Sashe 32
Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Aunt Zainab, Kin tabbata ba wanda yasan kin shigo? Ina mommy da daddy ne”
“Layla tana a palour, mahaifin ka kuma Yana a garden shi da kawunka Musa” Jin hakan Yasa shi saukowa daga saman gadon shi Ya nufe ta, tsayawa yai suna fuskantar Juna.
“Ka faɗa min wani taimako ka ke so In yi maka? in sha Allahu babu abunda zai gagara, a shirye nake da in share maka hawayen ka”
Hannayen ta biyu ya ruƙo a cikin nashi gabanta sai faɗuwa ya ke yi, tsoronta kada wani daga cikin Iyayenshi ya faɗo ɗakin, muddin hakan ya faru zata ɗanɗani kuɗarta ne.
“Aunt Zainab I feel in my heart that she’s still alive! Tun bayan da abun ya faru I’ve never dreamed of her as dead, I’ve always seen her alive in my dreams.” tun kafin ya ƙarasa maganar ta katse shi “How could that be possible, Shureim? Mutumin da ya mutu ai baya dawowa and the dreams you’re having aren’t real Don’t believe what you see in your dreams.”
Fuskarshi a yamutse ya ke dubanta
“Amma ni inaji araina bata mutu ba!” kafe mata yai akan zancen shi
Ta fahimci ya fara zaucewa, Zaifi ta lalla6a shi don ta kwantar mashi da hankalin shi”shureim, idan ma tana araye da buƙatar mu shirya plan don mu tabbatar da abunda muke zargi,”
Jinjina mata kai yai alamar yana fahimtarta.
“Dole Ka bi duk a bun da zan faɗa maka,” amsa mata yai da in sha Allah, mu zauna sai muyi magana” girgiza mashi kai tayi”a’a ina tsoron Mahaifiyarka ta faɗo dakin nan, Just A tsaitsaye zan faɗa maka matakin da zaka ɗauka domin mu ci nasara akan binciken da zamu yi” zame hannunta tayi daga cikin nashi da sauri ta nufi ƙofar ɗakin ta leƙa tana duban ko’ina don kada wani ya faɗo masu, ganin bakowa yasa ta gyara labulan ɗakin nashi, ta juyo da sauri ta nufe shi Yayin da take cigaba da yin maganarta”mataki na farko shine Dole ka tanƙwashi zuciyarka, ka danne raɗaɗin da ka ke ji ka daina sanya damuwa aranka”
“Mataki na Biyu Ka daina gudun Iyayen ka, Ina nufin Ka koma masu tamkar yadda ku ke da su Ada, Biyayya sau da ƙafa, ka nemi yafiyarsu akan 6ata masu rai da ka ke Yi.....” tun kan ta kai ƙarshen maganar ta lura da canzawar da yai, a marairaice yace da ita”Aunty zainab taya zan iya yin hakan? Ni bana jin zan Iya sakar masu fuska mu koma kamar yadda muke ada” murmushi ta ɗan saki kafin tace”Shureim kenan, Nafi so ina magana kana fahimtata, ta wannan hanyarce kaɗai zamu Iya gano meke wakana a tsakanin Iyayenka” jinjina mata kai yai alamar ya fahimta.
Har ya buɗe baki zai yi Magana ya ji ta yi saurin katse shi da cewa
“Me ka ke buƙata in kawo maka? nasan kana jin Yunwa”
A ruɗe ya ke kallonta da mamaki Akan fuskarshi, Me ya kawo zancen yunwa acikin maganar su.
“Ko dai kana buƙatar chips in haɗo maka da shi”? Ta wutsiyar idon shi Ya hango Layla A tsaye bakin ƙofar, Ta kifa ɗaurin ɗan kwalin atampa akanta, Riga da skirt ne sun bi shape ɗin jikinta, duk da alamun manyantaka atattare da ita, hakan bai 6oye kyawun surarta ba.
Wahalallan Yawu ya haɗiya haɗi da sauke nauyayyar ajiyar zuciya, aranshi ya ayyana ko yaushe tazo bakin ƙofar! Sai yanzu ya fahinci dalilin canza maganar zainab, ita tun kafin layla ta shigo tajiyo takun takalmanta saboda bata sanya takalmi idan ba mai tsini ba, Ba don Allah yasa taji motsinta ba da ko ta yabawa aya zaƙin ta
“Aunty zainab wai meyasa ki ke son takurani akan dole sai naci abinci, nace maki bana jin yunwa ki tafi kawai, Ni bana buƙatar ganin kowa akusa da ni, ana dole ne” Ranshi a matuƙar 6ace yai maganar, tare da Juya mata baya, Ya ruƙe qugu da hannu ɗaya, Zainab dake kallon bayanshi tace”Shureim zama da yunwa zai Iya haifa maka wata matsalar, abunda bama fata, Ni bari naje na faɗawa mahaifiyar taka kaƙi cin abinci wataƙil idan ita tayi maka magana ka ci” Har zata Juyawa shureim Ya juyo a sukwane Ya daka mata tsawa”Karki Kuskura ki ce zaki haɗani da ita, Ko kin faɗa mata abanza, matar da bata damu da ci na ko sha na ba.....” Sai da yai wannan maganar, Layla ta kai hannu ta ɗan kwankwashi Jikin Ƙofar ɗakin nashi Don hankalinsu ya dawo kanta, tamkar basu san da zamanta ba suka ɗago suna kallonta, Fuskarta tasha uban make up, gashinta baki wulik har mid back ɗinta, Cikin takun izza da nuna isa Ta nufo su tana magana”Zainab Nagode da kulawarki akan ɗana, ki ƙyale shi, shureim ya daina jin maganar kowa a yanzu bansan laifin me mu ka yi mashi ba da yake gudun mu,’ tun da ta fara magana Zainab take sauke ajiyar zuciya, jin bata gano me suke tattaunawa ba, shureim ko sai ƙara ɗaure fuskarshi ya ke yi kamar zata fashe saboda tsabar nuna fusatarshi.
Idanuwan mahaifiyarshi akan fuskarshi, Cikin girmamawa zainab tace”Shureim har yanzu yaro ne, tun da yana a ƙarƙashin kulawarku, sai ana haƙuri dashi ana kuma lallashin shi da jan shi a jiki ta hakanne zamu iya sanin meke damun shi” jikinta na ɗan kerma tayi maganar, gyaɗa kai Layla tayi”is Okey, ba sai kin koyamin yadda zan Kula da ɗana ba, Ni da na haife shi ni nasan kayana, Zaki Iya tafiya ki bamu wuri” ta yi maganar tare da nuna mata ƙofa da hannu.
layla kenan Ita ba’a mata gwaninta, Jiki asanyaye zainab ta kama hanyar fita ɗakin tana tafiya tana waiwayon shureim da ido take Yi mashi alamar Ya sake mata, kada ya manta da shirinsu, Lumshe mata idon da yai ne yasa ta fahimci ya gane me take nufi, Bayan fitar zainab, Layla ta tsare shi da idanuwanta
“me zan yi maka wanda zaisa Ka daina guduna? Haba Shureim saboda na kore ka cikin fushi shine ka kama Hanya ka tafi egypt wurin Ammi, Kasa ta kirani awaya tana ta zazzaga min masifa, ‘ ranta a6ace take yin maganar, har ya harzuƙa zai mayar mata da martani kalaman zainab suka faɗo mashi arai da sauri ya danne fushinsa, abunda ta tsana dashi tana magana Yana shareta, Wuyan farar jallabiyar jikinshi ta damƙa da hannayenta waɗanda ke a sanye da awarwaro da zabba na zallar zinari, Jijjiga shi tai”Shureim so kake baƙin cikin ka ya kashe ni? Na rasa benazir kaima kuma kana neman ɗaura min hawan jini, so ka ke zuciyata ta buga in mutu shureim”? hankalin shi ba ƙaramin tashi yai ba, ganin hawaye sun ciko idonta.
Duk da yasan ta yi hakanne don ta samu kanshi, sassauta muryarta tayi tare da sakin Kwalar rigarshi”Kai kaɗai nake gani naji daɗi, Meyasa ba za ka manta da abunda yawuce ba, ina magana kana share ni, kasan bana son hakan, Yana ƙona min rai” baisan sa’adda hawaye suka cigaba da wanke fuskarshi ba, muryarshi na ɗan rawa ya furta”?mommy saboda ni za ki zubar da hawayen ki”? Muryarta a kausashe tace”Shureim, how many times have I cried for you? I understand that you’re trying to drive me crazy,” Shureim ka daina ƙaunata” Tai maganar tana watsa hannayenta’ shiru Ya ɗanyi yana kallon fuskarta, tabbas ya ga 6acin rai acikinta.
“Astagfurillah” jin ya ambaci haka Yasa ta zaro idonta akan fuskarshi
“Mommy, I didn’t know you cared about me that much, I thought you’d stopped loving me, amma yanzu mommy akaina kike zubar da hawayenki”?
Mamakin kalaman shi ne yasa ta kafe shi da ido ba ƙyaftawa, Hadisi Ya soma janyo mata da ayoyin al’kur’ani mai girma waɗanda ke magana akan wanda Ya ƙuntatawa iyayen shi.
“Shureim ka sani kuma kake take sani? Shine Ka rufe ido Kana ƙuntata min? Meyasa”? Marairaice mata fuska yai”ya zanyi! Sharrin zuciyane da kuma sharrin shaiɗan, sune suke azalzalar zuciyata akan abunda Ya faru, sunƙi bari na manta komai,” Dafa kafaɗar shi tai da hannunta ɗaya”Ka yafe min shureim, nayi maka alƙawarin zan tarairaye ka na baka kulawa kamar yadda muke ada, Sannan inaso kamanta da abunda ya wuce, Ba laifin mu bane, mu ne sila, amma kaine ka aikata komai ba tare da ka yi shawara damu ba, kai kasan ba yadda za’ai da hankalin mu da tunanin mu mu goyi bayanka akan aikata hakan, a lokacin da ace ka yi shawara damu wlh shureim ba zamu goyi bayan abunda ka aikata ba” har cikin zuciyarta ta ke magana, Shi kanshi Yaji jikinshi yai sanyi, zuciyar shi ta karaya, tabbas maganar da ta faɗi gaskiya ne.
“ Mommy, ni ne ya kamata na nemi yafiyarki, akan gudun ku da nake Yi ke da Daddy, Dan Allah ku yafe min, na gane kuskurena”
yai maganar yana ƙoƙarin zubewa saman gwiwowinsa da sauri ta ɗago da shi ta rungume shi tana ɗan bubbuga bayanshi da yatsun hannayenta, Farin ciki duk Ya cikata, ta manta when last ta ji ɗumin shureim a jikinta, saboda rashin jituwar dake a tsakanin su.
Muryar shi da alamun karaya ya furta mata”Mommy, ana ‘uhibuk kathiran” Hawayen da suka taru acikin idanuwanta ne suka soma gangarowa saman kuncin ta, still ba su raba jikinsu daga na juna ba, martanin maganarshi ta mayar mashi”i love u too My son, ba zan Iya misalta farin cikin da nake a ciki ba, Shureim ka faranta min rai,” ta yi maganar tare da raba jikinsu daga na juna, fuskokin su ɗauke da murmushin ƙauna
“Idan har dagaske mun shirya inaso daga yau ka goge duk wasu hotunanta dake a cikin wayarka, kallonsu baida amfani shureim, saboda suke fama maka raunin dake a cikin zuciyar ka”
Shiru yai yana kallon fuskarta, har sai da ta kai ƙarshen maganar, Har ga Allah bai jin zai Iya goge hotonta a wayarshi, don ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya suke yi ba aduk lokacin da ya kalle su, Allah ya jarabce shi da ƙaunarta, Yafi sonta akan kowa na duniyar nan, duk da bata araye.
