Sashe 71
Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Sai dai har yanzu bamu rasa power ɗinmu ba, Garkuwa namu ne har abada, mu ke ruƙe da masarrafin da zamu Iya sarrafa linzamin shi, mu kaɗai ne mu ke da iko da shi, ba zamu ta6a yin danasanin Ɗaura shi amatsayin magajin kurkukun ƙaddara ba, kuskure ɗaya da muka tabka shine sakacin da mu ka yi da har ya samu nasarar guduwa daga kurkuku, Ni ban damu da sauran Yaran da suka ku6uta ba, saboda basu da amfani a wurinmu, mun ci moriyar su, mutun ukun ne sune rauninmu, Na farko Garkuwarmu dole sai da shi za’a Iya Cin galaba akanmu, Na biyu ƙaddarar kurkuku, yarinyar ta fi sauran hatsari tun da har ta Iya Jan hankalin garkuwarmu, wanda nayi imanin da ace babu ƙauna a tsakanin shi da yarinyar ba zai ta6a taimakon sauran ƴan uwan shi don su gudu daga tarkon mu,” Ya faɗa yana mai jan dogon numfashi Ya fetsar da shi, ya cigaba da faɗin “Itace silar komai, kuma itace kaɗai zata Iya sarrafa shi bayan mu, idan kuwa hakan Ya faru zai Iya fallasa mana sirrin mu ya kuma taimaka wurin ruguza kurkukun ƙaddara”! Da ƙarfi Ya ambaci hakan Yana mai nuna fusatar shi.
“Yarinya ta ƙarshe itace bugun zuciyar kurkukun ƙaddara, kamar yadda ya zo mana a allon tsafin mu, idan har muka samu nasarar Cire Zuciyarta daga ƙirjinta zamu samu ƙarfin Iko fiye da wanda muke da shi a yanzu, Ita kuma ƙaddarar kurkuku dole mu dawo da ita cikin mu idan har muna son ta zamar mana ƙaddara mai kyau, barin ta awaje shi zaisa ta zamto mummunar ƙaddara agare mu” Tamkar mayunwacin zaki haka yake kora masu jawabi yana fitar da huci.
Bayan ya rufe baki Na gefen shi ya soma magana da wata irin murya ta dattawa waɗanda suka Shahara a fagen zalunci.
“Tun fil azal, Banso Muka damƙa amanar mu ga tsohuwa tamira ba, dama tun lokacin Sai da na musa akan hakan, Ni dama nasani Jinin Habibullah ba zasu ta6a zama amintattun mu ba, sai gashi sun yaudaremu sunci amanar kurkuku, sun kashe mana Zafreen ɗaya daga cikin shuwagabannin mu, babu wanda ya ta6a tsammanin zasu Ci amanar mu ita da ɗanta Salsabeel, sai da suka bari mun basu yarda mu su kuma suka butulce mana, haƙiƙa Nayi takaicin rasa gangar jikin tamira, da ba abun da zai hana mu azabtar da ita, mu sa6ule naman jikinta sannan muyi farfesun shi muba ma Karnuka su shanye roman, amma duk da haka bamu makaro ba, Zamu huce haushin mu akan ɗanta Salsabeel” mutumin da yayi maganar babu ɗigon imani akansa.
