Sashe 96
Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Idan muka koma 6angaren zahra, tun wuraren ƙarfe shidda Mahboob Ya shigo mata da jakar kuɗin motarta da wayar da aka saida mata, shaf shaf ta shirya cikin jallabiya ta yafa mayafi akanta, tace da mahboob ya taimaka ya kaita gidan Hajiya falmata, yace zai kaita amma bisa sharadin zata bashi nashi kason, tunda ai yayi mata ƙokari, a lokacin taƙagara da taje tace mashi ta amince su tafi kawai, kafin su bar gidan saida ta fara cire miliyan ɗaya ta ajiye su cikin drawer, ya rage saura 3m dai dai kuɗin da zata bata.
Tana zaune a back seat na motar mahboob, yayin da shi kuma yake zaune a mazaunin driver, a tsanake yake yin driving har Allah Ya kawo su gidan Hajiya falmata.
A parking space mahboob yai parking din motar yace da ita ta shiga yana jiranta, ta amsa mashi da toh, ta buɗe motar ta fito ta nufi ƙofar shiga babban falon gidan”
Murmushin gefen fuska Mahboob ya dan saki yayin da yake bin Bayan zahra da kallo, ya zuro ƙafarshi daga cikin motar daya bar murfinta abuɗe
Wayarshi ce tayi ringing daga cikin aljihu da sauri Ya zura hannu ya duba mai kiranshi sunan Aunty Aneelerh ne Ya bayyana
Picking call din yai ya kara wayar a kunne”Babbar yayanmu, mun karaso gidan fa, Yau zahra zata sha mamaki, wallahi bakiga yadda take ta zubda uban gumi ba, kamar wadda tayi ma sarki ƙarya fadawa suka kamo ta” tuntsirewa yayi da dariya,
Muryar Aneelerh da sautin dariya tace”baiwar Allah, ina fata yau hankalinta zai kwanta, naji daɗi da nasarar da muka samu, ubangiji Allah Ya ƙara tsare mata ita” ya amsa mata da ameen
Ta kuma cewa”Idan kuka dawo gida, ka faɗa mata cewa motarta da wayarta jingina ka bada su, idan tanaso ta baka kuɗin za’a dawo mata da su, sannan please bana so tasan cewa jiya munje gidan hajiya falmata, ya amsa mata da toh, daga haka sukayi sallamar.
Tun da zahra ta shiga gidan, takasa zama, tana a tsaye tana jiran fitowar hajiya falmata don ta miƙa mata kuɗinta, mai aikin gidan ce ta fito daga part din dakin nata ta dubi zahra”ki zauna mana gatanan fitowa” galla mata harara zahra tayi’ba zama nazo yi ba” murmushi mai aikin tasaki kafin ta wuce ta nufi kitchen
Jim kaɗan, Hajiya falmata ta sauko down stairs, sleeping dress ne a jikinta riga da wando ta yafa mayafi akanta.
Fuskarta babu walwala ta dubi zahra”zauna mana” tayi maganar tana nuna mata sofa
Harara zahra ta watsa mata”ba zama nazo yi ba, kuɗinki na kawo maki” tayi maganar a fadace ta ajiye mata jakar gaban kujerar da take a zaune
Har ta juya zata fita muryar hajiya falmata ta katse mata hanzarinta
“Zahra! Dan Allah ki zauna inaso muyi magana badan halina ba”
Batayi mata gardama ba tace”dan kin haɗani da Allah, shiyasa zan zauna badan haka ba wallahi ko kallo baki ishe ni ba” murmushi hajiya falmata tasaki.
