← Book details Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 24 OF 152

Sashe 24

Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Hankulansu gaba ɗaya ya koma kan su, kowan nan su fuskarshi akumbure take suntum, babu walwala ko annuri, dagaske Azeezana bata mutu ba? Gabriel ne yai tambayar yayin da idonshi ke fitar da hawaye, Danish ne ya bashi amsar tambayarshi, Tsabar farin Cikine ya bayyana akan fuskarshi, Rumfa yai ma azeeza da ƙirjinshi motsa la66anta da take yi ne ya tabbatar mashi da cewa tana araye sungumarta yai tare da ɗaurata saman laps ɗinshi, Danish Ya miƙa mashi gorar ruwa don ya bata tasha, Yatsun hannun shi na kerma ya kar6a ya kafa mata abaki, ruwan yana wucewa ta maƙoshinta sai dai ta gaza buɗe idonta, Farin Ciki duk ya cikasu, Naufal ne ya ɗauki Parveen Baiwar Allah anji jiki, miƙa mashi gorar ruwan Gabriel yai ya kar6a yabawa parveen kamar zata haɗa da gorar duka ta shanye, Sai lokacin Danish Ya raba jikin shi daga na Batul Ya rarrafa zuwa gaban Haris dake kwance kamar matacce ya ɗaura hannayenshi biyu wurin ɗago dashi ya kwantar da kansa saman kafaɗarshi, Cikin sanyin murya ya ke ambaton sunanshi”Haris! Haris!” shiru bai amsa mashi ba, jikin shi yai zafi sosai babu alamun lafiya atattare dashi, ɗaura tafin hannun shi yai saman ƙirjinshi bugun zuciyar haris a hargitse yake fita, hakan ba ƙaramin tada mashi hankali yai ba, Yana fargabar wani abu ya same shi.
“Ɗan uwana Rabin raina nasan kana jin muryata pls kada ka bari damuwa tayi maka illa, ina atare da kai” jin muryar Danish acikin kunnanshi yasa shi ƙoƙarin motsa la66ansa sam sautin yaƙi fita, Fahimtar hakan yasa danish matsar da kunnanshi saitin bakin Haris

“Deeja ta mutu! Na rasa Deeja Danish! Bazan iya rayuwa ba tare da ita ba, zuciyata nauyi take yi min, ka taimaka ma rayuwata” a hargitse yake magana, tsananin tausayin shi ne ya kama Danish, dama sai da ranshi ya bashi cewar akan Deeja ne ya shiga mawuyacin halin nan.

“Haris ka kwantar da hankalin ka, ba mu da tabbacin suna araye ko sun mutu, tun da har su Azeeza suka farka bayan munyi tunanin sun mutu ina saran suma za’a iya samun masu rai acikin su” cikin jin ƙunar rai Haris ya furta”Danish idan har hakane deejana tana araye azzuluman mutanancan zasu Iya kashe min ita, mun barsu fa a kurkuku, Danish ka koma ka ɗauko min ita, idan baso kake na mutu ba’ sosai ya sanya mashi kuka, Rarrashin shi ya dinga yi yana lalla6a shi duk don ya samu ciwon nashi ya lafa.

Waɗanda suka fi jin jiki a cikinsu Jemimah ce da Azeeza sai Haris, Ita parveen tunda taji ta ajikin Naufal ta wartsake, har tana iya ambaton yunwa take ji, Jemimah kuwa taƙi daina yi masu kuka, Sautin kukanta ya karaɗe kogon dutsen kamar ana zare ranta, Hankalin Angel duk yabi ya tashi, Ta rasa ya zatayi da ita, Cikin muryar kuka take yiwa Danish magana akan yazo yataimaka mata, Har ƙwara Azeeza tun da ta ƙanƙame Gabriel bata ƙara motsawa ba, ta lafe mashi idanuwanta arufe suke gam.