Bayan ya dasa aya a maganar shi, wani daga cikin shuwagabannin Ya numfasa tare da cewa”Garkuwa ya yi mana mummunar 6arnar da ba zamu Iya gyarata ba, bamu ta6a tsammanin zai Iya yi mana haka ba, sai dai ba zamu Iya hukunta shi ba, saboda shi jinin mu ne, abu ɗaya da zamu Iya yi mashi shine mu hana shi jin daɗin rayuwarshi da Yarinyar, mu shiga tsakaninsu, horon da zamu bashi kenan, sannan zamu ci gaba da sarrafa shi wurin azabtar da mutane, kafin muyi nasarar dawo da su Cikin mu, hikmar yin hakan mutane zasu fara tsoranshi suna nuna mashi ƙyamata, zai ji duk duniya kamar ba’a sonshi ne, kunga anan zai yi tunanin mu kaɗaine gatanshi, kurkukune kaɗai inda zai zauna yayi rayuwarshi ba tare da ƙuntata ba, daga lokacin daya fara wannan tunanin mu kuma zamu samu damar kwashesu su ukun mu dawo da su cikin mu”! Ya kai ƙarshen maganar tare da buga hannun arm chair ɗin da yake a zaune, gaba ɗaya matsafan suka fashe da dariya mai sautin gaske tamkar ana bubbuga ganga, jikinsu har jijjiga ya ke yi saboda tsabar yadda suke yin dariyar kamar dokuna.
“Mun Fi ƙarfin mutun, Ko mutuwa tsoron tunkararmu take Yi, shiyasa muka daɗe muna sheƙe ayarmu, shan jinin mutune da cin tsokar naman su yanzu muka fara, Rainon Yara ba zamu fasa ba, zamu cigaba da tarasu a cikin kurkukun ƙaddara muna biyan buƙatarmu dasu domin samun ƙarfin ikonmu” Ihu suka dinga Yi sunayin shewa sautin muryoyinsu tamkar zasu fasa bangon Fadar, kusan atare matsafan suke miƙe tsaye suna taka rawarsu ta matsafa, kowan nan su, ya ɗauki abunda yake ra’ayin ci asaman table wasu giya, wasu farfesun naman mutun wasu jini wasu kuma naman dabbobi suke ci, Yayin da wasun su a tsaye suke saduwa da junansu kamar dabbobi wa’iya zubillah.
*DAULAR OBIE ESTATE*
*Dr. jazz❤*
Ƙudundune yake acikin bargo, saman katafaren gadonshi na gidan Sir mubarak, cikin muryar raɗa yake yin magana a wayar shi.
“I’m not working today, I’m at home. yanzu haka da ni ke yi maka magana Ina akwance saman gadona” shiru ya ɗanyi yana sauraron mutumin da suke yin wayarshi, can yaci gaba da cewa”Boss Man kasan bana wasa da aikin ka, idan ka bani umarni jiki na rawa nike yin shi, ko jiya na shiga gidan gonar na duba lafiyar kajin, sai dai muce Alhamdulillah, Jikin su yayi kyau baka ga yadda suke tafiya ba tsokar jikinsu har girgiza take yi saboda ƙoshin lafiyar dake gare su” ya ƙare maganar muryarshi da sautin dariya
“My Boss Man, Amma dani da kai zamu ɗubi na azumi ko? Ko zamu bari sai sallah Ayi layya da su”? Tuntsirewa yayi da dariya jin amsar da mutumin ya bashi muryarshi cikin harshen turanci yake yi mashi magana.
“Amma ai kasan nayi ƙoƙari, tun da na fara kiwon kajin nan wlh ko ɗaya ban ta6a gigin kamawa don in yanka ba, kuma miyau na ya biya fa” da shagwa6a ya ƙare maganar.
Abun da bai sani ba, tun da ya fara yin wayar, Sir mubarak Ya shigo ɗakin jikinshi sanye da kakin sojoji, Hannunsa biyu ruƙe da faffaɗan plate, daga saman shi an jera Chocolate raspberry cupcakes.
Ya shigo ɗakin ne da niyar ya faranta mashi, tun lokacin da turai ta faɗa mashi game da gorin da Hajiya saratu ke yi mashi akan cewa shi ba mahaifin shi bane sai yaji ya ƙara ƙaunar yaron yana matuƙar sonshi.
Lamarin Ya ɗaure mashi kai, ba tun yau ba, Ya jima yana mamakin wayar da dr jazz ke yi akan Kajin gidan gona, cikin tafiyar sanɗa Sir mubarak Ya ƙarasa shiga ɗakin ya zauna gefen gadon shi hannun shi ruƙe da plate din, Ya kasa kunne Yana sauraron tattaunawar jazz da Boss man din shi.