Bayan zahra ta zauna tana faman haɗe rai tace”ina sauraronki sauri nake yi in tafi”
“Nasan zakiyi mamaki zahra, kuma ba lallai ki yarda da abunda zan faɗa maki ba, abunda Ya faru a tsakanina dake badagaske bane, jarabaki nayi saboda wani dalili nawa....” da mamaki zahra take dubanta, jinjina kai hajiya falmata tayi”tabbas ba halina bane, nayi ƙoƙarin jan ra’ayinki ne don insan dawa ƴata take tarayya”
Tunkan ta kare maganar zahra tasaki dariyar rainin wayau tana fadin”dallah malama dakata! Banason zancen banza, harni zaki raina ma wayau? Ki gama zubda mutuncinki agabana kuma ki dawo kina fadin jarabani kikayi akan me kenan? A tsiwace ta furta hakan
Numfasawa hajiya falmata tayi”zahra dalilin dayasa nayi maki hakan, Mun samu sabani nida wata aminiyata hajiya naja’at akan ƴarta dake bin mata, ta laƙafa mun sharrin cewa ƴata fatima ce ta koya mata, saboda ita kaɗaice suke tarayya, sannan ita taba yarta tarbiya tasan bazata ta6a aikata hakan ba, faɗa sosai mukayi da ita, ta zageni taci mutuncina, damuwar duniya ta isheni, lokacin dana dawo gida narasa ya zanyi in tuhumi fatima saboda nima ina tsoron ace ƴata tana aikata kalar abunda Yarinyar aminiyartawa take yi, nasan zaiyi wuya fatima ta faɗa min gaskiya, kinji dalilin dayasa na yanke shawarar yi maki hakan saboda nasan ke kaɗaice aminiyar fatima, duk wani abu da zatayi saida shawararki, atare kuke yin komai, Ni a tunanina ta hanyar dana 6ullo maki zan samu abunda nake nema na gano abunda ƴata take aikawata ashe ba haka bane nayi babban kuskure zahra, dan Allah Ki yafe min” fashewa tayi da kuka hawaye nabin fuskarta, baiwar Allah zahra tuni zuciyarta ta karya, sam bata kawo komai aranta ba, ta yadda da kalaman hajiya falmata, cikin shessheƙar kuka tace”Amma meyasa zaki yi jarabawar dani? Kin hanani bacci kin hanani cin abinci, kin jefa rayuwata cikin matsanancin tashin hankali, babban abun takaicina shine karya min zuciya da kikayi saboda na ɗauke ki tamkar mahaifiyata ina ganin girmanki, ashe dama duk plan ne kika shirya min”?
Hajiya falmata na matsar ƙwalla tace”kiyi hakuri zahra nasan ban kyauta maki ba, dan Allah ki rufe min asiri kada kowa Yaji maganar nan, saboda banaso ayi tsammanin nima ina aikatawa ne sannan, maganar kuɗin da nake binku ni tuntuni na yafe maku, wallahi na bar maku su babu abunda zanyi dasu, sannan maganar yin order na kaya daga dubai in sha Allah gobe zasu iso Nigeria, inaso kuci gaba da gudanar da aikinku a companyna ke da fatima, don bazanso in rasa mace mai nagarta da tawakkali irinki ba, komai kuke so zanyi maku zahra, ni dai fatana ki manta da duk wani abu daya faru a tsakanina dake, Ki cigaba da daukata tamkar mahaifiyarki”
Rushewa zahra tayi da kuka, kamar ranta zai fita, bata ta6a tsammanin komai zai zo mata da sauƙi ba, harta fidda ran cigaba da aiki a companynsu da kuma damar zuwa obie estate ashe da rabon mafarkin ta ya zama gaskiya.
Cikin shessheƙar kuka tace”In sha Allah mommy babu wanda zaiji maganar nan, komai Ya wuce amma dan Allah kada ki ƙara yi min wasan nan, ni kaɗai nasan raɗaɗin da naji acikin zuciyata”
Jinjina kai hajiya falmata tayi da karyayyar murya tace”bazan ƙaraba zahra, nima nayi danasani, dan Allah ki tsaya mu yi breakfast atare kada kice zaki tafiya”
Zahra tace”sauri nake yi wata rana zan dawo, Ina fatima take”? Hajiya falmata tace”bata nan, jiya ta tafi gidan uncle dinta amma yau zata dawo saboda aikin da zakuyi tare” murmushin farin cikine Ya bayyana akan fuskar Zahra, sai faman washe bake takeyi harta fara tunanin irin rashin mutuncin da zatayi ma Aneelerh idan ta koma gida,
Godiya sosai hajiya falmata tayi mata, itama zahra tayi mata godiya da fara’a suka rabu.
