Sashe 23
Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Mun ƙaraso,” Jin abunda yace ne yasa ta ɗago da kanta, tana ƙarewa wurin kallo, nan ta ke ta ji tana sha’awar shan ruwan, Zuƙunnawa yai ta sauko daga saman bayan nashi, a jere suka tsaya suna bin ruwan da kallo, ga dukkan alamu ya burgesu .
“Danish ƙishi na ke ji, nasan kaima kana ji, mu sha sai mu ɗebi wani mu kai ma su Parveen ko”? Ba tare da ya juyo ya kalli fuskarta ba ya soma magana”Wanka nake so nayi maki, saboda kinyi muni, jikin ki yayi datti”
Har saida gabanta ya faɗi jin abunda yace, juyowa yai da fuskarshi ya kalleta tare da kashe mata ido ɗaya
“za ki iya cire kayan ko in taimaka maki ne”? gabanta ne ya dinga faɗuwa sai ta ga kamar ya canza mata, babu alamun wasa akan fuskar shi yai maganar.
Ganin yana matsowa kusa da ita, yasa ta juya da niyar ta gudu, ko ta ku ɗaya bata kai ga yi ba taji Ya damƙi ƙugunta, ƙarfi ba ɗaya ba, Duk yadda taso ta kubce mashi ta kasa, matseta yai a ƙirjin shi, A hankali Yai amfani da hannun shi ɗaya wurin zame rigar Jikin shi, tare da wandon kakinsa na Giant, ya rage daga shi sai short fari, saman gungurumeman dutsen dake agefen ruwan, ya jefar da uniform ɗinshi.
kamar jinjira haka ya ɗauke ta, kaitsaye Ya nufi Cikin ruwan da ke gangarowa, ba yadda ta iya dashi, Tana kuka tana fadin bataso ya ƙyale ya rabu da ita, ahaka yayi mata wanka tass ya wanketa Kamar yayi amfani da sabulu ita kanta tayi mamikin yadda Jinin jikinta ke fita, Farar fatarta sol ta dawo har wani salƙi takeyi da ɗaukar ido, hatta uniform ɗin da ke ajikinta sun wanku sosai sun manne ma fatarta,
kwantar da kanta yai saman broad chest ɗinshi, Ya cusa yatsun hannunshi cikin sumar kanta yana cuccuɗata da ruwa, Jinin da ya danƙare mata a cikin kan ya dinga fita, gashin kanta ya dawo ainihin launin shi dark brown mai kyan gaske, ba ƙaramin taimakonta yai ba da yayi mata wanka, Ita kanta tasan bazata iya wanke najasar dake a jikinta ba, ƙanƙame jikinshi tayi sosai la66anta na kerma take faɗin”sanyi Danish san yi ni ke ji, tamkar ana ƙara gudun ruwan sun jiƙe sharkaf acikinsa, sai da ya kammala tsaftace mata jikinta tukunna ya ɗaukota saman kafaɗarshi ya dawo da ita Gefen dutsen da ya ɗaura uniform ɗinshi.
Tun da ya sauke ta ta faɗa ma faffaɗan ƙirjinshi, ta zagayo da hannayenta saman bayanshi, sai faman sauke ajiyar zuciya take yi, idanuwanta a lumshe, ita kaɗai tasan daɗin da ta ke ji, da farko taji haushi da ya yi mata wanka, amma yanzu ta fahimci Dalilin dayasa ya tursasa mata yin wanka, jikinta yayi mata daɗi wata irin ni’ima ke sauka, tamkar an yaye mata damuwar dake acikin zuciyarta, sun natsu suna sauraron bugun zuciyar junansu, irin yanayin da yafi son kasancewa tare da ita, yana son Angel dinsa fiye da yadda yake son kanshi, a shirye yake daya sadaukar da ranshi indai akanta ne”
Fatar wuyanta ya ƙurawa ido fara sol sai ƴan tabannin da ba arasa ba, na gurjewar da tayi, ɗaura tafin hannayensa yai asaman bayan nata,
“My Angel!” a kasalance ya furta sunanta shiru bata amsa mashi ba
“Are you feeling sleepy?” kamar yayi magana da bango shiru taƙi buɗe ba ki ta yi magana, ƙoƙarin rabata yayi daga ƙirjinsa, sai dai taƙi bari ya ɗago da ita, ta yi tighting ɗin shi tamkar zata koma cikin shi, baiwar Allah, Dama abuƙace take da ta samu inda zata sassauta raɗaɗin da ke acikin zuciyarta, abubuwan da suka faruwa a rayuwarta ta soma tariyowa tun daga lokacin da ta mallaki hankalin ta, har zuwa rayuwarta a hannun fulanin Daji da kuma faɗowarta gidan kurkukun ƙaddara, Zafafan hawayene suka wanke fuskarta, jin shessheƙar kukanta ne yasa shi rikicewa ya shiga ambaton sunanta adabarbarce, daƙyar ya iya 6an6arota daga ƙirjinshi, eyes dinshi akan fuskarta ta runtse idonta
“My Angel I don’t want you to dwell on what happened before, I know it hurts you, but please forget about the past. I don’t like to see you cry.
