← Book details Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 7 OF 152

Sashe 7

Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Baiwar Allah ga zazza6i mai zafi daya rufar mata, Jikinta sai kakarwa ya ke yi, ta gama fita hayyacinta, Neman hanyar da zata koma cikin ƴan uwanta ta ke yi saboda ta riga da ta sare da kurkukun, mutuwa ka ɗai ta ke gani acikin idanuwanta gashi ba ta son ta mutu ba tare da ta yi bankwana da ƴan uwanta ba.

Tsabar raɗaɗin da bakin ta ke yi mata ne ya jaza mata rauni da rashin kuzari a jikinta Ƙaffuwanta suka harɗe Gaba ɗaya ta kife saman floor, kanta ya daki ƙasa sosai, runtse idanuwanta ta yi yayin da hawaye ke cigaba da wanke fuskarta miryarta babu sauti take ambaton sunan ƴan uwanta tana neman taimakon su akan su zo su taimake ta, kada ta mutu ba tare da sun gana da junan su ba, Babu alamun hankali atattare da ita, sai sambatu ta ke yi ita kaɗai, Addu’o’in da ta ke ƙokarin yi yanzu sun kufce mata......

Sautin tafiya ta soma Ji kamar motsi motsi saman jikinta, a daddafe ta miƙe tana faman yin nishi, Ras taji gabanta Ya faɗi ganin wasu Girgizo kwafta kwafta a kewaye da ita, Tashin hankalin da ta shiga ne yasa ta fasa ƙara tare da yunƙurawa ta miƙe da gudun gaske ta miƙi hanya tana gudu tana waiwayon su gaba ɗaya sumar kanta mai tarin yawa ta rufe mata idanuwanta, Cikin rashin sa’a Ta 6urma cikin wani ɗaki tare da Jan ƙofa ta datse, ba tare da ta ankara da inda ta faɗo ba, Jikinta sai kerma ya ke Yi.

“Barka da zuwa Ɗakin Fiɗa, Ga dukkan Alamu mun samu wata sabuwar ma’aikaciyar” Muryar matashin saurayi taji acikin kunnanta, Tun kafin ta juya ta kalle su Jikinta ya hau tsuma, A furgice ta waiwaya tare da sanya hannu ta nannaɗe sumar kanta da ta rufe mata idanuwanta, Inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un bakomai ne yasa ta ambaton hakan ba face Matasan ƴan matan da ta gani kwance saman gadaje kalar na marasa lafiya, zindir babu kaya a jikin su hada masu Ɗauke da juna Biyu, gwanin ban tausayi, Giants ne tsaitsaye akansu Hannayensu ruƙe da kayan theater suna acikin shigarsu ta baƙaƙen Kaya.

“Ƴar uwa dan Allah ki taimake ni, ki fitar dani daga wurin nan kada su kashe ni” waro ido sosai Angel ta yi akan matar da ta yi mata magana, Ita ce mai ɗauke da juna biyu Daga ganin cikinta tsoho ne Ya shiga wata na tara. Sun tu6e mata kaya tsiraicinsu duk abayyane, Wannan wata irin masifa ce? Hasbunallahu wa’ni e mal wakeel Lahaula wala ƙuwata Illa Billah, Allahumma ajirni fil musibati wa aklif ni khairan min ha,’ adabarbarce Angel ta ke ambaton hakan. Matar sai kuka take yi tana rokonta akan ta taimake ta ko dan saboda yaron da ke a cikinta, rushewa Angel ta yi da kuka ba tare da ta Iya furta magana ba.

Ɗaya daga Cikin Giant ɗin dake a ɗakin tiyatar ne Ya tunkarota Hannun shi ruƙe da wuƙa, Tunkan yai magana ta fahimci abinda ya ke nufi, aiko Jiki na 6ari ta juya tana ƙoƙarin buɗe ƙofar ɗakin don ta gudu, sai dai ina kafin ta yi hakan ta ji Ya damƙi hannunta, ruƙo bana wasa ba, ta ƙarfi ya dinga janta har sai da ya kai ta bakin gadon da matar nan me ciki take kwance.

Zura mata wuƙar ya yi a cikin hannunta Ya damƙe shi da nashi hannun, Ta ƙarfi ya soma ƙoƙari sanyata farke cikin matar, Kamar zata zauce saboda tsabar kiɗima har Allah ta dinga roƙo akan ya ɗauki ranta kafin faruwar hakan, Bata ta6a danasanin zuwanta duniya ba sai yau, ta yi fatan ace bata ta6a wanzuwa acikinta ba, ta yi kuka kamar ranta zai fita tayi haukan tayi borin duk abanza, ta ƙarfi giant din nan ya ɗaura hannunta saman cikin matar nan da ke ta kuka tana roƙonta akan ta taimake ta, Saboda rashin imani Ya yi amfani da hannun Angel wurin farke cikinta Kamar an fasa pipe ɗin ruwa Haka jini yadinga tsastsafowa yana wanke fuskar Angel har ta cikin bakinta ya dinga fallasa yana shiga.

Hatta jaririn da ke acikinta bai tsiri ba, Biyu suka raba shi da wuƙar, Allah sarki Angel Gani ta yi kamar ita ta aikata kisan kan, Wata irin kururuwa ta saki da iya ƙarfinta na karshe ta bangaje giant ɗin da ke a ruƙe da ta ita Amakance ta dinga Tafiya tana neman Hanyar fita, muryarta da sautin kuka ta ke faɗin.

“Nashiga Uku na bani na lalace Inalillah wa’inna ilaihirraji’in Na aikata kisan kai! na yi kisa da hannayena Shikanen Na mutu, nasan Allah ba zai ƙyale ni ba, Na kashe mashi baiwarshi da bata ji ba bata gani ba, Wayyo Allah Na......”

Yatsun hannayenta ta ɗaura asaman kanta kamar Aljanna Jinin matar duk ya canza mata kamanninta, duhu ya mamaye idanuwanta da zuciyarta.

Giants ɗin da ke Yin aikin fiɗar sai tiƙar dariya su ke Yi, Hankalinsu kwance su ke Cigaba da gudanar da aikin su, yadda su ke farke cikin mutun kamar dabba babu imani ko misƙala Zarratin.

Da wata irin raunatacciyar murya ta ke faɗin”Allah ba zai ta6a barin ku ba, Mugaye Azzalumai, Tun agidan duniya za ku fara gir6ar abunda ku ka shuka ƴan iska fasiƙai masu zuciya irin ta kafuran farko, In sha Allah Ni ce Ajalin ku, Sai kun ɗanɗani kuɗar ku sai kun gane ba ku da wayau, kamar yarda kuka sa na zubar da hawaye na in sha Allah kuma za ku zubar da naku hawayen Na jini ma, Yadda ku ka cutar dani ku ka sa na aikata kisa kuma sai an yi maku mafiyin shi......” ƙululun baƙin Cikine ya tokare maƙoshinta, silar hakan yasa ta kasa ƙarasa maganar.

Hannayen ta biyu ta sanya saman wuyanta, ta shaƙe shi sosai cikin fitar hayyaci kamar zata kashe kanta, tsabar raɗaɗin da ƙunar da zuciyarta ke yi mata ne yasa ta ke ƙokarin aikata hakan, tana a cikin wannan mawuyacin halin taji An sunkuce ta kamar Ɗiyar roba haka aka ɗauke ta sama, wani gabjejen giant ne yai mata wannan ɗaukar, fucewa yai da ita daga Cikin ɗakin Ɗauke saman kafaɗarshi bai nufi ko’ina da ita ba sai cikin wannan Ƙaton palourn Da taron matsafa su ke gudanar da Bautar su, Wasu dogayen mutane masu sanye da jajayen kaya ko’ina na jikin su arufe ya ke, sun kai su talatin, Agaban dodon tsafin su, Anan Ya sauke ta saman floor, a durƙushe ta kife kasa saboda rashin ƙwarin Jikinta, Hatta numfashinta a hargitse yake fita Jikinta yai zafi rau kamar wadda aka tsomo daga cikin wuta.

A lokacin ta kai maƙura bata iya ta6uka komai, motsin hannun mutun ta ji ajikinta, saboda duhun da idanuwanta su ka yi mata yasa ta makance, bata ganin komai, kayan Jikinta suka cire mata gaba ɗaya iya pant ɗin ta su ka bar mata, duk da bata acikin hayyacinta sai da ta shiga matsanancin tashin hankali tunawa da robar ruwan zamzam ɗin da ke a cikin wandonta, rarrafe ta dinga tana laluban suturarta don ta mayar dasu a jikinta sai dai kash bata samu damar ganin inda aka jefa mata kayanta ba. Kukan zuci ta dinga yi, duk wani motsinta akan idon matsafan, ita damuwarta ba akan tsiraicinta da suke kallo ba, robar ruwan Zam zam ce damuwar ta, Ya za ta yi idan ta rasa ta? Ita kaɗai ce damar da suke da ita.

Kunnuwata ne suka soma Jiyo mata Sautin muryoyinsu Marasa daɗin ji magana su ke yi da yaren su na matsafa gur6ataccen yare mara daɗin ji, kamar zata haukace, Lallai yau Angel ta shaida tana acikin kurkukun ƙaddara.

Ƙwaryoyin ne ruƙe a hannun matsafan masu ɗauke Da zallar Jinin mutane mai ƙarni, Layi suka jera agabanta suka tsaya tare da Kwarara mata Jinin A saman kanta, Wa’iya zubillah Numfashinta ya gauraye da Ƙarnin Jinin Nan ta ke Ta ƙara sa faɗuwa ƙasa tana fitar da numfashi sama sama, basu ƙyale ta ba sai da su ka yi mata wankan tsarki da jinin da ke a hannunsu, wani kalar Jini mai wari da ƙarni daga gani sun tsuma shi sosai, ba ƙaramin zautar da ita su ka yi ba, Kwakwalwarta bazata Iya jure abinda suke yi mata ba, Tana jin motsin hannayensu a jikinta saƙo da lungu su ke cuccuɗata kamar suna yi mata wanka, Sun goga mata najasa a jikinta sun wulaƙanta Martabar jikinta. Allah ne bai nufa Angel zata mutu ba da tuni ta jima da mutuwa lokacinta ne bai yi ba, domin kuwa warin jinin da suka yi mata wanka dashi kaɗai ya isa ya halakar da ɗan adam. Bayan sun kammala yi mata wankan tsarkin nasu na matsafa, Giant ɗin da ya kawota Ya sanya hannu tare da tattareta kamar tsumma Ya ɗauke ta, Ya fito da ita daga Cikin Falon Ya nufi Hawa Na uku da ita, ba tare da sun mayar mata da uniform ɗin ta ba, ko yatsun hannunta bata Iya motsawa, Sautin tafiyar shi ka ɗai ta ke iya ji acikin kunnuwanta, ƙofar Wani ɗaki Ya tura da ƙafarshi Ya shigar da ita, Katafaren bedroom ne na zamani kamar ba’a cikin kurkukun Ya ke ba, Da jinin jikinta da komai Ya jefar da ita saman gadon tare da Juyawa Ya buɗe ƙofar Ya fuce.

Kaɗan daga Cikin Abunda ya faru da Angel kenan A cikin Daren ranar, Shin me kuke Tunani zai biyo Baya? Bayan gaba ɗaya Shirinsu Ya tarwatse Babu alamun zata haɗu da Danish, Ko da ta haɗu dashi daƙyar ma Ta iya gane shi saboda bata a cikin hayyacinta babbar matsalar babu ruwan zamzam ɗin da zata Iya shawo kanshi, saboda kwalbar tana a cikin aljihun uniform ɗinta, Ya salam!! Wannan wace irin mummunar ƙaddarar rayuwace!!! Me zai faru da su Azeeza? Me tsohuwa zafreen zata yi masu🥺

*Boss Bature✍️ Mu haɗu Gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*

First bank

3196407426,

*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08103884440, Banda kira whatsapp kawai*

_~*BossLadiesWriters*~_

*KURKUKUN ƘADDARA*

_The Prisoners E3🔥💫_

*Daga alƙalamin Hafsat Bature*
Chapter 7 · 0% Book details