Sun rasa ya za su yi dasu, kukan jamima ba ƙaramin tsuma zuciyarsu yake yi ba, taji jiki baiwar Allah, Sunga ƙoƙarinta da har ta iya yin kukan, azabar raɗaɗin gabanta ne ya addabeta, ta rasa ina zata tsoma ranta taji daɗi, fuskarta jaga jaga da hawaye, yarinyar da bata wuci shekara goma da watanni ba, ta rasa budurcinta, su kansu sunyi mamakin da ta iya rayuwa, lokacin mutuwarta ne baiyi ba, Tana kuka suna kuka, Babu wanda bai zubar mata da ƙwalla ba in ka cire Danish, kwantar da Haris yai saman shimfiɗar, jikinshi na tsuma ya nufi Angel Ya sanya hannu biyu ya kar6i jemimah daga hannunta, fucewa yai da ita daga Cikin kogon dutsen basu san Inda ya nufa da ita ba.

Tsawon mintuna sai gashi ya dawo rungume da ita a ƙirjinshi, ajiyar zuciya suka sauke Jin tayi shiru tadaina kukan, Akwatin kayansu ya buɗe ya ɗauko mata rigar sanyi, cikin waɗanɗa tsohuwa ta yi masu kyautarsu, Ya sanya mata a jikinta, ga dukkan alamu wanka ya yi mata, bayan ya kammala sanya mata rigar, ya curo mata hula ya zura mata akanta, ya kuma ɗauko Mayafin kayansu, Sai kallon shi suke yi, Danish ya basu mamaki, Asaman bayanta ya yafa mata mayafin ya miƙe tsaye yana lallashinta kamar yadda akeyi wa jarirai, jemimah ta natsu sai faman lumshe idanuwanta takeyi, Jikinta ya lafa sosai ta daina jin raɗaɗi ciwo nata, juyowa yai tare da nufar Angel ya miƙa mata jemimah,

“Zan tafi da Azeeza ki basu naman su fara ci” amsa mashi tayi da toh, ta kar6i jemimah tare da rungume ta a ƙirjinta, bayan Ya ɗauki Azeeza Ya fuce da ita, janyo masu naman tayi zuwa gabansu, duk da halin da suke aciki hakan bai hanasu Cin naman ba, Saboda matsiyaciyar yunwar da suke ji, Mutun ɗayane ya kasa cin naman, ko da Javed Ya tallabo shi ya zaunar dashi Yana tura mashi abaki, Amayar dashi ya dinga Yi, ruwa kaɗai ya iya sha, sun damu da rashin lafiyar Haris Ya galabaita sosai, Jemimah dai ta ɗanci naman Angel ce take bata abaki, har yanzu bata buɗe idanuwanta ba, balle ta san a ina suke.

Shigowa cikin Kogon Danish yai Hannunshi ɗauke da Azeeza, Ya wanke ta tass jikinta sai kakarwa yakeyi, tunkafin ya ƙaraso Gabriel Ya buɗe akwatin kayansu ya ɗauko mata rigar sanyi tare da mayafi, Bayan Danish Ya miƙa mashi ita, Ya sanya mata rigar asaman uniform ɗinta, Ya ɗaura mata mayafi saman kanta, kafin ya kwantar da ita saman ƙirjin shi, Abaki ya dinga gutsuro namanta yana tura mata abaki daƙyar take iya taune shi, Hakan ba ƙaramin daɗi yayi masu ba, duk fa wannan budurin da sukeyi Azeeza da Jamimah da Parveen basu san cewa sun bar kurkukun ƙaddara ba, Saboda basa acikin hayyacin su.