Jin shiru Jazz bai ƙara yin magana ba yai tunanin ko ya kammala yin wayar ne, Gyaran murya ya yi mashi.
Jazz da ke ƙudundune cikin bargo yai lamo jikinshi ya kama yin kerma jin muryar Sir mubarak Hankalin shi ba ƙaramin tashi yai ba.
“Jazz nasan idonka Biyu Ka tashi inason magana dakai” A hankali Ya zame bargon, Ƴar singlet ce ajikinshi tare da Gajeran wando, sumar kanshi duk ta hargitse.
Yana faman mutsustsuke ido da hannu ya saci kallon Sir mubarak
Muryarshi da kasala Ya furta
“Daddy ina kwana, ka tashi lafiya, ya mommy’ adabarbarce ya ambaci hakan sam bai lura da plate din hannunsa ba.
Babu alamun zai amsa mashi gaisuwar tashi, wani irin kallon tuhuma Yake jefa mashi, Ƴan kame kame jazz ya kama Yi, don Ya fahimci dadyn nasa yaji komai da ya ke faɗi a wayarshi.
“Jazz, da wa ka ke yin magana a waya? muryar shi a kausashe Ya jefa mashi tambayar.
Cikin rawar murya Jazz yace”daddy abokina ne dr fawan ai na faɗa maka tare da shi muka buɗe gidan kaji muna yin kiwon su’ yaƙi yarda su haɗa ido da uncle mubarak.
Gyaɗa kai yai”Jazz zan ƙara jan kunnanka akan Ka kiyaye mutanan da za ka yi mu’amala dasu! Bana son kayi abunda zaka Yi danasani, Ni bana zargin ka da wani abu, Ina yi maka kyakkyawan zato My son, Nasihar da zanyi maka shine Kaji tsoron Allah komi za ka yi a duniyar nan kada ka manta Allah Yana ganin ka, kuma zaka koma gare shi ne, jin daɗin duniyar nan ƙalilan nan komai da muka samu anan zamu barshi, a kowani yanayi na rayuwa mutawa zata Iya riskar mutun, me yakamata muyi? Mu kasance muna aikata aikin Alkhairi akoda yaushe, sannan duk runtsi duk wuya kada ka ta6a karya zuciyar wanda ya aminta dakai.....” cikin kwantar da murya Sir mubarak Yake yi mashi nasiha, jikinshi duk yai sanyi, idanuwanshi sun cicciko tab da ƙwalla Ya ɗago Yana kallon fuskar Sir mubarak, Har Ila yau yana mamakin Halin Sir mubarak da Obinna suna da mutunci da daraja ɗan adam, duk da kasancewar shi ɗan mai aikin gidansu sun maida shi tamkar jinin su, tun kafin Ya mallaki hankalinshi suke yin ɗawainiya dashi, cin shi shan shi suturarshi da karatun shi sune suka ɗauki nauyin komai na rayuwarshi.
Yayi zurfi acikin tunanin shi muryar sir mubarak ta katse shi”Ina magana ka tsareni da ido” da sauri Ya sunnar da kanshi ƙasa, Ƙwallar da suka taru cikin idonshi tuni sun soma gangarowa saman kuncinsa.
“Jazz Why are you crying”? Ya faɗa yana duban face dinsa.
cikin shessheƙar kuka ya soma magana”nagode sosai daddyna, ina matuƙar alfahari dakai, saboda ƙaunar da kuke nuna mun kai da baba, ban ta6a danasanin kasancewata acikin family dinku ba, Ina jin daɗin nasihar da ka ke yi min daddy, ka maidani tamkar ɗanka komai na rayuwa kana Yi min...” murmushin gefe fuska sir mubarak yaɗan saki.