Gudun kada ta zarge shi, yasa shi yin saurin cewa”saboda farin Cikin ki mommy zan yi deleting ɗinsu, ni kaina bana son abunda zai ƙara shiga tsakanina da ke,”
“Layla tana a palour, mahaifin ka kuma Yana a garden shi da kawunka Musa” Jin hakan Yasa shi saukowa daga saman gadon shi Ya nufe ta, tsayawa yai suna fuskantar Juna.
“Ka faɗa min wani taimako ka ke so In yi maka? in sha Allahu babu abunda zai gagara, a shirye nake da in share maka hawayen ka”
Hannayen ta biyu ya ruƙo a cikin nashi gabanta sai faɗuwa ya ke yi, tsoronta kada wani daga cikin Iyayenshi ya faɗo ɗakin, muddin hakan ya faru zata ɗanɗani kuɗarta ne.
“Aunt Zainab I feel in my heart that she’s still alive! Tun bayan da abun ya faru I’ve never dreamed of her as dead, I’ve always seen her alive in my dreams.” tun kafin ya ƙarasa maganar ta katse shi “How could that be possible, Shureim? Mutumin da ya mutu ai baya dawowa and the dreams you’re having aren’t real Don’t believe what you see in your dreams.”
Fuskarshi a yamutse ya ke dubanta
“Amma ni inaji araina bata mutu ba!” kafe mata yai akan zancen shi
Ta fahimci ya fara zaucewa, Zaifi ta lalla6a shi don ta kwantar mashi da hankalin shi”shureim, idan ma tana araye da buƙatar mu shirya plan don mu tabbatar da abunda muke zargi,”
Jinjina mata kai yai alamar yana fahimtarta.
“Dole Ka bi duk a bun da zan faɗa maka,” amsa mata yai da in sha Allah, mu zauna sai muyi magana” girgiza mashi kai tayi”a’a ina tsoron Mahaifiyarka ta faɗo dakin nan, Just A tsaitsaye zan faɗa maka matakin da zaka ɗauka domin mu ci nasara akan binciken da zamu yi” zame hannunta tayi daga cikin nashi da sauri ta nufi ƙofar ɗakin ta leƙa tana duban ko’ina don kada wani ya faɗo masu, ganin bakowa yasa ta gyara labulan ɗakin nashi, ta juyo da sauri ta nufe shi Yayin da take cigaba da yin maganarta”mataki na farko shine Dole ka tanƙwashi zuciyarka, ka danne raɗaɗin da ka ke ji ka daina sanya damuwa aranka”
“Mataki na Biyu Ka daina gudun Iyayen ka, Ina nufin Ka koma masu tamkar yadda ku ke da su Ada, Biyayya sau da ƙafa, ka nemi yafiyarsu akan 6ata masu rai da ka ke Yi.....” tun kan ta kai ƙarshen maganar ta lura da canzawar da yai, a marairaice yace da ita”Aunty zainab taya zan iya yin hakan? Ni bana jin zan Iya sakar masu fuska mu koma kamar yadda muke ada” murmushi ta ɗan saki kafin tace”Shureim kenan, Nafi so ina magana kana fahimtata, ta wannan hanyarce kaɗai zamu Iya gano meke wakana a tsakanin Iyayenka” jinjina mata kai yai alamar ya fahimta.
Har ya buɗe baki zai yi Magana ya ji ta yi saurin katse shi da cewa
“Me ka ke buƙata in kawo maka? nasan kana jin Yunwa”
A ruɗe ya ke kallonta da mamaki Akan fuskarshi, Me ya kawo zancen yunwa acikin maganar su.
“Ko dai kana buƙatar chips in haɗo maka da shi”? Ta wutsiyar idon shi Ya hango Layla A tsaye bakin ƙofar, Ta kifa ɗaurin ɗan kwalin atampa akanta, Riga da skirt ne sun bi shape ɗin jikinta, duk da alamun manyantaka atattare da ita, hakan bai 6oye kyawun surarta ba.
Wahalallan Yawu ya haɗiya haɗi da sauke nauyayyar ajiyar zuciya, aranshi ya ayyana ko yaushe tazo bakin ƙofar! Sai yanzu ya fahinci dalilin canza maganar zainab, ita tun kafin layla ta shigo tajiyo takun takalmanta saboda bata sanya takalmi idan ba mai tsini ba, Ba don Allah yasa taji motsinta ba da ko ta yabawa aya zaƙin ta
“Aunty zainab wai meyasa ki ke son takurani akan dole sai naci abinci, nace maki bana jin yunwa ki tafi kawai, Ni bana buƙatar ganin kowa akusa da ni, ana dole ne” Ranshi a matuƙar 6ace yai maganar, tare da Juya mata baya, Ya ruƙe qugu da hannu ɗaya, Zainab dake kallon bayanshi tace”Shureim zama da yunwa zai Iya haifa maka wata matsalar, abunda bama fata, Ni bari naje na faɗawa mahaifiyar taka kaƙi cin abinci wataƙil idan ita tayi maka magana ka ci” Har zata Juyawa shureim Ya juyo a sukwane Ya daka mata tsawa”Karki Kuskura ki ce zaki haɗani da ita, Ko kin faɗa mata abanza, matar da bata damu da ci na ko sha na ba.....” Sai da yai wannan maganar, Layla ta kai hannu ta ɗan kwankwashi Jikin Ƙofar ɗakin nashi Don hankalinsu ya dawo kanta, tamkar basu san da zamanta ba suka ɗago suna kallonta, Fuskarta tasha uban make up, gashinta baki wulik har mid back ɗinta, Cikin takun izza da nuna isa Ta nufo su tana magana”Zainab Nagode da kulawarki akan ɗana, ki ƙyale shi, shureim ya daina jin maganar kowa a yanzu bansan laifin me mu ka yi mashi ba da yake gudun mu,’ tun da ta fara magana Zainab take sauke ajiyar zuciya, jin bata gano me suke tattaunawa ba, shureim ko sai ƙara ɗaure fuskarshi ya ke yi kamar zata fashe saboda tsabar nuna fusatarshi.
Idanuwan mahaifiyarshi akan fuskarshi, Cikin girmamawa zainab tace”Shureim har yanzu yaro ne, tun da yana a ƙarƙashin kulawarku, sai ana haƙuri dashi ana kuma lallashin shi da jan shi a jiki ta hakanne zamu iya sanin meke damun shi” jikinta na ɗan kerma tayi maganar, gyaɗa kai Layla tayi”is Okey, ba sai kin koyamin yadda zan Kula da ɗana ba, Ni da na haife shi ni nasan kayana, Zaki Iya tafiya ki bamu wuri” ta yi maganar tare da nuna mata ƙofa da hannu.
layla kenan Ita ba’a mata gwaninta, Jiki asanyaye zainab ta kama hanyar fita ɗakin tana tafiya tana waiwayon shureim da ido take Yi mashi alamar Ya sake mata, kada ya manta da shirinsu, Lumshe mata idon da yai ne yasa ta fahimci ya gane me take nufi, Bayan fitar zainab, Layla ta tsare shi da idanuwanta
“me zan yi maka wanda zaisa Ka daina guduna? Haba Shureim saboda na kore ka cikin fushi shine ka kama Hanya ka tafi egypt wurin Ammi, Kasa ta kirani awaya tana ta zazzaga min masifa, ‘ ranta a6ace take yin maganar, har ya harzuƙa zai mayar mata da martani kalaman zainab suka faɗo mashi arai da sauri ya danne fushinsa, abunda ta tsana dashi tana magana Yana shareta, Wuyan farar jallabiyar jikinshi ta damƙa da hannayenta waɗanda ke a sanye da awarwaro da zabba na zallar zinari, Jijjiga shi tai”Shureim so kake baƙin cikin ka ya kashe ni? Na rasa benazir kaima kuma kana neman ɗaura min hawan jini, so ka ke zuciyata ta buga in mutu shureim”? hankalin shi ba ƙaramin tashi yai ba, ganin hawaye sun ciko idonta.