tun da ya soma lallashinta bata buɗe idanuwanta ba, tsawon mintuna kafin a hankali ta ɗago da kanta tare da jingina bayanta jikin dutse.
Matsawa yayi jikin ƙaton dutsen ya miƙa hannu ya ruƙo uniform ɗin shi, A tsanake Ya sanyasu a jikin shi
“Zaki Iya jirana anan”? girgiza mashi kai tayi”tsoro nake ji, ka maida ni cikin ƴan uwana” yaso ta amince ko dan ya samu ya shiga cikin Dajin Ya nemo masu abunda zasu ci, kwantar mata da hankalinta yai”Yanzu zan dawo, bana so ƴan uwanmu su tashi da yunwa pls ki jirani anan, ba abunda zai same ki, kada kije ko’ina” bai jira amsarta ba, ya 6ace ma ganinta.
Tunawa da cewa ita fa yanzu mai ƴanci ce yasa ta ɗan saki murmushi, har ta fara tunanin irin mugun kisan da za ta yi ma waɗanda su ka sadaukar da su, badajimawa ba ta soma Jin motsin tafiyar mutun a firgice ta buɗe idanuwanta lokaci ɗaya ta sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya ganin Danish ne ya dawo hannun shi a ruƙe da Zomayen Daji da ya yo masu farautarsu, ya ruƙe ƙafafuwansu da hannu ɗaya, yayin da ɗayan hannun ke aruƙe da gorar ruwan, mamaki ne ya kamata ganin zomaye, miƙa mata gorar ruwan yai da sauri tasa hannu ta kar6a, Acike take da ruwa, jera kafaɗa su ka yi suna tafiya suna satar kallon juna, abunda ya ɗaure mata kai yadda Danish yasan komai dangane da Daji mutumin da bai ta6a fita daga cikin kurkuku ba, Yanzu tadaina yi mashi kallon solo6iyo, A Namijinsa ta ke kallon shi.
Lokacin da su ka ƙaraso Gaban Kogon dutsen, Atare su ka shiga Ciki, Ya ajiye zomayen saman korayen ciyayin da ke shimfiɗe ƙasa, ya ɗago da ido ya kalle ta, zanje na haɗo itace yanzu zan dawo, Ta amsa mashi da toh,’
Bayan tafiyarshi ta ajiye gorar ruwan ƙasa, kafin ta nufi shimfiɗar su, ba ta yi mamakin ganin ba su farka ba saboda ta riga ta gane aikin Danishi, gaban akwatin kayansu ta zuƙunna ta buɗe ta curo tsoffin uniform ɗinta, Cikin ƙanƙanin lokaci ta canza na jikinta da suka jiƙe ta shanya su daga wajen dutsen, dawowa tayi cikin kogon Agaban shimfiɗar ta zuƙunna tana ƙare masu kallo, idanuwanta akan Jemimah da Azeeza, daɗi kamar zai kasheta, a ƙagare ta ke da su farka su ga wurin da Allah ya kawosu tasan zasu sha mamaki da al’ajabi kuma zasu ji daɗin cika masu alƙawarin da ta yi.