“My son ya isa Haka, share hawayenka, Ni dai fatana Ka ruƙe mutuncinka Jazz, Kada ka bani Kunya, inaso ka zama abunda duniya zata yi alfahari dakai”
Jinjina kai yai tare da ɗago da kai Ya ɗaura rinannun idanuwanshi akan fuskar Sir Mubarak “In sha Allah, Nayi maka alƙawarin hakan, Zan kama mutuncina kuma bazan ta6a baka kunya ba”
Miƙa mashi plate din hannun shi yayi
“Your mother made this for you. I know how much you love cupcakes.” fuskarshi ɗauke da ƙayataccen murmushi Yake dubanshi, Hannun Dr Jazz Har kerma Yake yi wurin kar6ar Plate din
“Kayi brush kuwa? Naga kamar yanzu ka farka daga bacci,”
“Yarinya ta ƙarshe itace bugun zuciyar kurkukun ƙaddara, kamar yadda ya zo mana a allon tsafin mu, idan har muka samu nasarar Cire Zuciyarta daga ƙirjinta zamu samu ƙarfin Iko fiye da wanda muke da shi a yanzu, Ita kuma ƙaddarar kurkuku dole mu dawo da ita cikin mu idan har muna son ta zamar mana ƙaddara mai kyau, barin ta awaje shi zaisa ta zamto mummunar ƙaddara agare mu” Tamkar mayunwacin zaki haka yake kora masu jawabi yana fitar da huci.
Bayan ya rufe baki Na gefen shi ya soma magana da wata irin murya ta dattawa waɗanda suka Shahara a fagen zalunci.
“Tun fil azal, Banso Muka damƙa amanar mu ga tsohuwa tamira ba, dama tun lokacin Sai da na musa akan hakan, Ni dama nasani Jinin Habibullah ba zasu ta6a zama amintattun mu ba, sai gashi sun yaudaremu sunci amanar kurkuku, sun kashe mana Zafreen ɗaya daga cikin shuwagabannin mu, babu wanda ya ta6a tsammanin zasu Ci amanar mu ita da ɗanta Salsabeel, sai da suka bari mun basu yarda mu su kuma suka butulce mana, haƙiƙa Nayi takaicin rasa gangar jikin tamira, da ba abun da zai hana mu azabtar da ita, mu sa6ule naman jikinta sannan muyi farfesun shi muba ma Karnuka su shanye roman, amma duk da haka bamu makaro ba, Zamu huce haushin mu akan ɗanta Salsabeel” mutumin da yayi maganar babu ɗigon imani akansa.
Bayan ya dasa aya a maganar shi, wani daga cikin shuwagabannin Ya numfasa tare da cewa”Garkuwa ya yi mana mummunar 6arnar da ba zamu Iya gyarata ba, bamu ta6a tsammanin zai Iya yi mana haka ba, sai dai ba zamu Iya hukunta shi ba, saboda shi jinin mu ne, abu ɗaya da zamu Iya yi mashi shine mu hana shi jin daɗin rayuwarshi da Yarinyar, mu shiga tsakaninsu, horon da zamu bashi kenan, sannan zamu ci gaba da sarrafa shi wurin azabtar da mutane, kafin muyi nasarar dawo da su Cikin mu, hikmar yin hakan mutane zasu fara tsoranshi suna nuna mashi ƙyamata, zai ji duk duniya kamar ba’a sonshi ne, kunga anan zai yi tunanin mu kaɗaine gatanshi, kurkukune kaɗai inda zai zauna yayi rayuwarshi ba tare da ƙuntata ba, daga lokacin daya fara wannan tunanin mu kuma zamu samu damar kwashesu su ukun mu dawo da su cikin mu”! Ya kai ƙarshen maganar tare da buga hannun arm chair ɗin da yake a zaune, gaba ɗaya matsafan suka fashe da dariya mai sautin gaske tamkar ana bubbuga ganga, jikinsu har jijjiga ya ke yi saboda tsabar yadda suke yin dariyar kamar dokuna.