Ta ruƙo jakar kuɗinta a hannu, tana fitowa daga falon da gudu ta nufi motar mahboob tana dariya haɗi da yin rawa tana jujjuya,
Mahboob tamkar baisan komai yace”zahra kin haukace ne? Lafiya kike dariya kamar wadda ta zauce ga hawaye akan fuskarki” da sauri ta share hawayen da gyalen jallabiyarta
Tace dashi”bro ka tayani murna yau ina cikin farin ciki, amma fa kada ka tambayeni meyasani shiga yanayin nan”
Mahboob na murmushi yace”shakuruminki aini ba ɗan jarida bane da zan tsareki da tambaya, Yanzu dai shiga mota muje gida muyi magana akan haƙƙina,”
Da farin ciki tace”ai mahboob kamar yadda Allah Ya rufa min asiri kaima zan rufa maka asiri, kai dai muje gidan” ta faɗa haɗi da shiga motar, ya tada suka nufi Hanyar komawa gida.
*EX-PRISONERS🥳*
*At abuja Nigeria🛬*
Alhamdulillah Matafiya sun samu damar sauka Lafiya basu wayi gari ba sai acikin Katafaren Luxury Villa Mallakin Chief Owais sharafuddeen Obinna! haɗaɗɗiyar Daular arzƙi ce wadda zamu Iya kiranta da Aljannar duniya saboda Kayan alatun dake acikin ta, Katafaren gini ne mai girman gaske ta 6angaren tsayi da faɗi Yana ɗauke da Sassa Uku acikinsa, a ɗaya daga cikin Part din gidan aka yima Prisoners masaukinsu, A hankali nake bin ginin da kallo domin in ƙarasa ga cikinsa, ta ko’ina na kalla ƙyalƙyalin gilassai ne suke kashe min idona da kyawunsu, wasu irin haɗaɗɗun floor-to-ceiling Glass windows ne masu mamaye bango, daga ƙasa har sama glass ne, Kana Iya hangen Katafaren Main falo din dake acikin sashen ta glass windows din, Ga wasu sliding doors ƙofofi masu zuge kansu da zarar sun gama tantance mutun saboda gidan Yana da mugun tsaro ba iya mutane ba hada na’urori ke sarrafa shi, ba za ka ta6a Iya ƙetare Gingirimeman entry way din gidan ba tare da An tantance ka ba, daga ƙasa har sama, bana tunanin ko aljani zai Iya shiga salin alin ba tare da na’ura ta haska shi ba, salon kuma ace nayi karya (😂)
Tana zaune a back seat na motar mahboob, yayin da shi kuma yake zaune a mazaunin driver, a tsanake yake yin driving har Allah Ya kawo su gidan Hajiya falmata.
A parking space mahboob yai parking din motar yace da ita ta shiga yana jiranta, ta amsa mashi da toh, ta buɗe motar ta fito ta nufi ƙofar shiga babban falon gidan”
Murmushin gefen fuska Mahboob ya dan saki yayin da yake bin Bayan zahra da kallo, ya zuro ƙafarshi daga cikin motar daya bar murfinta abuɗe
Wayarshi ce tayi ringing daga cikin aljihu da sauri Ya zura hannu ya duba mai kiranshi sunan Aunty Aneelerh ne Ya bayyana
Picking call din yai ya kara wayar a kunne”Babbar yayanmu, mun karaso gidan fa, Yau zahra zata sha mamaki, wallahi bakiga yadda take ta zubda uban gumi ba, kamar wadda tayi ma sarki ƙarya fadawa suka kamo ta” tuntsirewa yayi da dariya,
Muryar Aneelerh da sautin dariya tace”baiwar Allah, ina fata yau hankalinta zai kwanta, naji daɗi da nasarar da muka samu, ubangiji Allah Ya ƙara tsare mata ita” ya amsa mata da ameen
Ta kuma cewa”Idan kuka dawo gida, ka faɗa mata cewa motarta da wayarta jingina ka bada su, idan tanaso ta baka kuɗin za’a dawo mata da su, sannan please bana so tasan cewa jiya munje gidan hajiya falmata, ya amsa mata da toh, daga haka sukayi sallamar.
Tun da zahra ta shiga gidan, takasa zama, tana a tsaye tana jiran fitowar hajiya falmata don ta miƙa mata kuɗinta, mai aikin gidan ce ta fito daga part din dakin nata ta dubi zahra”ki zauna mana gatanan fitowa” galla mata harara zahra tayi’ba zama nazo yi ba” murmushi mai aikin tasaki kafin ta wuce ta nufi kitchen
Jim kaɗan, Hajiya falmata ta sauko down stairs, sleeping dress ne a jikinta riga da wando ta yafa mayafi akanta.
Fuskarta babu walwala ta dubi zahra”zauna mana” tayi maganar tana nuna mata sofa
Harara zahra ta watsa mata”ba zama nazo yi ba, kuɗinki na kawo maki” tayi maganar a fadace ta ajiye mata jakar gaban kujerar da take a zaune
Har ta juya zata fita muryar hajiya falmata ta katse mata hanzarinta
“Zahra! Dan Allah ki zauna inaso muyi magana badan halina ba”
Batayi mata gardama ba tace”dan kin haɗani da Allah, shiyasa zan zauna badan haka ba wallahi ko kallo baki ishe ni ba” murmushi hajiya falmata tasaki.
Bayan zahra ta zauna tana faman haɗe rai tace”ina sauraronki sauri nake yi in tafi”
“Nasan zakiyi mamaki zahra, kuma ba lallai ki yarda da abunda zan faɗa maki ba, abunda Ya faru a tsakanina dake badagaske bane, jarabaki nayi saboda wani dalili nawa....” da mamaki zahra take dubanta, jinjina kai hajiya falmata tayi”tabbas ba halina bane, nayi ƙoƙarin jan ra’ayinki ne don insan dawa ƴata take tarayya”
Tunkan ta kare maganar zahra tasaki dariyar rainin wayau tana fadin”dallah malama dakata! Banason zancen banza, harni zaki raina ma wayau? Ki gama zubda mutuncinki agabana kuma ki dawo kina fadin jarabani kikayi akan me kenan? A tsiwace ta furta hakan
Numfasawa hajiya falmata tayi”zahra dalilin dayasa nayi maki hakan, Mun samu sabani nida wata aminiyata hajiya naja’at akan ƴarta dake bin mata, ta laƙafa mun sharrin cewa ƴata fatima ce ta koya mata, saboda ita kaɗaice suke tarayya, sannan ita taba yarta tarbiya tasan bazata ta6a aikata hakan ba, faɗa sosai mukayi da ita, ta zageni taci mutuncina, damuwar duniya ta isheni, lokacin dana dawo gida narasa ya zanyi in tuhumi fatima saboda nima ina tsoron ace ƴata tana aikata kalar abunda Yarinyar aminiyartawa take yi, nasan zaiyi wuya fatima ta faɗa min gaskiya, kinji dalilin dayasa na yanke shawarar yi maki hakan saboda nasan ke kaɗaice aminiyar fatima, duk wani abu da zatayi saida shawararki, atare kuke yin komai, Ni a tunanina ta hanyar dana 6ullo maki zan samu abunda nake nema na gano abunda ƴata take aikawata ashe ba haka bane nayi babban kuskure zahra, dan Allah Ki yafe min” fashewa tayi da kuka hawaye nabin fuskarta, baiwar Allah zahra tuni zuciyarta ta karya, sam bata kawo komai aranta ba, ta yadda da kalaman hajiya falmata, cikin shessheƙar kuka tace”Amma meyasa zaki yi jarabawar dani? Kin hanani bacci kin hanani cin abinci, kin jefa rayuwata cikin matsanancin tashin hankali, babban abun takaicina shine karya min zuciya da kikayi saboda na ɗauke ki tamkar mahaifiyata ina ganin girmanki, ashe dama duk plan ne kika shirya min”?
