Sashe 150
Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
“Ni abun da yafi burge ni, haɗuwar ƴa’ƴan baba obie da jikokinsa, da surukansa sun ɗauki wanka na mutunci na kece raini kai komai ma sun haɗa, waɗanda suka fi burgeni kinga prime minister Hateem, da president dinmu Sharafudeen sun iya dattako, komai nasu da aji suke yin shi, matayensu sunfi kowa haduwa gimbiya mujeedat da Hajiya malikat sarauta, sai kuma mutuniyata Hajiya saratu inayin matarnan saboda tana ƙaunata mutane suna fadin masifarta ni wallahi bata ta6a yi min koda tsawa ba kamar ƴar cikinta haka take yi min magana....” da farin ciki akan fuskarta tayi maganar.
Aneelerh tace”Jinin ku Ya haɗune dana juna, Allah yasa ta zama surukarki kinga shikenan kema zaki samu matsugunni a obie estate” wani irin ihun farin ciki zahra tasaki hada jujjuya qugu tana fadin”Amen Ya Allah, Aunty Aneelerh Allah ya kar6i addu’arki”
Dariya Aneelerh tasaki yayin da take ɗauraye plates din da take wanke wa da ruwan dake fita a faucet.
“Zahra baki faɗamin haduwarki da mutumin ba”?
Kwa6e fuska zahra tayi annurin fuskarta ya ragu.
“Bai zo taron ba, duk irin burin dana ci nason ganinshi bai halarta ba, banji dadi ba dama nasan zai yi wuya yaje saboda mutunne shi da baisan hayaniya”
“Eyyah zahra najiye maki baƙin ciki, in sha Allah wata rana zaku haɗu da shi”
Ta6e baki tayi”Ni yanzu ba wannan ba auntyna, Inataso in baki labarin Nazli da Yazrin Ƴa’ƴan Prime minister da ƙanwar Chief Owais hindu, kinga waɗannan dana lissafa maki ƙarshene su afagen kyau da aji, cikin maza kuwa in ka cire chief owais sai wani ɗan uwansu menene ma sunanshi.....” ta faɗa tana cizon yatsa takasa tuna sunan.
“Namanta, shima a canada yake zaune, mutumin ya iya ɗaukar wanka, ga kyau da aji bayan shi sai twins sun haɗuwa sunyi kyau kamar dollars.
Dariya Aneelerh tayi, jin yadda zahra ta haƙiƙance tana bata labari ko gajiya batayi.
“Yanzu faɗa min alherin da sukayi maki naji ɗazu kince zaki fada min”
Gyara tsayuwa zahra tayi kafin tace
“Kinga da farko Hajiya saratu tayi min kyautar tsadadden leshi guda biyu, da hand bag, hada set na agogo da zobe, da turarurruka......” jinjina kai Aneelerh ta yi tana fadin”masha Allah, zahra najiye maki daɗi, kin samu na sallah”
“Bangama fada maki ba, bayan kuɗin aikin decoration da hajiya saratu ta biyamu, prime minsiter yayi mana kyautar kuɗi duk mutun ɗaya 1.5 million” waro ido waje Aneelerh tayi mahboob dake la6e jin an ambaci kuɗi sai gashi ya dawo gefen zahra Yana raira waƙa.
“In rabo ya tsago dakai kuma abun ya tabbatar saida kai to rabbine yace sai da kai in sai da kai kawai sai da kai, don haka nima Allah ne ya tsaga da rabona ashe arziƙine ke kirana......” gaba ɗaya suka sanya dariya, Aneelerh tace”mahboob yaushe ka shigo kitchen din nan”
Da murmushi akan fuskarshi yace”tun ɗazu ina la6e bakin ƙofa na kasa kunne ina sauraron aku sarkin ɗumi, yau surutun zahra yayi min rana wannan arziƙi haka, wato saboda baƙin ciki zahra ƙiri ƙiri kika hana in rakaki obie estate da yanzu hadani za’ayi rabon kuɗin nan....”
Dariya zara tayi tana fadin”ai baka ji komai ba, bayan kuɗin da prime minister yabamu, president Ya ƙara mana, duk mutun ɗaya dubu ɗari takwas” dafe ƙirji mahboob yayi kamar wanda yaji wani mugun abun
“Sannan Abokin Baba Obie, Jan kunne ya raba mana dubu ɗari biyar biyar da dollar ya bamu su”
Kallon juna mahboob da Aneelerh su kayi.