“Mun Fi ƙarfin mutun, Ko mutuwa tsoron tunkararmu take Yi, shiyasa muka daɗe muna sheƙe ayarmu, shan jinin mutune da cin tsokar naman su yanzu muka fara, Rainon Yara ba zamu fasa ba, zamu cigaba da tarasu a cikin kurkukun ƙaddara muna biyan buƙatarmu dasu domin samun ƙarfin ikonmu” Ihu suka dinga Yi sunayin shewa sautin muryoyinsu tamkar zasu fasa bangon Fadar, kusan atare matsafan suke miƙe tsaye suna taka rawarsu ta matsafa, kowan nan su, ya ɗauki abunda yake ra’ayin ci asaman table wasu giya, wasu farfesun naman mutun wasu jini wasu kuma naman dabbobi suke ci, Yayin da wasun su a tsaye suke saduwa da junansu kamar dabbobi wa’iya zubillah.
*DAULAR OBIE ESTATE*
*Dr. jazz❤*
Ƙudundune yake acikin bargo, saman katafaren gadonshi na gidan Sir mubarak, cikin muryar raɗa yake yin magana a wayar shi.
“I’m not working today, I’m at home. yanzu haka da ni ke yi maka magana Ina akwance saman gadona” shiru ya ɗanyi yana sauraron mutumin da suke yin wayarshi, can yaci gaba da cewa”Boss Man kasan bana wasa da aikin ka, idan ka bani umarni jiki na rawa nike yin shi, ko jiya na shiga gidan gonar na duba lafiyar kajin, sai dai muce Alhamdulillah, Jikin su yayi kyau baka ga yadda suke tafiya ba tsokar jikinsu har girgiza take yi saboda ƙoshin lafiyar dake gare su” ya ƙare maganar muryarshi da sautin dariya
“My Boss Man, Amma dani da kai zamu ɗubi na azumi ko? Ko zamu bari sai sallah Ayi layya da su”? Tuntsirewa yayi da dariya jin amsar da mutumin ya bashi muryarshi cikin harshen turanci yake yi mashi magana.
“Amma ai kasan nayi ƙoƙari, tun da na fara kiwon kajin nan wlh ko ɗaya ban ta6a gigin kamawa don in yanka ba, kuma miyau na ya biya fa” da shagwa6a ya ƙare maganar.
Abun da bai sani ba, tun da ya fara yin wayar, Sir mubarak Ya shigo ɗakin jikinshi sanye da kakin sojoji, Hannunsa biyu ruƙe da faffaɗan plate, daga saman shi an jera Chocolate raspberry cupcakes.
Ya shigo ɗakin ne da niyar ya faranta mashi, tun lokacin da turai ta faɗa mashi game da gorin da Hajiya saratu ke yi mashi akan cewa shi ba mahaifin shi bane sai yaji ya ƙara ƙaunar yaron yana matuƙar sonshi.
Lamarin Ya ɗaure mashi kai, ba tun yau ba, Ya jima yana mamakin wayar da dr jazz ke yi akan Kajin gidan gona, cikin tafiyar sanɗa Sir mubarak Ya ƙarasa shiga ɗakin ya zauna gefen gadon shi hannun shi ruƙe da plate din, Ya kasa kunne Yana sauraron tattaunawar jazz da Boss man din shi.
Jin shiru Jazz bai ƙara yin magana ba yai tunanin ko ya kammala yin wayar ne, Gyaran murya ya yi mashi.
Jazz da ke ƙudundune cikin bargo yai lamo jikinshi ya kama yin kerma jin muryar Sir mubarak Hankalin shi ba ƙaramin tashi yai ba.
“Jazz nasan idonka Biyu Ka tashi inason magana dakai” A hankali Ya zame bargon, Ƴar singlet ce ajikinshi tare da Gajeran wando, sumar kanshi duk ta hargitse.
