Sashe 24
Dan Mace Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Ta share hawaye tace "Saboda kunga bana raye kuka wulakanta min y'ata.! Me yasa sai da kuka bari na tafi sannan za ku wofantar da ita.!?"
Ina kuka ina bawa Inna hak'uri,bata saurare ni ba ta juya ta ci gaba da tafiya tana cewa "Idan har baki nemi inda y'ar uwarki take kin zauna tare da ita ba,kada ki sake kira na mahaifiyarki,ni ba mahaifiyarki bace,a kullum ina jin bak'in ciki na haifi y'a irin ki.."
Nace "Inna ki yi hak'uri dan Allah,nima fa duka ba laifi na bane,ki yarda dani,babanmu ya hana ni zuwa na dubasu."
Ta juyo ta kalle ni tana goge hawaye tace "Shi kenan,tunda kin yarda ya raba muku zumunci ki zauna tare da mahaifinki,in sha Allah ubangijin daya hallice mu ba zai tab'a barin Hauwa'u tayi maraici ba.. Daga yau ba zaki sake gani na ba,ki je ki zauna da mahaifinki.."
Tana gama fad'ar haka ta juya da sauri,ina kuka ina kiranta amma bata sake waiwayowa ba,jan jiki naci gaba da yi ina son bin hanyar da ta bi,saboda lokacin dana fad'i na ji ciwo sosai a k'afata,na kasa tashi na bita ina nan kwance ina kuka da kiranta har ta b'acewa ganina,cikin k'araji na kwalla kiran Inna,,a firgice na tashi ina dube²,na bud'e ido naga y'an uwanmu mata zagaye da ni sai kallona suke yi suna jiran su ji abunda ya faru na ke zabgaga ihu a farkon dare,na daure na juya ban yiwa kowa magana ba duk tarin tambayoyin da suke min,da suka ga ba ni da niyyar amsa musu kowacce ta juya ta kwanta,,a wannan daren ni dai ban samu damar komawa bacci ba har gari ya waye.
Misalin k'arfe 10am lokacin babanmu ya fita na shirya cikin damuwa,ba tare da sanin kowa ba na d'auki takardata na fita daga gida,na samu mai napep na fad'a masa inda zai kaini,yace na shiga ya san gurin,na shiga muka d'auki hanya,mintuna kusan talatin suka d'auke mu saboda baya wani sauri sosai muka k'araso,ya tsaya a dai² block d'in dana fad'a masa,ina ta tunanin halin da zan tarar da ita yace min "Hajiya mun k'araso."
Na kalli gurin da muke nace "Ka tabbata nan ne kuwa.!?"
Yace "Hajiya ai number za ki duba,ke kika fad'a min fa,ga gidan nan ki sake dubawa mana"
Na kalli house number sosai na duba ta jikin takarda,na ga iri d'aya ce babu bambanci,na sake kallon tsarin gidan na tabbatar nan ne inda ta rubuta,na sauka na biya mai napep kud'insa sannan na juya na kalli gidan,zuciyata har lokacin cike taf da tunanin anya nan d'in ne.!? Ina wannan tunanin na tunkari get d'in gidan,na yi shahada nayi knocking ina tunanin ganin ta inda Hauwa zata b'illo amma sai naji shiru,har kusan mintuna goma ban ji motsin kowa ba bare na ga mutum,nayi tunanin sake kwankwasawa amma wannan karon sai na tab'a entrance d'in,abun mamaki ashe k'ofar a bud'e take duk tsaiwar da nake yi,da mamaki sosai akan fuskata na kalli unguwar da nake jinta shiru sannan na wuce ciki na fara tafiya ina yi ina kallon ikon Allah da mamakin yadda aka yi Rafeek yayi mata kyautar gida kamar wannan,har na k'araso varenda da zata sada ni da parlor,na tsaya ina jin fargaba,a zuciyata ina addu'ar Allah yasa lafiya,na daure nayi knocking door d'in kusan mintuna uku shiru babu wani amsan da na samu,na sake yin knocking abun mamakin babu alamun mutum yana rayuwa a cikin gidan,gabana ya fad'i dana tuno kalamanta na ji hawaye suna k'ok'arin wanke min fuska,na nemi guri na zauna na ci gaba da addu'ar Allah yasa ba mutuwa Hauwa tayi ta barni ba,after 2 hours na goge hawaye idanuna duk sun kumbura,na mik'e da niyyar tafiya jikina duk yayi sanyi,na sakko daga saman varenda na kama hanyar get zan bar gidan,ina tafiya ina waiwaye,na yi nisa cikin hukuncin ubangiji na jiyo kamar sautin tari,da sauri na tsaya ina kalle² da tunanin ta ina sautin yake fitowa,amma kuma sai na rasa ina ne,na dawo da sauri na fara bin windows d'in da suke zagaye da gidan,duk window da na nufa sai na tarar da ita a rufe,idan na lek'a bana iya ganin komai saboda curtains dake zagaye da su duka masu duhu ne,nayi ta zagayawa kasancewar ginin gidan detached house ne da baiyi joining ko wane wall ba,irin ginin nan dai kawai da ake yinsa a tsakiya,na kusa gama zagaye gidan ina neman hanyar da zan shiga,dai² lokacin dana gama fitar da tsammani da samun mafita ubangiji ya taimake ni ya ji k'aina.
Window ne guda d'aya daga can edge na k'arshe na gidan a bud'e,har ina had'awa da gudu na k'arasa jikinsa na tsaya ina addu'ar Allah yasa abunda zuciyata take sanar da ni ya kasance gaskiya,sai dana gama addu'o'i na sannan nayi k'arfin hali na kai hannuna jikin windowpanes d'in ina k'ok'arin bud'ewa,kasancewar da yawa windows dana bari a baya na yi gwada bud'ewa ban samu dama ba,sai wannan da alamu suka nuna a bud'e take,ina janyowa ta bud'e na runtse idanuna cikin fargaba,curtains d'in da suka rufe ba'a ganin komai nasa hannu ina k'ok'arin bud'ewa duka,a nan idanuna suka yi bak'in gani.....
#Share pls.
#Real Smasher.
💠💠💠💠💠
*©®2020.*
*'DAN MACE..*
(Tʜᴇ ᴘꜱʏᴄʜɪᴀᴛʀɪꜱᴛ)..💥
*WATTPAD:REAL-SMASHER898.*
https://my.w.tt/29u2S26SG2
*Wah! 😍 U people are killing me with ur warmth comments,thank u so very much,thank u all my friends..Bahot² shukhurya..*♥
Pᴀɢᴇ 12.
#Iɴꜱᴀɴɪᴛʏ
Akan Hauwa idanuna suka fara sauka,kwance take amma cikin wani irin yanayi mai ban tsoro da firgitarwa,na koma baya da sauri cikin tsananin tashin hankali har ban san lokacin da na fasa k'ara ba,ta juyo ta kalli inda taji ihun bata ga kowa ba,ta juyar da kanta babu damuwar komai a ranta,nayi kuka sosai har sai da naji na sire bana iya sake yin hawaye,guiwoyina sun yi sanyi bayan na bawa zuciyata hak'uri na sake matsawa jikin window ina ta kallonta a hankali cikin muryar mai kashe jiki na kira sunan ta "Hauwa'u.!"
Ta juyo da sauri ta kallo inda nake,a hankali ta k'uramin ido kamar mai son tuna wace ce ni,na daure duk da hawayen da suke bin fuskata nace "Me ya same ki kika dawo haka.!?"
Ta yi shiru ta ci gaba da kallo na ba tare da ta ce komai ba,ina kuka nace "zo maza ki bud'e min k'ofa,ni ce y'ar uwar ki,ban san haka rayuwarki zata dawo ba,ki gafarce ni y'ar uwata,da na san haka al'amarin nan zai kasance tabbas ba zan tab'a bari kiyi nisa da ni ba,sai dai duk abunda zai faru ya faru,ki yimin afuwa k'anwata,ba a son raina haka ta faru ba.."
Still bata motsa daga inda take ba,ta yi shiru dai ta zuba min idanunta,duk abunda nake fad'a tana saurare na,sai dai alamu sun gwada gaba d'aya bata fahimtar abunda nake cewa,nayi magana nayi begging d'inta amma kusan duka a banza babu wanda ta ji,bare ta aikata.
Yinin ranar ya kasance a nan na yi shi ina yawo tsakanin harabar gidan da window d'in d'akin da take,har dare ya fara gabatowa ban samu damar shiga cikin gidan ba,wajen misalin k'arfe goma saura mintuna na sake komawa inda take,har lokacin tana nan kamar yadda na barta,na tsaya ina kallonta da tausayawa nace "Hauwa.!"
Jin magana yasa tayi sauri ta waiwayo tana kallona,na daure nace "Zanje gida na tattaro kayana,in sha Allah ina nan dawowa ba da jimawa ba kin ji.!?"
Kamar ta fahimci abunda nake nufi ta juyar da kanta ta k'urawa guri d'aya ido,cikin yanayin sanyin jiki na janyo k'afafuna na fito,ta waje na samu cable na d'aure get d'in sannan na kama hanya ina tafe ina gabana sai fad'uwa yake,a haka na fara neman abun hawa,da kyar lokacin 11pm saura mintuna 15 na samu napep,na fad'a masa inda zai kai ni,yace na hau mu tafi,na shiga muka fara tafiya,Allah ya taimake ni na samu irin masu napep d'in zamani,gudun da muka yi a lokacin ni na san ba kadan bane,11:00pm muka tsaya a k'ofar gidanmu,na sauka na sallami mai napep,na wuce cikin gida gabana yana ci gaba da fad'uwa,saboda ban san me zan tarar ba.
***
Abunda ya faru gidan mu kuwa a yinin ranar,bayan fita ta daga gida,ban san wane ne ya fad'awa Baba na fita ba,ya saba baya dawowa da wuri amma ranar after Maghreb Baba ya dawo ya fara jkran yaga ta inda zan b'illo,har 11:00pm saura mintuna bai ganni ba bai kuma samu labarin inda na mak'ale ba,dai² lokacin da agogo ya nuna 11pm Baba ya kira babban yayanmu Abdullahi yace yaje ya rufe masa k'ofar gidansa,yayanmu ya taho da niyyar rufe k'ofa kamar yadda Baba yayi masa umarni muka gamu a zaure,ya kalleni ya wuce ba tare da yace min komai ba,na wuce cikin mutuwar jiki saboda irin kallon da naga yayanmu yayi min na k'araso tsakar gida,nayi sallama babu wanda ya amsa,na kallesu d'aya bayan d'aya naga ni suke kallo,nayi ajiyar zuciya ina k'ok'arin wucewa suka fara gulma a tsakaninsu suna tambayar juna "Ko daga ina take da wannan talatainin daren.." rashin samun amsa yasa kowacce taja bakinta ta tsuke.
Ina kuka ina bawa Inna hak'uri,bata saurare ni ba ta juya ta ci gaba da tafiya tana cewa "Idan har baki nemi inda y'ar uwarki take kin zauna tare da ita ba,kada ki sake kira na mahaifiyarki,ni ba mahaifiyarki bace,a kullum ina jin bak'in ciki na haifi y'a irin ki.."
Nace "Inna ki yi hak'uri dan Allah,nima fa duka ba laifi na bane,ki yarda dani,babanmu ya hana ni zuwa na dubasu."
Ta juyo ta kalle ni tana goge hawaye tace "Shi kenan,tunda kin yarda ya raba muku zumunci ki zauna tare da mahaifinki,in sha Allah ubangijin daya hallice mu ba zai tab'a barin Hauwa'u tayi maraici ba.. Daga yau ba zaki sake gani na ba,ki je ki zauna da mahaifinki.."
Tana gama fad'ar haka ta juya da sauri,ina kuka ina kiranta amma bata sake waiwayowa ba,jan jiki naci gaba da yi ina son bin hanyar da ta bi,saboda lokacin dana fad'i na ji ciwo sosai a k'afata,na kasa tashi na bita ina nan kwance ina kuka da kiranta har ta b'acewa ganina,cikin k'araji na kwalla kiran Inna,,a firgice na tashi ina dube²,na bud'e ido naga y'an uwanmu mata zagaye da ni sai kallona suke yi suna jiran su ji abunda ya faru na ke zabgaga ihu a farkon dare,na daure na juya ban yiwa kowa magana ba duk tarin tambayoyin da suke min,da suka ga ba ni da niyyar amsa musu kowacce ta juya ta kwanta,,a wannan daren ni dai ban samu damar komawa bacci ba har gari ya waye.
Misalin k'arfe 10am lokacin babanmu ya fita na shirya cikin damuwa,ba tare da sanin kowa ba na d'auki takardata na fita daga gida,na samu mai napep na fad'a masa inda zai kaini,yace na shiga ya san gurin,na shiga muka d'auki hanya,mintuna kusan talatin suka d'auke mu saboda baya wani sauri sosai muka k'araso,ya tsaya a dai² block d'in dana fad'a masa,ina ta tunanin halin da zan tarar da ita yace min "Hajiya mun k'araso."
Na kalli gurin da muke nace "Ka tabbata nan ne kuwa.!?"
Yace "Hajiya ai number za ki duba,ke kika fad'a min fa,ga gidan nan ki sake dubawa mana"
Na kalli house number sosai na duba ta jikin takarda,na ga iri d'aya ce babu bambanci,na sake kallon tsarin gidan na tabbatar nan ne inda ta rubuta,na sauka na biya mai napep kud'insa sannan na juya na kalli gidan,zuciyata har lokacin cike taf da tunanin anya nan d'in ne.!? Ina wannan tunanin na tunkari get d'in gidan,na yi shahada nayi knocking ina tunanin ganin ta inda Hauwa zata b'illo amma sai naji shiru,har kusan mintuna goma ban ji motsin kowa ba bare na ga mutum,nayi tunanin sake kwankwasawa amma wannan karon sai na tab'a entrance d'in,abun mamaki ashe k'ofar a bud'e take duk tsaiwar da nake yi,da mamaki sosai akan fuskata na kalli unguwar da nake jinta shiru sannan na wuce ciki na fara tafiya ina yi ina kallon ikon Allah da mamakin yadda aka yi Rafeek yayi mata kyautar gida kamar wannan,har na k'araso varenda da zata sada ni da parlor,na tsaya ina jin fargaba,a zuciyata ina addu'ar Allah yasa lafiya,na daure nayi knocking door d'in kusan mintuna uku shiru babu wani amsan da na samu,na sake yin knocking abun mamakin babu alamun mutum yana rayuwa a cikin gidan,gabana ya fad'i dana tuno kalamanta na ji hawaye suna k'ok'arin wanke min fuska,na nemi guri na zauna na ci gaba da addu'ar Allah yasa ba mutuwa Hauwa tayi ta barni ba,after 2 hours na goge hawaye idanuna duk sun kumbura,na mik'e da niyyar tafiya jikina duk yayi sanyi,na sakko daga saman varenda na kama hanyar get zan bar gidan,ina tafiya ina waiwaye,na yi nisa cikin hukuncin ubangiji na jiyo kamar sautin tari,da sauri na tsaya ina kalle² da tunanin ta ina sautin yake fitowa,amma kuma sai na rasa ina ne,na dawo da sauri na fara bin windows d'in da suke zagaye da gidan,duk window da na nufa sai na tarar da ita a rufe,idan na lek'a bana iya ganin komai saboda curtains dake zagaye da su duka masu duhu ne,nayi ta zagayawa kasancewar ginin gidan detached house ne da baiyi joining ko wane wall ba,irin ginin nan dai kawai da ake yinsa a tsakiya,na kusa gama zagaye gidan ina neman hanyar da zan shiga,dai² lokacin dana gama fitar da tsammani da samun mafita ubangiji ya taimake ni ya ji k'aina.
Window ne guda d'aya daga can edge na k'arshe na gidan a bud'e,har ina had'awa da gudu na k'arasa jikinsa na tsaya ina addu'ar Allah yasa abunda zuciyata take sanar da ni ya kasance gaskiya,sai dana gama addu'o'i na sannan nayi k'arfin hali na kai hannuna jikin windowpanes d'in ina k'ok'arin bud'ewa,kasancewar da yawa windows dana bari a baya na yi gwada bud'ewa ban samu dama ba,sai wannan da alamu suka nuna a bud'e take,ina janyowa ta bud'e na runtse idanuna cikin fargaba,curtains d'in da suka rufe ba'a ganin komai nasa hannu ina k'ok'arin bud'ewa duka,a nan idanuna suka yi bak'in gani.....
#Share pls.
#Real Smasher.
💠💠💠💠💠
*©®2020.*
*'DAN MACE..*
(Tʜᴇ ᴘꜱʏᴄʜɪᴀᴛʀɪꜱᴛ)..💥
*WATTPAD:REAL-SMASHER898.*
https://my.w.tt/29u2S26SG2
*Wah! 😍 U people are killing me with ur warmth comments,thank u so very much,thank u all my friends..Bahot² shukhurya..*♥
Pᴀɢᴇ 12.