Sam ba ta ji motsin shigowarshi ba, har sai da yai mata gyaran murya tukunna ta waiwayo su ka haɗa ido da shi
In zo in tayaka”? girgiza mata kai yai” a’a bana so ki wahala” miƙewa tayi tare da zuwa gabanshi ta zuƙunna tana ƙare mashi kallo, hankalin shi ya koma akan itacen da ya ke jerawa bayan ya kammala ya ɗauki duwatsun jiya da yai amfani wurin rura wuta, duk wani motsin shi akan idonta har ce mata yai “kije ki huta mana, ba kince kina jin sanyi ba? Ki ɗauko bargo” maƙe mashi kafaɗa tai alamar ba za ta je ba.
Bawan Allah shiya zauna zaman gasa masu naman, sai maiƙo yake yi kamar an soya shi da mai, Kitsan jikin zomayen ne ke narkewa, bayan ya kammala ya ɗaura gasasshen naman da ya tsira Jikin icce saman faffaɗan ganyan da ya shimfiɗa a ƙasa.
“Danish” ɗagowa yai tare da kallonta, bakomai ya gani acikin idanuwanta ba face Tsantsar tausayin shi
“Kada ki damu kanki am ok, idan zan shekara inayi maku bauta ba zan gaji ba” kalamanshi sun ƙara sanya mata ƙaunarshi acikin zuciyarta.
“A ina ka samu wannan gorar ruwa”? Tai maganar tana nuna ta da yatsa
“A cikin Daji ba abunda ba zaki Iya samu ba, Hada kan mutun” murmushin gefen fuska ta saki, ga dukkan alamu zasu fara kafa nasu tarihin soyayyar tun acikin Daji.
Ɗagowa yai da lumsassun idanuwanshi ya ɗaura su kan fuskarta
“Can you eat by yourself? Or do I need to feed you?”
Girgiza mashi kai tai” ka wahala sosai, ni ya kamata in baka da hannuna” ya ji daɗin maganarta har ya buɗe baki da niyar mayar mata da martanin maganarta, kwatsam! muryar Jemimah ta katsesu da wani irin sautin mai amo take kwaɗawa Angel kira amatuƙar gigice take fadin”Genie wayyo Allah Genie Zafi Jikina ƙaiƙayi nake ji” Ahanzarce Danish da Angel suka miƙe da sauri suka nufi shimfiɗarsu atare suka zuƙunna agabansu, Hannu biyu Angel ta sanya ta ɗauko ta zuwa saman jikinta, ta ƙanƙameta, Duk tabi ta furgice sai kuka takeyi masu tana harba ƙafafuwanta, Sautin kukanta ne ya farfaɗo da sauran ƴan uwan nasu, Batul ce ta fara miƙewa kamar fatalwa idanuwanta luhu luhu sun kaɗa jawur, baiwar Allah har faɗawa tayi sai uban haske, gashin kanta kuwa a hargitse yake, Buɗe idonta keda wuya ta sauke su akan na Danish dake kallonta, Muryarshi na ɗan rawa ya furta sunanta”Ba..tul” ɗauke idonta tayi daga kan fuskarshi ta mayar dasu Kan kogon dutsen da suke aciki saƙo da lungu tabi da kallo, kukan farin cikine ya kubce mata, Da sauri Danish ya ruƙo hannunta acikin nashi ya kwanto da kanta saman ƙirjinshi, sosai ta ƙanƙameshi tana cigaba da yin kukan.
Farkawa Gabriel yai zumbur ya miƙe yana ambaton sunan Azeeza, da ita ya kwanta acikin ranshi, sai tsuma yake yi yana fitar da huci, Cikin shessheƙar Kuka Angel tace dashi”She’s still alive! Azeezar mu bata mutu ba, suna araye,”
Karaf maganarta ta sauka akan kunnan sauran ƴan uwan su da suka farka, a zazzaune suka miƙe Tun daga kan Javed, Naufal da Hannah mutun uku ne basu motsa ba, parveen Azeeza da Haris, ga dukkan alamu sun farka daga bacci sai dai sun kasa motsawa, Jikinsu ba ƙoshin lafiya, ko yatsan su sun gaza ɗagawa.