Yana faman mutsustsuke ido da hannu ya saci kallon Sir mubarak
Muryarshi da kasala Ya furta
“Daddy ina kwana, ka tashi lafiya, ya mommy’ adabarbarce ya ambaci hakan sam bai lura da plate din hannunsa ba.
Babu alamun zai amsa mashi gaisuwar tashi, wani irin kallon tuhuma Yake jefa mashi, Ƴan kame kame jazz ya kama Yi, don Ya fahimci dadyn nasa yaji komai da ya ke faɗi a wayarshi.
“Jazz, da wa ka ke yin magana a waya? muryar shi a kausashe Ya jefa mashi tambayar.
Cikin rawar murya Jazz yace”daddy abokina ne dr fawan ai na faɗa maka tare da shi muka buɗe gidan kaji muna yin kiwon su’ yaƙi yarda su haɗa ido da uncle mubarak.
Gyaɗa kai yai”Jazz zan ƙara jan kunnanka akan Ka kiyaye mutanan da za ka yi mu’amala dasu! Bana son kayi abunda zaka Yi danasani, Ni bana zargin ka da wani abu, Ina yi maka kyakkyawan zato My son, Nasihar da zanyi maka shine Kaji tsoron Allah komi za ka yi a duniyar nan kada ka manta Allah Yana ganin ka, kuma zaka koma gare shi ne, jin daɗin duniyar nan ƙalilan nan komai da muka samu anan zamu barshi, a kowani yanayi na rayuwa mutawa zata Iya riskar mutun, me yakamata muyi? Mu kasance muna aikata aikin Alkhairi akoda yaushe, sannan duk runtsi duk wuya kada ka ta6a karya zuciyar wanda ya aminta dakai.....” cikin kwantar da murya Sir mubarak Yake yi mashi nasiha, jikinshi duk yai sanyi, idanuwanshi sun cicciko tab da ƙwalla Ya ɗago Yana kallon fuskar Sir mubarak, Har Ila yau yana mamakin Halin Sir mubarak da Obinna suna da mutunci da daraja ɗan adam, duk da kasancewar shi ɗan mai aikin gidansu sun maida shi tamkar jinin su, tun kafin Ya mallaki hankalinshi suke yin ɗawainiya dashi, cin shi shan shi suturarshi da karatun shi sune suka ɗauki nauyin komai na rayuwarshi.
Yayi zurfi acikin tunanin shi muryar sir mubarak ta katse shi”Ina magana ka tsareni da ido” da sauri Ya sunnar da kanshi ƙasa, Ƙwallar da suka taru cikin idonshi tuni sun soma gangarowa saman kuncinsa.
“Jazz Why are you crying”? Ya faɗa yana duban face dinsa.
cikin shessheƙar kuka ya soma magana”nagode sosai daddyna, ina matuƙar alfahari dakai, saboda ƙaunar da kuke nuna mun kai da baba, ban ta6a danasanin kasancewata acikin family dinku ba, Ina jin daɗin nasihar da ka ke yi min daddy, ka maidani tamkar ɗanka komai na rayuwa kana Yi min...” murmushin gefe fuska sir mubarak yaɗan saki.
“My son ya isa Haka, share hawayenka, Ni dai fatana Ka ruƙe mutuncinka Jazz, Kada ka bani Kunya, inaso ka zama abunda duniya zata yi alfahari dakai”
Jinjina kai yai tare da ɗago da kai Ya ɗaura rinannun idanuwanshi akan fuskar Sir Mubarak “In sha Allah, Nayi maka alƙawarin hakan, Zan kama mutuncina kuma bazan ta6a baka kunya ba”
Miƙa mashi plate din hannun shi yayi
“Your mother made this for you. I know how much you love cupcakes.” fuskarshi ɗauke da ƙayataccen murmushi Yake dubanshi, Hannun Dr Jazz Har kerma Yake yi wurin kar6ar Plate din
“Kayi brush kuwa? Naga kamar yanzu ka farka daga bacci,”