“Anya zahra dagaske kike kuwa? Wannan kuɗi haka kamar akan bishiya ake tsunkosu”
Hararar shi zahra tayi”an gaya maka kowa mai maƙone irinka, ai su a wurinsu kuɗin da suka bamu bakomai bane”
Jinjina kai mahboob yayi”Allahumma arzuƙni, Sister Yanzu ina kuɗin suke? inaso zan tayaki ƙirgawa”
Dariyar shaƙiyanci zahra tayi kafin tace”suna kwance cikin account bank dina suna bacci, dollar din da aka ba mu ne kaɗai suke a dakina kuma na 6oye su saboda nasan halinka sarai, tsaf zaka Iya zuwa ɗaki yi min halin 6era”
Dariya Aneelerh tasaki, a lokacin ta kammala yin wanke wanken, ta mayar da hankali akan fuskar zahra
Mahboob Yace”kar dai kice zakiyi min rashin mutunci wallahi sai inyi zuciya inje in nemi auran ɗaya daga cikin jikokin baba obie”
Dariya suka saki gaba dayansu bayan sun tsagaita Aneelerh ta dubi mahboob”Ya ake ciki? Kunyi magana da Ana”?
Ɗaga mata kai yai alamar eh, zahra tace me ya faru ne ko bata da lafiya”
Nan mahboob Ya kwashe komai Ya sanar dasu dangane da halin da Ana take aciki.
Shiru sukayi jikin kowa yayi sanyi, musamman Aneelerh, ranta Ya dan 6aci bata ji dadin ƙin gaya matan da tayi ba.
“Idan kuwa hakana Ana bata kyauta min ba,Yanzu har akwai abunda zata 6oye min duk irin shaƙuwar dake atsakanin mu?”
“Aunty Aneelerh please kada ranki ya 6aci, na riga da nayi mata faɗa, abun da ya dace ku harhaɗa mata kudin da zata turama ƴan uwan nata”
Zahra sarkin tausayi tace”nida da halima wallahi da sun dawo gidan nan da zama.....” wata uwar harara Mahboob Ya watsa mata”saboda ke zaki ciyar dasu ko”? Fashewa sukayi da dariya.
Aneelerh tace’baka da dama mahboob, yanzu fa ka gama fadin a harhada mata kudi aturawa ƴan uwanta shine kuma don tace su dawo nan da zama kake tada jijiyoyin wuya daga maganar taimako”
Yamutsa fuska mahboob yayi”abun da nake nufi Aunty Aneelerh, ɗan adam ba abun yarda bane, muna iya mu taimake su su kuma su butulce mana shine abunda nake jiye mana, kawai dai ƙwara in taimakon zamuyi masu mu tura masu can su ƙarata”
“Ka faɗi gaskiya mahboob, nima nayi wannan tunanin, Yanzu me yakamata muyi”? Acewar Aneelerh.
Zahra tayi karaf ta kar6e dacewa”kowa ya kawo abunda yake dashi hada kai mahboob nakama sai yafi yawa tunda kaine jagaba atafiyar”
Harararta yayi”zahra ki daina wannan maganar, ni bawai bazan bada ba, idan na bada ai ba faduwa nayi ba, duk wanda ya taimaki wani shima Allah zai ji ƙansa, ga lada da mutun zai samu, kawai dai ni bani da kuɗinne Yanzu.....” ya fada yana soso keyarshi.
da zolaya zahra tace”hmmm, Ana fa ba musulma bace, ta ina zamu samu lada idan muka taimake ta”?
Banza yayi da ita baice komai ba, Aneelerh tace”babu ruwanmu da wannan, don Allah zamuyi da kyakkyawar niya, kidaina wannan tunanin” gyaɗa kai zahra tayi”shikenan naji, zan bata wani abu cikin kuɗin dana samu, Mahboob Idan kana da acct number dinta ka tura min” Aneelerh tace”Ina da ita, Idan muka koma ɗaki zan tura maki, Nima zan sanya nawa kudin”
Farin ciki ne tsantsa akan fuskar mahboob, Yaji daɗi zasu taimaki Ana batare da ko sisin shi ba.