“Danish ƙishi na ke ji, nasan kaima kana ji, mu sha sai mu ɗebi wani mu kai ma su Parveen ko”? Ba tare da ya juyo ya kalli fuskarta ba ya soma magana”Wanka nake so nayi maki, saboda kinyi muni, jikin ki yayi datti”
Har saida gabanta ya faɗi jin abunda yace, juyowa yai da fuskarshi ya kalleta tare da kashe mata ido ɗaya
“za ki iya cire kayan ko in taimaka maki ne”? gabanta ne ya dinga faɗuwa sai ta ga kamar ya canza mata, babu alamun wasa akan fuskar shi yai maganar.
Ganin yana matsowa kusa da ita, yasa ta juya da niyar ta gudu, ko ta ku ɗaya bata kai ga yi ba taji Ya damƙi ƙugunta, ƙarfi ba ɗaya ba, Duk yadda taso ta kubce mashi ta kasa, matseta yai a ƙirjin shi, A hankali Yai amfani da hannun shi ɗaya wurin zame rigar Jikin shi, tare da wandon kakinsa na Giant, ya rage daga shi sai short fari, saman gungurumeman dutsen dake agefen ruwan, ya jefar da uniform ɗinshi.
kamar jinjira haka ya ɗauke ta, kaitsaye Ya nufi Cikin ruwan da ke gangarowa, ba yadda ta iya dashi, Tana kuka tana fadin bataso ya ƙyale ya rabu da ita, ahaka yayi mata wanka tass ya wanketa Kamar yayi amfani da sabulu ita kanta tayi mamikin yadda Jinin jikinta ke fita, Farar fatarta sol ta dawo har wani salƙi takeyi da ɗaukar ido, hatta uniform ɗin da ke ajikinta sun wanku sosai sun manne ma fatarta,
kwantar da kanta yai saman broad chest ɗinshi, Ya cusa yatsun hannunshi cikin sumar kanta yana cuccuɗata da ruwa, Jinin da ya danƙare mata a cikin kan ya dinga fita, gashin kanta ya dawo ainihin launin shi dark brown mai kyan gaske, ba ƙaramin taimakonta yai ba da yayi mata wanka, Ita kanta tasan bazata iya wanke najasar dake a jikinta ba, ƙanƙame jikinshi tayi sosai la66anta na kerma take faɗin”sanyi Danish san yi ni ke ji, tamkar ana ƙara gudun ruwan sun jiƙe sharkaf acikinsa, sai da ya kammala tsaftace mata jikinta tukunna ya ɗaukota saman kafaɗarshi ya dawo da ita Gefen dutsen da ya ɗaura uniform ɗinshi.
Tun da ya sauke ta ta faɗa ma faffaɗan ƙirjinshi, ta zagayo da hannayenta saman bayanshi, sai faman sauke ajiyar zuciya take yi, idanuwanta a lumshe, ita kaɗai tasan daɗin da ta ke ji, da farko taji haushi da ya yi mata wanka, amma yanzu ta fahimci Dalilin dayasa ya tursasa mata yin wanka, jikinta yayi mata daɗi wata irin ni’ima ke sauka, tamkar an yaye mata damuwar dake acikin zuciyarta, sun natsu suna sauraron bugun zuciyar junansu, irin yanayin da yafi son kasancewa tare da ita, yana son Angel dinsa fiye da yadda yake son kanshi, a shirye yake daya sadaukar da ranshi indai akanta ne”
Fatar wuyanta ya ƙurawa ido fara sol sai ƴan tabannin da ba arasa ba, na gurjewar da tayi, ɗaura tafin hannayensa yai asaman bayan nata,
“My Angel!” a kasalance ya furta sunanta shiru bata amsa mashi ba
“Are you feeling sleepy?” kamar yayi magana da bango shiru taƙi buɗe ba ki ta yi magana, ƙoƙarin rabata yayi daga ƙirjinsa, sai dai taƙi bari ya ɗago da ita, ta yi tighting ɗin shi tamkar zata koma cikin shi, baiwar Allah, Dama abuƙace take da ta samu inda zata sassauta raɗaɗin da ke acikin zuciyarta, abubuwan da suka faruwa a rayuwarta ta soma tariyowa tun daga lokacin da ta mallaki hankalin ta, har zuwa rayuwarta a hannun fulanin Daji da kuma faɗowarta gidan kurkukun ƙaddara, Zafafan hawayene suka wanke fuskarta, jin shessheƙar kukanta ne yasa shi rikicewa ya shiga ambaton sunanta adabarbarce, daƙyar ya iya 6an6arota daga ƙirjinshi, eyes dinshi akan fuskarta ta runtse idonta
“My Angel I don’t want you to dwell on what happened before, I know it hurts you, but please forget about the past. I don’t like to see you cry.
tun da ya soma lallashinta bata buɗe idanuwanta ba, tsawon mintuna kafin a hankali ta ɗago da kanta tare da jingina bayanta jikin dutse.
Matsawa yayi jikin ƙaton dutsen ya miƙa hannu ya ruƙo uniform ɗin shi, A tsanake Ya sanyasu a jikin shi
“Zaki Iya jirana anan”? girgiza mashi kai tayi”tsoro nake ji, ka maida ni cikin ƴan uwana” yaso ta amince ko dan ya samu ya shiga cikin Dajin Ya nemo masu abunda zasu ci, kwantar mata da hankalinta yai”Yanzu zan dawo, bana so ƴan uwanmu su tashi da yunwa pls ki jirani anan, ba abunda zai same ki, kada kije ko’ina” bai jira amsarta ba, ya 6ace ma ganinta.
Tunawa da cewa ita fa yanzu mai ƴanci ce yasa ta ɗan saki murmushi, har ta fara tunanin irin mugun kisan da za ta yi ma waɗanda su ka sadaukar da su, badajimawa ba ta soma Jin motsin tafiyar mutun a firgice ta buɗe idanuwanta lokaci ɗaya ta sauke nauyayyiyar ajiyar zuciya ganin Danish ne ya dawo hannun shi a ruƙe da Zomayen Daji da ya yo masu farautarsu, ya ruƙe ƙafafuwansu da hannu ɗaya, yayin da ɗayan hannun ke aruƙe da gorar ruwan, mamaki ne ya kamata ganin zomaye, miƙa mata gorar ruwan yai da sauri tasa hannu ta kar6a, Acike take da ruwa, jera kafaɗa su ka yi suna tafiya suna satar kallon juna, abunda ya ɗaure mata kai yadda Danish yasan komai dangane da Daji mutumin da bai ta6a fita daga cikin kurkuku ba, Yanzu tadaina yi mashi kallon solo6iyo, A Namijinsa ta ke kallon shi.
Lokacin da su ka ƙaraso Gaban Kogon dutsen, Atare su ka shiga Ciki, Ya ajiye zomayen saman korayen ciyayin da ke shimfiɗe ƙasa, ya ɗago da ido ya kalle ta, zanje na haɗo itace yanzu zan dawo, Ta amsa mashi da toh,’
Bayan tafiyarshi ta ajiye gorar ruwan ƙasa, kafin ta nufi shimfiɗar su, ba ta yi mamakin ganin ba su farka ba saboda ta riga ta gane aikin Danishi, gaban akwatin kayansu ta zuƙunna ta buɗe ta curo tsoffin uniform ɗinta, Cikin ƙanƙanin lokaci ta canza na jikinta da suka jiƙe ta shanya su daga wajen dutsen, dawowa tayi cikin kogon Agaban shimfiɗar ta zuƙunna tana ƙare masu kallo, idanuwanta akan Jemimah da Azeeza, daɗi kamar zai kasheta, a ƙagare ta ke da su farka su ga wurin da Allah ya kawosu tasan zasu sha mamaki da al’ajabi kuma zasu ji daɗin cika masu alƙawarin da ta yi.
Sam ba ta ji motsin shigowarshi ba, har sai da yai mata gyaran murya tukunna ta waiwayo su ka haɗa ido da shi
In zo in tayaka”? girgiza mata kai yai” a’a bana so ki wahala” miƙewa tayi tare da zuwa gabanshi ta zuƙunna tana ƙare mashi kallo, hankalin shi ya koma akan itacen da ya ke jerawa bayan ya kammala ya ɗauki duwatsun jiya da yai amfani wurin rura wuta, duk wani motsin shi akan idonta har ce mata yai “kije ki huta mana, ba kince kina jin sanyi ba? Ki ɗauko bargo” maƙe mashi kafaɗa tai alamar ba za ta je ba.
Bawan Allah shiya zauna zaman gasa masu naman, sai maiƙo yake yi kamar an soya shi da mai, Kitsan jikin zomayen ne ke narkewa, bayan ya kammala ya ɗaura gasasshen naman da ya tsira Jikin icce saman faffaɗan ganyan da ya shimfiɗa a ƙasa.
“Danish” ɗagowa yai tare da kallonta, bakomai ya gani acikin idanuwanta ba face Tsantsar tausayin shi
“Kada ki damu kanki am ok, idan zan shekara inayi maku bauta ba zan gaji ba” kalamanshi sun ƙara sanya mata ƙaunarshi acikin zuciyarta.
“A ina ka samu wannan gorar ruwa”? Tai maganar tana nuna ta da yatsa
“A cikin Daji ba abunda ba zaki Iya samu ba, Hada kan mutun” murmushin gefen fuska ta saki, ga dukkan alamu zasu fara kafa nasu tarihin soyayyar tun acikin Daji.
Ɗagowa yai da lumsassun idanuwanshi ya ɗaura su kan fuskarta
“Can you eat by yourself? Or do I need to feed you?”
Girgiza mashi kai tai” ka wahala sosai, ni ya kamata in baka da hannuna” ya ji daɗin maganarta har ya buɗe baki da niyar mayar mata da martanin maganarta, kwatsam! muryar Jemimah ta katsesu da wani irin sautin mai amo take kwaɗawa Angel kira amatuƙar gigice take fadin”Genie wayyo Allah Genie Zafi Jikina ƙaiƙayi nake ji” Ahanzarce Danish da Angel suka miƙe da sauri suka nufi shimfiɗarsu atare suka zuƙunna agabansu, Hannu biyu Angel ta sanya ta ɗauko ta zuwa saman jikinta, ta ƙanƙameta, Duk tabi ta furgice sai kuka takeyi masu tana harba ƙafafuwanta, Sautin kukanta ne ya farfaɗo da sauran ƴan uwan nasu, Batul ce ta fara miƙewa kamar fatalwa idanuwanta luhu luhu sun kaɗa jawur, baiwar Allah har faɗawa tayi sai uban haske, gashin kanta kuwa a hargitse yake, Buɗe idonta keda wuya ta sauke su akan na Danish dake kallonta, Muryarshi na ɗan rawa ya furta sunanta”Ba..tul” ɗauke idonta tayi daga kan fuskarshi ta mayar dasu Kan kogon dutsen da suke aciki saƙo da lungu tabi da kallo, kukan farin cikine ya kubce mata, Da sauri Danish ya ruƙo hannunta acikin nashi ya kwanto da kanta saman ƙirjinshi, sosai ta ƙanƙameshi tana cigaba da yin kukan.
Farkawa Gabriel yai zumbur ya miƙe yana ambaton sunan Azeeza, da ita ya kwanta acikin ranshi, sai tsuma yake yi yana fitar da huci, Cikin shessheƙar Kuka Angel tace dashi”She’s still alive! Azeezar mu bata mutu ba, suna araye,”
Karaf maganarta ta sauka akan kunnan sauran ƴan uwan su da suka farka, a zazzaune suka miƙe Tun daga kan Javed, Naufal da Hannah mutun uku ne basu motsa ba, parveen Azeeza da Haris, ga dukkan alamu sun farka daga bacci sai dai sun kasa motsawa, Jikinsu ba ƙoshin lafiya, ko yatsan su sun gaza ɗagawa.