Sashe 77
Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Sam bai ji takun tafiyarta ba, saboda hankalinshi baya atare da shi, wankan swiss lace ne a jikinta, launin ash colour riga da skirt sunbi shape din jikinta, kamar a jikinta aka ɗinka kayan, duk da bata ƙiba kayan sunyi bala’en Yi mata Kyau, Tani da Lami ne sukayi mata Make up, hatta ɗaurin ɗan kwalin kanta sune suka ɗaura mata shi, ziririyar sarƙar wuyanta ta diamond ce, stone din jikinta sai ƙyalli Yake Yi, ta yafa gyale a saman kafadarta, hannunta ruƙe da handbag, fragrance din turaren jikinta mai daɗin shaƙa ahanci.
Hankalinta ba akwance yake ba, tun kafin ta shigo ɗakin tayi mashi sallama bai amsa bata ba, har ta gaji da yin sallamar shiyasa ta yanke shawarar shigowa don ta ga ko bacci yake yi ne
Tun kafin ta ƙaraso gaban gadonshi blue eye balls dinta suka sauka akan screen din Laptop nasa
Ras taji gabanta yai mugun faɗuwa, zuciyarta tamkar zata faso ƙirjinta saboda zafin da take yi mata, zeenatu tana da saukin kai sai dai tana da zuciya idan ta hasala, ranta ya 6aci sosai ganin abunda yake kallo, hoton da ta tsana a duniyar nan duk da batasan hoton menene yake kallo ba, ranta ya bata cewar budurwarsa ce yake kallo.
Idanuwanta sun makance, bakomai suke hango mata ba face dr shureim ɗinta rungume da mace a kirjinsa.
Runtse ido tayi da karfi ta fasa wata irin gigitacciyar ƙara wadda tayi silar firgitar da shi, da sauri Ya miƙe tare da wurga idonshi Kanta, tuni ta saki jakar hannunta ƙasa, Zafafan hawayene suka wanke fuskarta.
Hankalinshi ba ƙaramin tashi yai ba, a hanzarce ya sauko daga saman gadon ya nufeta fuskarshi da alamun ruɗu ya furta”zeenatu! Lafiya? Meya faru?
Girgiza mashi kai tadinga yi tana faɗin”kada ka matso kusa dani yaya shureim, inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un” gaba ɗaya ta gama rikitar dashi”zeenatu ki natsu kiyi min bayani meya faru dake? Ko wani abu ne ya tsoratar da ke?
Cikin shessheƙar kuka tace”yaya shureim bazan Iya jurewaba, zuciyata zata Iya bugawa, tun ɗazu mukayi magana dakai akan zamu fita yawo atare, kace min inje in shirya kafin in dawo kaima za ka shiga wanka ka kimtsa, ashe baka yi komai ba, ko wankan ma bakayi ba, ka zauna kana kallon hotonta saboda tafi ni mahimmanci awurinka, ba tun yau ba kullum ne saina ganka kana kallonta, wai wacece wannan ne? Dame tafi ni? Numfashinta na fita da hucin zafi ta ƙarasa maganar, tare da juyawa da gudu ta fuce daga ɗakin nashi.
Hankalin shi ba ƙaramin tashi yai ba, idonshi akan bayanta harta 6ace ma ganin shi.
Dafe kanshi yai da hannu ɗaya, har cikin ranshi baiji daɗin kalamanta ba, baiso yai silar 6ata mata rai ba, duk da bai fahimci inda maganganunta su ka dosa ba, lumshe idanuwanshi ya ɗanyi kafin ya ware su a hankali, yayin da zuciyarshi ke tariyo mashi furucin da tayi mashi, yasan bai kyauta mata ba, ta ƙwalla fa rai akan son su fita tun Jiya shi da kanshi yai mata alƙawarin yau zai ɗauke ta a sabuwar motarshi su fita yawo.