#Iɴꜱᴀɴɪᴛʏ
Akan Hauwa idanuna suka fara sauka,kwance take amma cikin wani irin yanayi mai ban tsoro da firgitarwa,na koma baya da sauri cikin tsananin tashin hankali har ban san lokacin da na fasa k'ara ba,ta juyo ta kalli inda taji ihun bata ga kowa ba,ta juyar da kanta babu damuwar komai a ranta,nayi kuka sosai har sai da naji na sire bana iya sake yin hawaye,guiwoyina sun yi sanyi bayan na bawa zuciyata hak'uri na sake matsawa jikin window ina ta kallonta a hankali cikin muryar mai kashe jiki na kira sunan ta "Hauwa'u.!"
Ta juyo da sauri ta kallo inda nake,a hankali ta k'uramin ido kamar mai son tuna wace ce ni,na daure duk da hawayen da suke bin fuskata nace "Me ya same ki kika dawo haka.!?"
Ta yi shiru ta ci gaba da kallo na ba tare da ta ce komai ba,ina kuka nace "zo maza ki bud'e min k'ofa,ni ce y'ar uwar ki,ban san haka rayuwarki zata dawo ba,ki gafarce ni y'ar uwata,da na san haka al'amarin nan zai kasance tabbas ba zan tab'a bari kiyi nisa da ni ba,sai dai duk abunda zai faru ya faru,ki yimin afuwa k'anwata,ba a son raina haka ta faru ba.."
Still bata motsa daga inda take ba,ta yi shiru dai ta zuba min idanunta,duk abunda nake fad'a tana saurare na,sai dai alamu sun gwada gaba d'aya bata fahimtar abunda nake cewa,nayi magana nayi begging d'inta amma kusan duka a banza babu wanda ta ji,bare ta aikata.
Yinin ranar ya kasance a nan na yi shi ina yawo tsakanin harabar gidan da window d'in d'akin da take,har dare ya fara gabatowa ban samu damar shiga cikin gidan ba,wajen misalin k'arfe goma saura mintuna na sake komawa inda take,har lokacin tana nan kamar yadda na barta,na tsaya ina kallonta da tausayawa nace "Hauwa.!"
Jin magana yasa tayi sauri ta waiwayo tana kallona,na daure nace "Zanje gida na tattaro kayana,in sha Allah ina nan dawowa ba da jimawa ba kin ji.!?"
Kamar ta fahimci abunda nake nufi ta juyar da kanta ta k'urawa guri d'aya ido,cikin yanayin sanyin jiki na janyo k'afafuna na fito,ta waje na samu cable na d'aure get d'in sannan na kama hanya ina tafe ina gabana sai fad'uwa yake,a haka na fara neman abun hawa,da kyar lokacin 11pm saura mintuna 15 na samu napep,na fad'a masa inda zai kai ni,yace na hau mu tafi,na shiga muka fara tafiya,Allah ya taimake ni na samu irin masu napep d'in zamani,gudun da muka yi a lokacin ni na san ba kadan bane,11:00pm muka tsaya a k'ofar gidanmu,na sauka na sallami mai napep,na wuce cikin gida gabana yana ci gaba da fad'uwa,saboda ban san me zan tarar ba.
***
Abunda ya faru gidan mu kuwa a yinin ranar,bayan fita ta daga gida,ban san wane ne ya fad'awa Baba na fita ba,ya saba baya dawowa da wuri amma ranar after Maghreb Baba ya dawo ya fara jkran yaga ta inda zan b'illo,har 11:00pm saura mintuna bai ganni ba bai kuma samu labarin inda na mak'ale ba,dai² lokacin da agogo ya nuna 11pm Baba ya kira babban yayanmu Abdullahi yace yaje ya rufe masa k'ofar gidansa,yayanmu ya taho da niyyar rufe k'ofa kamar yadda Baba yayi masa umarni muka gamu a zaure,ya kalleni ya wuce ba tare da yace min komai ba,na wuce cikin mutuwar jiki saboda irin kallon da naga yayanmu yayi min na k'araso tsakar gida,nayi sallama babu wanda ya amsa,na kallesu d'aya bayan d'aya naga ni suke kallo,nayi ajiyar zuciya ina k'ok'arin wucewa suka fara gulma a tsakaninsu suna tambayar juna "Ko daga ina take da wannan talatainin daren.." rashin samun amsa yasa kowacce taja bakinta ta tsuke.