Hajiya falmata na matsar ƙwalla tace”kiyi hakuri zahra nasan ban kyauta maki ba, dan Allah ki rufe min asiri kada kowa Yaji maganar nan, saboda banaso ayi tsammanin nima ina aikatawa ne sannan, maganar kuɗin da nake binku ni tuntuni na yafe maku, wallahi na bar maku su babu abunda zanyi dasu, sannan maganar yin order na kaya daga dubai in sha Allah gobe zasu iso Nigeria, inaso kuci gaba da gudanar da aikinku a companyna ke da fatima, don bazanso in rasa mace mai nagarta da tawakkali irinki ba, komai kuke so zanyi maku zahra, ni dai fatana ki manta da duk wani abu daya faru a tsakanina dake, Ki cigaba da daukata tamkar mahaifiyarki”
Rushewa zahra tayi da kuka, kamar ranta zai fita, bata ta6a tsammanin komai zai zo mata da sauƙi ba, harta fidda ran cigaba da aiki a companynsu da kuma damar zuwa obie estate ashe da rabon mafarkin ta ya zama gaskiya.
Cikin shessheƙar kuka tace”In sha Allah mommy babu wanda zaiji maganar nan, komai Ya wuce amma dan Allah kada ki ƙara yi min wasan nan, ni kaɗai nasan raɗaɗin da naji acikin zuciyata”
Jinjina kai hajiya falmata tayi da karyayyar murya tace”bazan ƙaraba zahra, nima nayi danasani, dan Allah ki tsaya mu yi breakfast atare kada kice zaki tafiya”
Zahra tace”sauri nake yi wata rana zan dawo, Ina fatima take”? Hajiya falmata tace”bata nan, jiya ta tafi gidan uncle dinta amma yau zata dawo saboda aikin da zakuyi tare” murmushin farin cikine Ya bayyana akan fuskar Zahra, sai faman washe bake takeyi harta fara tunanin irin rashin mutuncin da zatayi ma Aneelerh idan ta koma gida,
Godiya sosai hajiya falmata tayi mata, itama zahra tayi mata godiya da fara’a suka rabu.
Ta ruƙo jakar kuɗinta a hannu, tana fitowa daga falon da gudu ta nufi motar mahboob tana dariya haɗi da yin rawa tana jujjuya,
Mahboob tamkar baisan komai yace”zahra kin haukace ne? Lafiya kike dariya kamar wadda ta zauce ga hawaye akan fuskarki” da sauri ta share hawayen da gyalen jallabiyarta
Tace dashi”bro ka tayani murna yau ina cikin farin ciki, amma fa kada ka tambayeni meyasani shiga yanayin nan”
Mahboob na murmushi yace”shakuruminki aini ba ɗan jarida bane da zan tsareki da tambaya, Yanzu dai shiga mota muje gida muyi magana akan haƙƙina,”
Da farin ciki tace”ai mahboob kamar yadda Allah Ya rufa min asiri kaima zan rufa maka asiri, kai dai muje gidan” ta faɗa haɗi da shiga motar, ya tada suka nufi Hanyar komawa gida.
*EX-PRISONERS🥳*
*At abuja Nigeria🛬*
Alhamdulillah Matafiya sun samu damar sauka Lafiya basu wayi gari ba sai acikin Katafaren Luxury Villa Mallakin Chief Owais sharafuddeen Obinna! haɗaɗɗiyar Daular arzƙi ce wadda zamu Iya kiranta da Aljannar duniya saboda Kayan alatun dake acikin ta, Katafaren gini ne mai girman gaske ta 6angaren tsayi da faɗi Yana ɗauke da Sassa Uku acikinsa, a ɗaya daga cikin Part din gidan aka yima Prisoners masaukinsu, A hankali nake bin ginin da kallo domin in ƙarasa ga cikinsa, ta ko’ina na kalla ƙyalƙyalin gilassai ne suke kashe min idona da kyawunsu, wasu irin haɗaɗɗun floor-to-ceiling Glass windows ne masu mamaye bango, daga ƙasa har sama glass ne, Kana Iya hangen Katafaren Main falo din dake acikin sashen ta glass windows din, Ga wasu sliding doors ƙofofi masu zuge kansu da zarar sun gama tantance mutun saboda gidan Yana da mugun tsaro ba iya mutane ba hada na’urori ke sarrafa shi, ba za ka ta6a Iya ƙetare Gingirimeman entry way din gidan ba tare da An tantance ka ba, daga ƙasa har sama, bana tunanin ko aljani zai Iya shiga salin alin ba tare da na’ura ta haska shi ba, salon kuma ace nayi karya (😂)