Cikin sanyin murya ya furta”am sorry my zeenat, “ da sauri Ya nufi toilet don yai wanka.
*Boss Bature✍️ Mu haɗu Gobe In sha Allah Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*
First bank
3196407426,
*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*
_*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_
~Middle step~
سجن القدر❤🤍❤
_THE PRISONERS E23🔥💫_
*Daga alƙalamin Boss Bature*
Confusion of the heart💫
Sir mubarak ne zaune Cikin Motarshi, da su ka yi parking dinta a harabar ajiye motoci na asibitin Obinna,Tanƙameman asibiti ne Ya haɗu tamkar ba wurin Jinyar marasa lafiya ba, An zuba dukiya wurin gininsa, suna da ƙwararrun ma’aikata na gida Nigeria dana ƙasar waje.
Su biyu ne acikin motar, Shi yana a back seat na motar Ya zauna a hakimce, A yayin da Driver-operator dake driving dinsa Yana zaune saman driver’s seat kowan nan su na sanye ciki kakinsa na sojoji, sun yi shiru, Sanyin A.c din motar na ratsa fatar jikinsu, ga dukkan alamu wani muhimmin abu ne ya kawo su asibitin, akwai wanda suke Jira Ya ƙaraso, tsawon mintuna Biyar, wani kyakkyawan matashin likita Ya nufo motar da saurin shi kamar zai yi tuntu6e.
A gaban motar su ya dakata da yin tafiyar, ya kai hannu yai knocking glass din motar, turo ƙofar da a kayi ne Yasa shi yin saurin gyara natsuwar shi, Sam hankalin shi ba a kwance ya ke ba, tun da sir mubarak ya kira shi awaya ya sanar da shi game da zuwan shi asibitin gaba ɗaya ya rasa natsuwar shi, saboda sanin matsayin shi a ƙasar.
“Dr fawan, shigo ciki mana “ muryar Sir mubarak ce ta fargar da shi, Jiki na rawa ya shiga motar, ya zauna yana faman zazzare idonshi yace”daddy, ina wuni Ya gida ya Iyali” sir mubarak yace”lafiya lou fawan, Ya aiki ya fama da marasa lafiya” tun da ya fara magana bai ɗago Ya daura idonshi akan fuskar fawan ba, Hankalin shi na akan Wayar hannun shi da yake daddanawa.
Still muryarshi na rawa ya furta”Lafiya lou daddy, sai ga kiranka, Na ɗanyi mamaki” sai da ya ambaci hakan sir mubarak Ya ɗago da ido ya kalli fuskar fawan, duk da sanyin A c na motar, abun mamaki zufa ce ke tsastsafo mashi, kallon tuhuma sir mubarak yake jefa mashi, saboda zufar daya gani a saman goshin shi.
“Ya akai naga kana zubar da gumi? Ko baka da lafiya ne”? Yawu fawan Ya haɗiya tare da cewa”babu komai, Lafiya ta ƙalau”
Ta6e baki Sir mubarak Yai”Okey, Inaso ka kaini gidan kajin da kuke kiwo kai da Jazz,” da alamun ruɗu akan fuskar dr Fawan yace”Gidan kaji? Daddy ban fahimci abunda kake nufi ba, waye ya buɗe gidan kaji” yanayin yadda ya furta maganar, babu alamun yasan da zancen.
Fuskar sir mubarak a ɗaure tamau yace”You know who I am. I don’t need to explain this to you, Don haka kada ka 6oye min gaskiya, wani gidan kaji ne kuka buɗe kai da jazz? Da kanshi ya faɗa mini cewa kun zuba jari don kuyi kiwon kaji, kusan kullum ne saina kama shi yana yin waya akan gidan kiwon kajin ku”
Hankalin dr fawan ba ƙaramin tashi yai fa, Muyarshi na rawa ya furta”`wallahi thumma tallahi daddy bansan da zancen gidan kaji ba, sai dai ko ƙarya dr jazz yayi maka, ka ji na rantse maka da Allah...” Lamarin ya ɗaurewa Sir mubarak kai, Sojan dake zaune a driver seat Ya natsu Yana sauraron su, ta cikin ear-view mirror din motar Yake kallonsu.
“Fawan, Ka faɗamin gaskiya, ni nasan Jazz ba zai ta6a yi mini ƙarya ba, na lura gaba ɗaya baka acikin hayyacin ka, idan ma saboda ni ne to ka kwantar da hankalin ka, babu abun da zan yi maka, ni dai buri na shine ka kai ni gidan Kajin ku, inaso in gansu, nayi maka alƙawarin idan ka rakani na gansu zan ƙara maku jari”
cikin ruɗu dr fawan ya girgiza kai yana fadin”bazan yi maka ƙarya ba daddy, ina ganin ka tamkar uba agareni saboda ƙaunar dake a tsakanina da Jazz, wlh Daddy ni bamu ta6a yin maganar buɗe gidan kaji da dr jazz ba”
Da kakkausar murya Sojan dake a gaban motar yace”Sir, this boy isn’t telling us the truth. Why don’t we take him to the headquarter? Maybe if we do, he’ll tell us the truth.”(yalla6ai Yaron nan bazai fada mana gaskiya ba, Me zai hana Mu shiga dashi headquarter Wata’ƙil idan mu ka je can Ya faɗa mana gaskiya)
Zaro ido waje dr fawan yai, jin ance za’aje dashi headquarter, sir mubarak yace”kada ka damu ai basai munje headquarter ba, akwai bindiga a ƙuguna, “yai maganar tare da sanya hannu ya zaro bindigar Ya ɗaurata saman laps dinshi, tsabar tashin hankali ne tsantsa akan fuskar fawan.
Sir mubarak yace”idan na kashe ka na kashe banza, sai dai idan munje lahira ayi mana hisabi, don haka ka faɗa min gasiya, idan ba haka ba zan tarwatsa kanka da bindigar hannuna” bawan Allah dr fawan duk sun tsoratar dashi da barazanar su, ƴan hanjin cikin shi sun kaɗa.
Hawaye tuni sun soma wanke fuskarshi, cikin sanyin murya yace”ko da zaka kashe ni daddy, bazan fasa faɗa maka gaskiyata ba, wlh rantsuwar ɗan musulmi bani da masaniya akan maganar gidan kaji, daddy banyi niyar fada maka ba, amma don in kare kaina zan sanar dakai wani abu da baka sani ba” Hankalinsu gaba ɗaya yana akan fuskarshi.
Numfasawa yayi kafin ya ɗaura da cewa “Daddy, jazz baya zuwa aiki, yau kusan wata ɗaya da sati, bansani ba ko kunsan da hakan, Ni kaina na damu da canzawarshi,”. Zuciyar Sir mubarak a hautsine Ya furta”idan kuwa har hakane Dr fawan baka kyauta mini ba! Meyasa tuntuni baka kira awaya ka sanar dani cewa baya zuwa aiki ba? Kusan kullum sai na ganshi ya shirya zai je asibiti, hakan na nufin ba aiki yake zuwaba wani wurin daban ya ke tafiya? Ya jefa mashi tambayar yana mai jin ɗaci acikin zuciyarshi.
“Ka yi hakuri daddy, Bana son in shiga tsakaninka da shi, sannan ni bansan baku da masaniya akan hakan ba”
“Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un!” Sir mubarak ne ya furta hakan, zuciyarshi tayi matuƙar karaya da jin cewa jazz baya zuwa aiki, Ya fara zargin shi akan ƙarairakin da ya ke yi mashi, bai ta6a tunanin Jazz zai yi mashi haka ba, duk da irin ƙaunar da yake nuna mashi.
Idanuwan shi tuni sun kaɗa jawur, zuciyarshi ta motsa.
“Bana so Jazz ya san cewa nazo asibitin nan! Ko nayi magana dakai! Kaja baki kayi shiru,” dr fawan ya amsa mashi da toh daddy, in sha Allah bazan faɗa mashi ba.
“Ka share hawayen ka,” da sauri dr fawan ya zaro hanky ya soma goge fuskarshi.
Hankalinta ba akwance yake ba, tun kafin ta shigo ɗakin tayi mashi sallama bai amsa bata ba, har ta gaji da yin sallamar shiyasa ta yanke shawarar shigowa don ta ga ko bacci yake yi ne
Tun kafin ta ƙaraso gaban gadonshi blue eye balls dinta suka sauka akan screen din Laptop nasa
Ras taji gabanta yai mugun faɗuwa, zuciyarta tamkar zata faso ƙirjinta saboda zafin da take yi mata, zeenatu tana da saukin kai sai dai tana da zuciya idan ta hasala, ranta ya 6aci sosai ganin abunda yake kallo, hoton da ta tsana a duniyar nan duk da batasan hoton menene yake kallo ba, ranta ya bata cewar budurwarsa ce yake kallo.
Idanuwanta sun makance, bakomai suke hango mata ba face dr shureim ɗinta rungume da mace a kirjinsa.
Runtse ido tayi da karfi ta fasa wata irin gigitacciyar ƙara wadda tayi silar firgitar da shi, da sauri Ya miƙe tare da wurga idonshi Kanta, tuni ta saki jakar hannunta ƙasa, Zafafan hawayene suka wanke fuskarta.
Hankalinshi ba ƙaramin tashi yai ba, a hanzarce ya sauko daga saman gadon ya nufeta fuskarshi da alamun ruɗu ya furta”zeenatu! Lafiya? Meya faru?
Girgiza mashi kai tadinga yi tana faɗin”kada ka matso kusa dani yaya shureim, inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un” gaba ɗaya ta gama rikitar dashi”zeenatu ki natsu kiyi min bayani meya faru dake? Ko wani abu ne ya tsoratar da ke?
Cikin shessheƙar kuka tace”yaya shureim bazan Iya jurewaba, zuciyata zata Iya bugawa, tun ɗazu mukayi magana dakai akan zamu fita yawo atare, kace min inje in shirya kafin in dawo kaima za ka shiga wanka ka kimtsa, ashe baka yi komai ba, ko wankan ma bakayi ba, ka zauna kana kallon hotonta saboda tafi ni mahimmanci awurinka, ba tun yau ba kullum ne saina ganka kana kallonta, wai wacece wannan ne? Dame tafi ni? Numfashinta na fita da hucin zafi ta ƙarasa maganar, tare da juyawa da gudu ta fuce daga ɗakin nashi.
Hankalin shi ba ƙaramin tashi yai ba, idonshi akan bayanta harta 6ace ma ganin shi.
Dafe kanshi yai da hannu ɗaya, har cikin ranshi baiji daɗin kalamanta ba, baiso yai silar 6ata mata rai ba, duk da bai fahimci inda maganganunta su ka dosa ba, lumshe idanuwanshi ya ɗanyi kafin ya ware su a hankali, yayin da zuciyarshi ke tariyo mashi furucin da tayi mashi, yasan bai kyauta mata ba, ta ƙwalla fa rai akan son su fita tun Jiya shi da kanshi yai mata alƙawarin yau zai ɗauke ta a sabuwar motarshi su fita yawo.
Cikin sanyin murya ya furta”am sorry my zeenat, “ da sauri Ya nufi toilet don yai wanka.
*Boss Bature✍️ Mu haɗu Gobe In sha Allah Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*
First bank
3196407426,
*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*
_*💋KURKUKUN ƘADDARA💋*_
~Middle step~
سجن القدر❤🤍❤
_THE PRISONERS E23🔥💫_
*Daga alƙalamin Boss Bature*
Confusion of the heart💫
Sir mubarak ne zaune Cikin Motarshi, da su ka yi parking dinta a harabar ajiye motoci na asibitin Obinna,Tanƙameman asibiti ne Ya haɗu tamkar ba wurin Jinyar marasa lafiya ba, An zuba dukiya wurin gininsa, suna da ƙwararrun ma’aikata na gida Nigeria dana ƙasar waje.
Su biyu ne acikin motar, Shi yana a back seat na motar Ya zauna a hakimce, A yayin da Driver-operator dake driving dinsa Yana zaune saman driver’s seat kowan nan su na sanye ciki kakinsa na sojoji, sun yi shiru, Sanyin A.c din motar na ratsa fatar jikinsu, ga dukkan alamu wani muhimmin abu ne ya kawo su asibitin, akwai wanda suke Jira Ya ƙaraso, tsawon mintuna Biyar, wani kyakkyawan matashin likita Ya nufo motar da saurin shi kamar zai yi tuntu6e.
A gaban motar su ya dakata da yin tafiyar, ya kai hannu yai knocking glass din motar, turo ƙofar da a kayi ne Yasa shi yin saurin gyara natsuwar shi, Sam hankalin shi ba a kwance ya ke ba, tun da sir mubarak ya kira shi awaya ya sanar da shi game da zuwan shi asibitin gaba ɗaya ya rasa natsuwar shi, saboda sanin matsayin shi a ƙasar.
“Dr fawan, shigo ciki mana “ muryar Sir mubarak ce ta fargar da shi, Jiki na rawa ya shiga motar, ya zauna yana faman zazzare idonshi yace”daddy, ina wuni Ya gida ya Iyali” sir mubarak yace”lafiya lou fawan, Ya aiki ya fama da marasa lafiya” tun da ya fara magana bai ɗago Ya daura idonshi akan fuskar fawan ba, Hankalin shi na akan Wayar hannun shi da yake daddanawa.
Still muryarshi na rawa ya furta”Lafiya lou daddy, sai ga kiranka, Na ɗanyi mamaki” sai da ya ambaci hakan sir mubarak Ya ɗago da ido ya kalli fuskar fawan, duk da sanyin A c na motar, abun mamaki zufa ce ke tsastsafo mashi, kallon tuhuma sir mubarak yake jefa mashi, saboda zufar daya gani a saman goshin shi.
“Ya akai naga kana zubar da gumi? Ko baka da lafiya ne”? Yawu fawan Ya haɗiya tare da cewa”babu komai, Lafiya ta ƙalau”
Ta6e baki Sir mubarak Yai”Okey, Inaso ka kaini gidan kajin da kuke kiwo kai da Jazz,” da alamun ruɗu akan fuskar dr Fawan yace”Gidan kaji? Daddy ban fahimci abunda kake nufi ba, waye ya buɗe gidan kaji” yanayin yadda ya furta maganar, babu alamun yasan da zancen.
Fuskar sir mubarak a ɗaure tamau yace”You know who I am. I don’t need to explain this to you, Don haka kada ka 6oye min gaskiya, wani gidan kaji ne kuka buɗe kai da jazz? Da kanshi ya faɗa mini cewa kun zuba jari don kuyi kiwon kaji, kusan kullum ne saina kama shi yana yin waya akan gidan kiwon kajin ku”
Hankalin dr fawan ba ƙaramin tashi yai fa, Muyarshi na rawa ya furta”`wallahi thumma tallahi daddy bansan da zancen gidan kaji ba, sai dai ko ƙarya dr jazz yayi maka, ka ji na rantse maka da Allah...” Lamarin ya ɗaurewa Sir mubarak kai, Sojan dake zaune a driver seat Ya natsu Yana sauraron su, ta cikin ear-view mirror din motar Yake kallonsu.