Danish bai samu damar cin nashi naman ba, Jira yai sai da suka kammala ɗaya bayan ɗaya ya raka su zuwa bakin ruwan nan suna yin wanka, da taimakon shi Haris ya samu yayi wanka jikin shi ya ɗanyi mashi daɗi, bayan sun kammala Ya ƙara haɗo wasu itacen Ya kunna masu wuta Kogon dutsen ya ɗumama sosai Sanyin da su ke ji ya washe, sun cinye namansu duka, Kaɗan Danish ya samu yaci, kamar masu zaman makoki haka su ka zauna kewaye da wutar da ke ci, Suna kallon junan su kowa da abunda ya ke saƙawa aran shi, jemimah tuni bacci ya ɗauketa kamar jinjira haka Angel ta matseta a ƙirjinta, haka azeezama bacci ne ya ɗauke ta, tana kwance saman jikin gabriel, Haris ya langwa6a kanshi saman kafaɗar Danish, Batul ta ɗaura kanta saman kafadar Angel, Parveen tana a kwance saman ƙirjin naufal, da hannu biyu ya tallabeta, haka zalika Hannah tana arungume jikin Javed, sun natsu suna sauraron kukan namun dawan dake hargowa acikin Dajin, ba zaka ta6a fahimtar yanayin da su ke a ciki ba, kowa da abunda yake saƙawa aranshi.

*OBIE STATE*

In Abuja🏙

*Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*

First bank

3196407426,

*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*

_~*BossLadiesWriters*~_

_*KURKUKUN ƘADDARA*_

_The Prisoners E8🔥💫_

*Daga alƙalamin Boss Bature*

~Middle step~

_A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._

*Obie Estate*Haɗaɗɗiyar Daular arziƙi, Aljannar duniya da babu tamkarta a faɗin nahiyar Africa, Hamshaƙin Estate Ne Da ya haɗa tanƙama tanƙaman luxury Villas, da duk wani Ababen more rayuwa, Kayan alatun da ke a cikinsa kaɗai abun kallo ne, dollar ta yi kuka awurin ƙera ginin, yana da 6angarori da dama, kama daga katafaren Gate ɗin shiga Estate ɗin wanda Jami’ae ne ke tsaron shi Sojoji da ƴan sanda Ko sauro bai isa Ya ƙetara ƙofar shiga gidan ba saboda tsaron da ke gare shi, ba iya mutane ba hada na’urorin da ke sanya ido ga duk wani mai shige da fuce, kowace kusurwa ta villas ɗin tana maƙale da na’urorin cctv camera, daga bakin faffaɗan gate ɗin Santalelen titi ne zai isar da kai ga Interior ɗin daular, akwai Harabar ajiye motocinsu, Gardens da swimming pools area, Ga zoo wurin da ake kiwata dabbobin gidan. Kowani Villa na estate ɗin Yana da nashi kayan alatun na more rayuwa, parts ɗin da ke a cikin kowani gida ya haɗa da Haɗaɗɗun falullukansu waɗanda suka ji jigunannun furniture, Bedrooms, Dining rooms, Kitchens, Bathrooms, Laundry rooms, da sauransu, akwai Ƙayatattun dogayen benaye zubin twin stairs da U-shaped stairs, Idan ma mutun baida ra’ayin Hawa Benan Kowane Villa yana ɗauke da residential elevator wadda aka fi sani da lifter, tun daga Hawa na farko zata ɗauki mutun har izuwa hawa na Uku, dai dai da cokalin amfani na gidan babu wanda aka ƙera a ƙasa Nigeria, kaf kayansu daga ƙasar waje ake shigo dasu, mai karfin imani ne Kaɗai zai iya rayuwa acikin estate dinsu ba tare daya shagala daga yin ibadarshi ba, sai dai ta inda masu rayuwa cikin gidajen zasu burge ka Allah ya hore masu baiwar Ilmin duka na addini dana zamani, wayayyun mutanene masu daraja da ƙima a idon duniya, Sun Iya takun su ba zaka ta6a Iya aibatasu ba, saboda kyawawan ɗabi’unsu da halayansu, komai nasu is Extraordinary.

Tun da garin Allah ya waye masu aikin gidan su ke ta kai komo, kowaccensu ta yi dressing cikin chef’s uniform launin farare, ƙwararru ne a 6angaren girke girke da gyaran gida, basu wasa da aikin su, Suna ba lokacin mahimmancin sa, kuma suna takatsantsan wurin kula da buƙatun mutanan gidan.
Chapter 24 · 0% Book details