“Allah yabarmun ku sisters dina, zahra Allah ya baki miji nagari mai sonki mai ƙaunarki, and aunty Aneelerh ubangiji Allah ya bayyanar mana da mijinki da ƴan uwansa , Allah ya raya mana baby junaid dinmu....” addu’o’i yadinga yi masu suna amsa mashi da ameen, kafin Ya juya zai fuce daga kitchen din
“Mahboob” kiran sunanshi da Aneelerh tayine ya dakatar da shi daga yin tafiyar ya waiwayo yana kallonta
“Please idan ka fita ka faɗama su mami, zuwa anjima Hajiya adama zata zo kawo mana baby junaid nasan bata sanar da ita ba”
“Aunty Aneelerh ashe yau muna da babban baƙo agidan namu, mutumina zai dawo, zamu dasa daga inda muka tsaya”
Murmushi Aneelerh tasaki, zahra tace”wallahi har na kosa in ganshi,Yau zaisha daƙuna duk saina sale mashi fatarshi” Aneelerh na murmushi tace”inaso zamu shirya masu abincin da zasu ci, tun da Ana bata jin dadin zuciyarta mubarta ta huta sai muyi aikin atare”
Zahra tace”Lafiyalou, dama na kwana biyu banyi girki ba, har cake zan haɗama baby junaid dina”
Sun jima suna yin fira a kitchen kafin daga bisani suka fuce zuwa ɗakin domin yin sallar azhar da aka fara kira.
*OBIE ESTATE🌃*
Idan muka koma 6angaren dattijon arziƙi, tunda garin Allah ya waye Hankalinshi ba akwance Yake ba, gaba ɗaya yabi ya furgice masu sun rasa gane kanshi, ko jiya da dare bai runtsa ba, sambatu yadinga yi masu yana firgita yana fadin ga macijij nan zai sare shi, Ina owais dinshi Yana gani za’a cutar da shi bazai kashe macijin ba, mutun biyu da suka taya shi kwana a ɗaki his excellency Deen ne tare da His excellency abdul razak, su kansu basu yi bacciba jiya saboda halin da baban nasu yake aciki, hatta sallar asuba agida sukayi ta yaƙi fita daga ɗaki, kuma ya hana su tafi subarshi, bawan Allah ba ƙaramin jiki yaji ba, hada ruɗun tsufa ke damun shi, daƙyar suka samu nasarar sanya shi yin baccin dole.
A yanzu haka Yana daga kwance saman gadonshi Ya ɗaura kanshi kan pillow, deen da Abdul razak suna a zaune saman arm chairs din dakin idanuwansu akan fuskar baba obie.
Jin motsin buɗe kofane Yaja hankalinsu ga kallon mai shigowa
Senate lateef ne, fuskarshi babu walwala.
Daren jiya da damuwar abunda ya faru ya kwana
Miƙa masu hannu yai suka gaisa da ƴan uwan nashi
Kafin ya dubi baban nasu dake kwance kan gado yace”Bacci yake yi ko idon shi biyu”?
His excellency Deen ne yace”bacci yake yi, daƙyar muka samu Ya runtsa” ajiyar zuciya senate lateef ya sauke kafin yace”banji dadin abunda ya faru jiya ba, gashi har yana neman zautar mana da mahaifinmu, wai taya ma akai har maciji ya shigo part din nan”? Rai amatuƙar 6ace yayi maganar
His excellency Abdul razak Yace”abun da yafi ɗaura min kai shi Owais din Yace ba maciji bane mutunne ya rikiɗa....”tunkan Ya ƙare maganar Senate lateef yace”inko dagaske ne wannan maganar to kuwa ba mutun bane dama, Aljani ne sannan ita wannan ifritun yarinyar mai kasada dana gani atare da shi wacece ita!”? Kafin wani ya bashi amsa sallamar Pravin ta katse masu hanzarinsu,
Shigowa yai cikin shiga ta black suit.
Cikin girmamawa pravin ya gaishe da su, bayan sun amsa masu fuskokinsu babu walwala, pravin ya soma yin magana
“Baba bashi da lafiya ne? naga da asuba bai halarcin masallaci ba”
“Baka ga abun da ya faru jiya bane”? Acewar senate lateef.
“Nagani, kar dai ace shi ne ya hana shi sukuni”? Cikin nuna kulawa yayi maganar.
Aneelerh tace”Jinin ku Ya haɗune dana juna, Allah yasa ta zama surukarki kinga shikenan kema zaki samu matsugunni a obie estate” wani irin ihun farin ciki zahra tasaki hada jujjuya qugu tana fadin”Amen Ya Allah, Aunty Aneelerh Allah ya kar6i addu’arki”
Dariya Aneelerh tasaki yayin da take ɗauraye plates din da take wanke wa da ruwan dake fita a faucet.
“Zahra baki faɗamin haduwarki da mutumin ba”?
Kwa6e fuska zahra tayi annurin fuskarta ya ragu.
“Bai zo taron ba, duk irin burin dana ci nason ganinshi bai halarta ba, banji dadi ba dama nasan zai yi wuya yaje saboda mutunne shi da baisan hayaniya”
“Eyyah zahra najiye maki baƙin ciki, in sha Allah wata rana zaku haɗu da shi”
Ta6e baki tayi”Ni yanzu ba wannan ba auntyna, