefen gadon ya k'arasa bayan ya d'an yi jimm a kusa da ita yana kallonta da tausayawa ya rik'o hannunta slowly yana murzawa,lokaci guda yanayin damuwa ya bayyana saman kyakykyawar fuskarsa,ya jima sosai a kanta yana ta kallonta ba tare da ta san ya shigo ba,kamar wanda ake tursasawa dole yana ta kallonta ya bud'e bakinsa da kyar
"Lolly.! I dunno how things suke tafiya min a haka cikin kwanakin nan,ina yawan yin mafarkin abubuwa marasa dad'i suna faruwa,,but na san ba akan komai ne hakan yake faruwa ba face ciwon ki da a kullum da tunaninsa nake rayuwa,,tun bayan dana mallaki hankali na nake cikin damuwa,a duk lokacin dana bud'e idanuna na ganki cikin wannan yanayin ina tsintar rayuwata cikin k'unci,ban san mene ne zanyi na cire ki daga wannan k'angin ba,ina son ganinki cikin lafiya kamar kowane d'an adam mai y'anci,,but i don't even know mene ne zan aikata da zai sa ki dawo kamar kowa farat d'aya.. Ina sonki sosai kuma ina tausayinki,,,Ku biyun nan ku ne kad'ai duniyata kuma dangina,bayan ku ban san kowa ba,,ciki har da mahaifina,ban san wane ne shi ba,yaya yake.? A ina yake.? Duk ban sani ba,ban san komai game da shi ba,even his name ban sani ba,and u know ina son sanin abubuwa da dama game da rayuwata,but ban san mene ne dalilin da yasa kuka kasa sanar dani ba,,shin ina mahaifina yake ne..?? Ina son sanin wane ne shi.? Mene ne ya faru dake bayan samuwata.? Jikina ya jima yana sanar dani akwai damuwa a cikin rayuwarmu,,ina son sanin komai.."
Shiru ya d'anyi yana sakin numfashi,jikinsa duk ya sake yin sanyi,a hankali ya kai hannunsa ya goge hawayen da suka gangaro masa yaci gaba "All i wish a rayuwata shi ne na ganki kinyi rayuwa kamar kowa ne bil'adam mai y'anci,, sai dai ban san yaya zanyi ba ko ta yaya ne hakan zai kasance.. Duk irin sonyayyar da nake miki a matsayin mahaifiyata,na san ban isa na cire miki wannan larurar ba,,ina tsananin sonki,soyayya irin wacce baki bazai iya fad'a ba,ina miki so irin na tsakanin d'a da mahaifiya,ina sonki da dukkan zuciyata,,ana ahabbuk Mamah.. Ahabbuk.! Ahabbuk-thtiir.!"
Kansa ya sauke a hankali zuwa saman jikinta yana ci gaba da sauke hawayen damuwa da ajiyar zuciya masu nauyi,Annie dake tsaye bakin k'ofa tun d'azun ta gama jin kalaman da yake furtawa ita kanta bata san yaushe hawaye suka fara gangaro mata ba da sauri ta juya ta bar wajen tana ci gaba da hawaye masu d'umi da k'una,kitchen ta shige ta kulle kanta a nan tayi kuka har ta godewa Allah,bayan wucewar wasu mintuna still tana zaune ta buga tagumi take tunanin anya ta yiwa Nuraz d'in adalci da taja baki tayi shiru har tsayin wannan lokacin.? Shin tsayin wane lokaci ne zasu d'auka tana b'oye masa asalinsa.? A yanzun shekarunsa da hankalinsa ya kai ace yasan wane ne shi.? To amma ta ina zata fara sanar masa.? Shiru tayi tana sake zurfafa tunani har zuwa tsayin wani lokaci kafin ta yanke shawarar abunda take ganin shi ne yafi mata dai².
Yana kwance a jikinta bayan tafiyar Annie Dr Waseem ya shigo d'akin da sallama bcos lokacin daya kamata ya dubata yayi,har ya k'araso kusa da shi bai san ya shigo ba sai da ya tab'a shi
"Hello handsome..!"
A d'an tsorace Nuraz ya d'ago duk da ya fahimci muryar waye,cikin dabara ya goge idonsa sannan ya waiwayo ya mik'awa Dr Waseem hannu bayan ya k'irk'iro murmushi
"Welcome Dr."
Suka yi musabaha Dr Waseem yana sake tambayarsa
"How are u,,nd how was the patient.?"
"Alhamdulillah." Yace yana sake kallonta
"Allah ya k'ara mata lafiya" Dr Waseem ya fad'a yana maida hankalinsa kanta,Nuraz ya amsa da "Ameen" d'akin yayi shiru,Dr Waseem ya wuce kusa da ita ya fara shirin duba jikin nata,,Annie ta sake dawowa a karo na biyu bayan sun gaisa da Dr Waseem,ba tare da ta kalli Nuraz dake mak'ale da hannun mahaifiyarsa ba tace
"Habibiiy! Zo maza ina son ganinka yanzun ka kyale Dr yayi aikinsa.!"
Tana fad'a bata jira ba ta juya ta bar wajen,kamar bazai tashi ba ya fara binta da kallo har ta fita kafin ya mik'e ya bita yana jin zuciyarsa duk babu dad'i,a parlor ya tarar da ita zaune ta dafe chin d'inta da duka hannayenta biyu,tana ganin fitowarsa da sauri ta nuna masa kusa sa ita tace
"Sit" babu musu ya nemi guri ya zauna yana d'an kallonta but k'irjinsa yana ji kamar ana kwala masa abu ta ciki,nan da nan ya fara ji yayi masa wani irin nauyi,idanunsa ya runtse yana d'ora hannunsa a dai² saitin zuciyarsa slowly ya shiga karanta
"Allaahumma inniiy a'uzhu bika minal-hammi walhazan,wal'ajazi walkasal,walbukhli waljubni,wa'dhala'id-dayni wa'ghalabatir-rijaal."
A hankali² yana ta maimaitawa har ya fara jin k'irjinsa yana sanyi,damuwar da yake tare da ita ta fara yayewa,ci gaba yayi da maimaitawa har tsayin lokacin da yaji ya dawowa nutsuwarsa tamkar dama can wani abu bai faru da shi ba sannan ya dakata yana sake fuskantar Annie da itama shi d'in take kallo tun d'azun ganin yayi shiru da idanunsa a rufe.....
#Posting wannan karon yana wattpad da yardar Allah,but idan na ga babu voting zan ajiye na koma whatsapp & facebook kamar last novel.
#Vote,
#Comment &
#Share pls.
#Real Smasher.
💠💠💠💠💠
*©®2020.*
*'DAN MACE..*
(Tʜᴇ ᴘꜱʏᴄʜɪᴀᴛʀɪꜱᴛ)..💥
*WATTPAD:REAL-SMASHER898.*
https://my.w.tt/29u2S26SG2
Alkhairin Allah ya kai miki uwa ta gari *Hajiya Maryam Alhassan (Oum Feedy & I)* ina mik'o gaisuwa,da addu'ar fatan alkhairi gare ki,Ubangiji ya raya zuri'ah,ya albarkaci rayuwarsu.
Pᴀɢᴇ 3.
#Tʜᴇ Bᴇɢɪɴɴɪɴɢ
Duk abunda yake idanunta na kansa,duk da niyyarta da farko data kira shi,ta shirya yi masa nasiha ne akan damuwar da yake sawa kansa cikin kwanakin,but ganin da tayi masa a yanzun da maganganun da yake yi lokacin data shiga d'akin,yasa taji duk guiwoyinta sunyi sanyin da har tana ji a ranta baza ta iya sake b'oye masa komai dan gane da rayuwarsa ba,,sun d'auki lokaci zaune shiru babu wanda yayi magana tun zamansu ko wannensu da tunanin da yake zuciyarsa,fitowar Dr Waseem yana tambayar Annie abincin da aka dafa mata ya taimaka wajen dawo dasu cikin hankulansu,jikin Annie a sanyaye ta kira maidservant d'insu Bareerah dake taimakonta ta b'angaren kulawa da gidan ta kawo masa ya karb'a ya wuce,hannun Nuraz ta rik'o cikin nata a hankali bayan sun kasance su biyun tana sauke nauyayyun ajiyar zuciya tace
"Samahniiy ya ibniiy..!"
A d'an dake ya kalleta yace "Annie what's going wrong kike neman yafiya ta.?? Ni mene ne kika yi min,a iya sani na tun dana taso ni baki tab'a min komai ba.. Daya wuce kyautatawa."
Hannunta tayi saurin d'orawa saman lips d'insa tana girgiza masa kai tace
"Skutiiy habibiiy.. Kada kace komai.!"
"Annie.! Stop this drama,ni na san baki yimin komai bafa."
"A'a habibiiy kada kace haka,,tabbas a gareka na kasance mai laifi,kai ne dai da baka san na aikata hakan ba kake k'ok'arin nuna min bani da laifi a gurinka,,but idan har baka yafe min ba tabbas ban san yaya zanji a rayuwata ba,ban san ina zan kai girman hak'k'in ka akaina ba."
Ajiyar zuciya yayi ya sake damk'e hannunta a nasa fuskarsa bayyane da damuwa yace
"Annie.! Dan Allah ki bari,nifa babu abunda kika yimin,,idan ma akwai ni ina so ki k'addara a ranki tun kafin kiyi na yafe miki,bcos baki cancanta da zama a sahun wad'anda za'a ga laifinsu ba idan sunyi KUSKURE..I knew KUSKURE ne ba don kina sane ba.."
Sai da tayi murmushin samun sukuni ta shafo gefen fuskarsa sannan tace
"Shukhraan'kthiir habibiiy,,sai dai sam fa ba yadda kake tunani bane.."
"Uhn!" Yace yana sake zuba idanunsa akanta,kallonsa itama ta sake yi tace
"Je kayi breakfast tukun kazo,akwai maganganun da nake son muyi da kai a yau idan rabb ya nufa."
"Really Annie.!?" Tace "Haka nake tunani idan rabb ya ara mana lokaci!" A hankali ya jirkita kansa gefe sannan yace "Okay" ya tashi ya nufi dining,Annie nata kallonsa har ya fara bud'e warmers dake gurin,shi yayi serving kansa,bayan ya zauna ci kawai yake amma sam baza ka tab'a gane yanayin dake kan fuskarsa ba,kad'an yaci ya ture plate d'in da mug daya had'a tea,ya taso ya dawo kusa da ita yana fad'in
"Annie na gama.."
"Uhn!" Tace,,haka nan tunda ta amsa ya tsinci kansa da sake nutsuwa idanunsa a k'asa yana ta addu'ar Allah yasa ko mene ne zata fad'a masa a dai² lokacin yazo masa da sauk'i kuma ya kasance alkhairi,muryar Annie ta katse masa tunani data kirashi
"Habibiiy.!" A sanyaye da irin muryar data kira shi yace "Na'am Annie",jim tayi kafin tace
"I want to tell u something,,though i know it's extremely ugly.. But ina fatan baza ka k'arawa kanka damuwa ba bayan kaji abunda zan fad'a."
Gabansa yaji ya fad'i da sauri ya d'ago ya kalleta yana marairaicewa "Annie.! Please idan dai zai tada mana hankali kawai ki barshi ba sai kin fad'a ba,ni banga amfanin ace a yanayin da muke kuma muna sake sharing wani damuwar ba,kawai a hak'ura ba sai kin fad'a ba,dama haka Allah ya nufa.."
"Ya zama dole ka sani habibiiy,,wajibi na ne na fad'a maka,ko dama ace na b'oye maka a yanzun,dole ne wata rana nan gaba kad'an kai da kanka ka sake tambaya,wannan dalilin yasa tun kafin zuwan lokacin na yanke shawaran sanar da kai,ni na huta da dako kaima ka huta tunani da damun rayuwarka akan son binciko gaskiya."
"Amma Annie.!"
"Lolly.! I dunno how things suke tafiya min a haka cikin kwanakin nan,ina yawan yin mafarkin abubuwa marasa dad'i suna faruwa,,but na san ba akan komai ne hakan yake faruwa ba face ciwon ki da a kullum da tunaninsa nake rayuwa,,tun bayan dana mallaki hankali na nake cikin damuwa,a duk lokacin dana bud'e idanuna na ganki cikin wannan yanayin ina tsintar rayuwata cikin k'unci,ban san mene ne zanyi na cire ki daga wannan k'angin ba,ina son ganinki cikin lafiya kamar kowane d'an adam mai y'anci,,but i don't even know mene ne zan aikata da zai sa ki dawo kamar kowa farat d'aya.. Ina sonki sosai kuma ina tausayinki,,,Ku biyun nan ku ne kad'ai duniyata kuma dangina,bayan ku ban san kowa ba,,ciki har da mahaifina,ban san wane ne shi ba,yaya yake.? A ina yake.? Duk ban sani ba,ban san komai game da shi ba,even his name ban sani ba,and u know ina son sanin abubuwa da dama game da rayuwata,but ban san mene ne dalilin da yasa kuka kasa sanar dani ba,,shin ina mahaifina yake ne..?? Ina son sanin wane ne shi.? Mene ne ya faru dake bayan samuwata.? Jikina ya jima yana sanar dani akwai damuwa a cikin rayuwarmu,,ina son sanin komai.."
Shiru ya d'anyi yana sakin numfashi,jikinsa duk ya sake yin sanyi,a hankali ya kai hannunsa ya goge hawayen da suka gangaro masa yaci gaba "All i wish a rayuwata shi ne na ganki kinyi rayuwa kamar kowa ne bil'adam mai y'anci,, sai dai ban san yaya zanyi ba ko ta yaya ne hakan zai kasance.. Duk irin sonyayyar da nake miki a matsayin mahaifiyata,na san ban isa na cire miki wannan larurar ba,,ina tsananin sonki,soyayya irin wacce baki bazai iya fad'a ba,ina miki so irin na tsakanin d'a da mahaifiya,ina sonki da dukkan zuciyata,,ana ahabbuk Mamah.. Ahabbuk.! Ahabbuk-thtiir.!"
Kansa ya sauke a hankali zuwa saman jikinta yana ci gaba da sauke hawayen damuwa da ajiyar zuciya masu nauyi,Annie dake tsaye bakin k'ofa tun d'azun ta gama jin kalaman da yake furtawa ita kanta bata san yaushe hawaye suka fara gangaro mata ba da sauri ta juya ta bar wajen tana ci gaba da hawaye masu d'umi da k'una,kitchen ta shige ta kulle kanta a nan tayi kuka har ta godewa Allah,bayan wucewar wasu mintuna still tana zaune ta buga tagumi take tunanin anya ta yiwa Nuraz d'in adalci da taja baki tayi shiru har tsayin wannan lokacin.? Shin tsayin wane lokaci ne zasu d'auka tana b'oye masa asalinsa.? A yanzun shekarunsa da hankalinsa ya kai ace yasan wane ne shi.? To amma ta ina zata fara sanar masa.? Shiru tayi tana sake zurfafa tunani har zuwa tsayin wani lokaci kafin ta yanke shawarar abunda take ganin shi ne yafi mata dai².
Yana kwance a jikinta bayan tafiyar Annie Dr Waseem ya shigo d'akin da sallama bcos lokacin daya kamata ya dubata yayi,har ya k'araso kusa da shi bai san ya shigo ba sai da ya tab'a shi
"Hello handsome..!"
A d'an tsorace Nuraz ya d'ago duk da ya fahimci muryar waye,cikin dabara ya goge idonsa sannan ya waiwayo ya mik'awa Dr Waseem hannu bayan ya k'irk'iro murmushi
"Welcome Dr."
Suka yi musabaha Dr Waseem yana sake tambayarsa
"How are u,,nd how was the patient.?"
"Alhamdulillah." Yace yana sake kallonta
"Allah ya k'ara mata lafiya" Dr Waseem ya fad'a yana maida hankalinsa kanta,Nuraz ya amsa da "Ameen" d'akin yayi shiru,Dr Waseem ya wuce kusa da ita ya fara shirin duba jikin nata,,Annie ta sake dawowa a karo na biyu bayan sun gaisa da Dr Waseem,ba tare da ta kalli Nuraz dake mak'ale da hannun mahaifiyarsa ba tace
"Habibiiy! Zo maza ina son ganinka yanzun ka kyale Dr yayi aikinsa.!"
Tana fad'a bata jira ba ta juya ta bar wajen,kamar bazai tashi ba ya fara binta da kallo har ta fita kafin ya mik'e ya bita yana jin zuciyarsa duk babu dad'i,a parlor ya tarar da ita zaune ta dafe chin d'inta da duka hannayenta biyu,tana ganin fitowarsa da sauri ta nuna masa kusa sa ita tace
"Sit" babu musu ya nemi guri ya zauna yana d'an kallonta but k'irjinsa yana ji kamar ana kwala masa abu ta ciki,nan da nan ya fara ji yayi masa wani irin nauyi,idanunsa ya runtse yana d'ora hannunsa a dai² saitin zuciyarsa slowly ya shiga karanta
"Allaahumma inniiy a'uzhu bika minal-hammi walhazan,wal'ajazi walkasal,walbukhli waljubni,wa'dhala'id-dayni wa'ghalabatir-rijaal."
A hankali² yana ta maimaitawa har ya fara jin k'irjinsa yana sanyi,damuwar da yake tare da ita ta fara yayewa,ci gaba yayi da maimaitawa har tsayin lokacin da yaji ya dawowa nutsuwarsa tamkar dama can wani abu bai faru da shi ba sannan ya dakata yana sake fuskantar Annie da itama shi d'in take kallo tun d'azun ganin yayi shiru da idanunsa a rufe.....
#Posting wannan karon yana wattpad da yardar Allah,but idan na ga babu voting zan ajiye na koma whatsapp & facebook kamar last novel.
#Vote,
#Comment &
#Share pls.
#Real Smasher.
💠💠💠💠💠
*©®2020.*
*'DAN MACE..*
(Tʜᴇ ᴘꜱʏᴄʜɪᴀᴛʀɪꜱᴛ)..💥
*WATTPAD:REAL-SMASHER898.*
https://my.w.tt/29u2S26SG2
Alkhairin Allah ya kai miki uwa ta gari *Hajiya Maryam Alhassan (Oum Feedy & I)* ina mik'o gaisuwa,da addu'ar fatan alkhairi gare ki,Ubangiji ya raya zuri'ah,ya albarkaci rayuwarsu.
Pᴀɢᴇ 3.
#Tʜᴇ Bᴇɢɪɴɴɪɴɢ
Duk abunda yake idanunta na kansa,duk da niyyarta da farko data kira shi,ta shirya yi masa nasiha ne akan damuwar da yake sawa kansa cikin kwanakin,but ganin da tayi masa a yanzun da maganganun da yake yi lokacin data shiga d'akin,yasa taji duk guiwoyinta sunyi sanyin da har tana ji a ranta baza ta iya sake b'oye masa komai dan gane da rayuwarsa ba,,sun d'auki lokaci zaune shiru babu wanda yayi magana tun zamansu ko wannensu da tunanin da yake zuciyarsa,fitowar Dr Waseem yana tambayar Annie abincin da aka dafa mata ya taimaka wajen dawo dasu cikin hankulansu,jikin Annie a sanyaye ta kira maidservant d'insu Bareerah dake taimakonta ta b'angaren kulawa da gidan ta kawo masa ya karb'a ya wuce,hannun Nuraz ta rik'o cikin nata a hankali bayan sun kasance su biyun tana sauke nauyayyun ajiyar zuciya tace
"Samahniiy ya ibniiy..!"
A d'an dake ya kalleta yace "Annie what's going wrong kike neman yafiya ta.?? Ni mene ne kika yi min,a iya sani na tun dana taso ni baki tab'a min komai ba.. Daya wuce kyautatawa."
Hannunta tayi saurin d'orawa saman lips d'insa tana girgiza masa kai tace
"Skutiiy habibiiy.. Kada kace komai.!"
"Annie.! Stop this drama,ni na san baki yimin komai bafa."
"A'a habibiiy kada kace haka,,tabbas a gareka na kasance mai laifi,kai ne dai da baka san na aikata hakan ba kake k'ok'arin nuna min bani da laifi a gurinka,,but idan har baka yafe min ba tabbas ban san yaya zanji a rayuwata ba,ban san ina zan kai girman hak'k'in ka akaina ba."
Ajiyar zuciya yayi ya sake damk'e hannunta a nasa fuskarsa bayyane da damuwa yace
"Annie.! Dan Allah ki bari,nifa babu abunda kika yimin,,idan ma akwai ni ina so ki k'addara a ranki tun kafin kiyi na yafe miki,bcos baki cancanta da zama a sahun wad'anda za'a ga laifinsu ba idan sunyi KUSKURE..I knew KUSKURE ne ba don kina sane ba.."
Sai da tayi murmushin samun sukuni ta shafo gefen fuskarsa sannan tace
"Shukhraan'kthiir habibiiy,,sai dai sam fa ba yadda kake tunani bane.."
"Uhn!" Yace yana sake zuba idanunsa akanta,kallonsa itama ta sake yi tace
"Je kayi breakfast tukun kazo,akwai maganganun da nake son muyi da kai a yau idan rabb ya nufa."
"Really Annie.!?" Tace "Haka nake tunani idan rabb ya ara mana lokaci!" A hankali ya jirkita kansa gefe sannan yace "Okay" ya tashi ya nufi dining,Annie nata kallonsa har ya fara bud'e warmers dake gurin,shi yayi serving kansa,bayan ya zauna ci kawai yake amma sam baza ka tab'a gane yanayin dake kan fuskarsa ba,kad'an yaci ya ture plate d'in da mug daya had'a tea,ya taso ya dawo kusa da ita yana fad'in
"Annie na gama.."
"Uhn!" Tace,,haka nan tunda ta amsa ya tsinci kansa da sake nutsuwa idanunsa a k'asa yana ta addu'ar Allah yasa ko mene ne zata fad'a masa a dai² lokacin yazo masa da sauk'i kuma ya kasance alkhairi,muryar Annie ta katse masa tunani data kirashi
"Habibiiy.!" A sanyaye da irin muryar data kira shi yace "Na'am Annie",jim tayi kafin tace
"I want to tell u something,,though i know it's extremely ugly.. But ina fatan baza ka k'arawa kanka damuwa ba bayan kaji abunda zan fad'a."
Gabansa yaji ya fad'i da sauri ya d'ago ya kalleta yana marairaicewa "Annie.! Please idan dai zai tada mana hankali kawai ki barshi ba sai kin fad'a ba,ni banga amfanin ace a yanayin da muke kuma muna sake sharing wani damuwar ba,kawai a hak'ura ba sai kin fad'a ba,dama haka Allah ya nufa.."
"Ya zama dole ka sani habibiiy,,wajibi na ne na fad'a maka,ko dama ace na b'oye maka a yanzun,dole ne wata rana nan gaba kad'an kai da kanka ka sake tambaya,wannan dalilin yasa tun kafin zuwan lokacin na yanke shawaran sanar da kai,ni na huta da dako kaima ka huta tunani da damun rayuwarka akan son binciko gaskiya."
"Amma Annie.!"