Duk da yasan ta yi hakanne don ta samu kanshi, sassauta muryarta tayi tare da sakin Kwalar rigarshi”Kai kaɗai nake gani naji daɗi, Meyasa ba za ka manta da abunda yawuce ba, ina magana kana share ni, kasan bana son hakan, Yana ƙona min rai” baisan sa’adda hawaye suka cigaba da wanke fuskarshi ba, muryarshi na ɗan rawa ya furta”?mommy saboda ni za ki zubar da hawayen ki”? Muryarta a kausashe tace”Shureim, how many times have I cried for you? I understand that you’re trying to drive me crazy,” Shureim ka daina ƙaunata” Tai maganar tana watsa hannayenta’ shiru Ya ɗanyi yana kallon fuskarta, tabbas ya ga 6acin rai acikinta.
“Astagfurillah” jin ya ambaci haka Yasa ta zaro idonta akan fuskarshi
“Mommy, I didn’t know you cared about me that much, I thought you’d stopped loving me, amma yanzu mommy akaina kike zubar da hawayenki”?
Mamakin kalaman shi ne yasa ta kafe shi da ido ba ƙyaftawa, Hadisi Ya soma janyo mata da ayoyin al’kur’ani mai girma waɗanda ke magana akan wanda Ya ƙuntatawa iyayen shi.
“Shureim ka sani kuma kake take sani? Shine Ka rufe ido Kana ƙuntata min? Meyasa”? Marairaice mata fuska yai”ya zanyi! Sharrin zuciyane da kuma sharrin shaiɗan, sune suke azalzalar zuciyata akan abunda Ya faru, sunƙi bari na manta komai,” Dafa kafaɗar shi tai da hannunta ɗaya”Ka yafe min shureim, nayi maka alƙawarin zan tarairaye ka na baka kulawa kamar yadda muke ada, Sannan inaso kamanta da abunda ya wuce, Ba laifin mu bane, mu ne sila, amma kaine ka aikata komai ba tare da ka yi shawara damu ba, kai kasan ba yadda za’ai da hankalin mu da tunanin mu mu goyi bayanka akan aikata hakan, a lokacin da ace ka yi shawara damu wlh shureim ba zamu goyi bayan abunda ka aikata ba” har cikin zuciyarta ta ke magana, Shi kanshi Yaji jikinshi yai sanyi, zuciyar shi ta karaya, tabbas maganar da ta faɗi gaskiya ne.
“ Mommy, ni ne ya kamata na nemi yafiyarki, akan gudun ku da nake Yi ke da Daddy, Dan Allah ku yafe min, na gane kuskurena”
yai maganar yana ƙoƙarin zubewa saman gwiwowinsa da sauri ta ɗago da shi ta rungume shi tana ɗan bubbuga bayanshi da yatsun hannayenta, Farin ciki duk Ya cikata, ta manta when last ta ji ɗumin shureim a jikinta, saboda rashin jituwar dake a tsakanin su.
Muryar shi da alamun karaya ya furta mata”Mommy, ana ‘uhibuk kathiran” Hawayen da suka taru acikin idanuwanta ne suka soma gangarowa saman kuncin ta, still ba su raba jikinsu daga na juna ba, martanin maganarshi ta mayar mashi”i love u too My son, ba zan Iya misalta farin cikin da nake a ciki ba, Shureim ka faranta min rai,” ta yi maganar tare da raba jikinsu daga na juna, fuskokin su ɗauke da murmushin ƙauna
“Idan har dagaske mun shirya inaso daga yau ka goge duk wasu hotunanta dake a cikin wayarka, kallonsu baida amfani shureim, saboda suke fama maka raunin dake a cikin zuciyar ka”
Shiru yai yana kallon fuskarta, har sai da ta kai ƙarshen maganar, Har ga Allah bai jin zai Iya goge hotonta a wayarshi, don ba ƙaramin sanyaya mashi zuciya suke yi ba aduk lokacin da ya kalle su, Allah ya jarabce shi da ƙaunarta, Yafi sonta akan kowa na duniyar nan, duk da bata araye.
Gudun kada ta zarge shi, yasa shi yin saurin cewa”saboda farin Cikin ki mommy zan yi deleting ɗinsu, ni kaina bana son abunda zai ƙara shiga tsakanina da ke,”