“Fawan, Ka faɗamin gaskiya, ni nasan Jazz ba zai ta6a yi mini ƙarya ba, na lura gaba ɗaya baka acikin hayyacin ka, idan ma saboda ni ne to ka kwantar da hankalin ka, babu abun da zan yi maka, ni dai buri na shine ka kai ni gidan Kajin ku, inaso in gansu, nayi maka alƙawarin idan ka rakani na gansu zan ƙara maku jari”
cikin ruɗu dr fawan ya girgiza kai yana fadin”bazan yi maka ƙarya ba daddy, ina ganin ka tamkar uba agareni saboda ƙaunar dake a tsakanina da Jazz, wlh Daddy ni bamu ta6a yin maganar buɗe gidan kaji da dr jazz ba”
Da kakkausar murya Sojan dake a gaban motar yace”Sir, this boy isn’t telling us the truth. Why don’t we take him to the headquarter? Maybe if we do, he’ll tell us the truth.”(yalla6ai Yaron nan bazai fada mana gaskiya ba, Me zai hana Mu shiga dashi headquarter Wata’ƙil idan mu ka je can Ya faɗa mana gaskiya)
Zaro ido waje dr fawan yai, jin ance za’aje dashi headquarter, sir mubarak yace”kada ka damu ai basai munje headquarter ba, akwai bindiga a ƙuguna, “yai maganar tare da sanya hannu ya zaro bindigar Ya ɗaurata saman laps dinshi, tsabar tashin hankali ne tsantsa akan fuskar fawan.
Sir mubarak yace”idan na kashe ka na kashe banza, sai dai idan munje lahira ayi mana hisabi, don haka ka faɗa min gasiya, idan ba haka ba zan tarwatsa kanka da bindigar hannuna” bawan Allah dr fawan duk sun tsoratar dashi da barazanar su, ƴan hanjin cikin shi sun kaɗa.
Hawaye tuni sun soma wanke fuskarshi, cikin sanyin murya yace”ko da zaka kashe ni daddy, bazan fasa faɗa maka gaskiyata ba, wlh rantsuwar ɗan musulmi bani da masaniya akan maganar gidan kaji, daddy banyi niyar fada maka ba, amma don in kare kaina zan sanar dakai wani abu da baka sani ba” Hankalinsu gaba ɗaya yana akan fuskarshi.
Numfasawa yayi kafin ya ɗaura da cewa “Daddy, jazz baya zuwa aiki, yau kusan wata ɗaya da sati, bansani ba ko kunsan da hakan, Ni kaina na damu da canzawarshi,”. Zuciyar Sir mubarak a hautsine Ya furta”idan kuwa har hakane Dr fawan baka kyauta mini ba! Meyasa tuntuni baka kira awaya ka sanar dani cewa baya zuwa aiki ba? Kusan kullum sai na ganshi ya shirya zai je asibiti, hakan na nufin ba aiki yake zuwaba wani wurin daban ya ke tafiya? Ya jefa mashi tambayar yana mai jin ɗaci acikin zuciyarshi.
“Ka yi hakuri daddy, Bana son in shiga tsakaninka da shi, sannan ni bansan baku da masaniya akan hakan ba”
“Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un!” Sir mubarak ne ya furta hakan, zuciyarshi tayi matuƙar karaya da jin cewa jazz baya zuwa aiki, Ya fara zargin shi akan ƙarairakin da ya ke yi mashi, bai ta6a tunanin Jazz zai yi mashi haka ba, duk da irin ƙaunar da yake nuna mashi.
Idanuwan shi tuni sun kaɗa jawur, zuciyarshi ta motsa.
“Bana so Jazz ya san cewa nazo asibitin nan! Ko nayi magana dakai! Kaja baki kayi shiru,” dr fawan ya amsa mashi da toh daddy, in sha Allah bazan faɗa mashi ba.
“Ka share hawayen ka,” da sauri dr fawan ya zaro hanky ya soma goge fuskarshi.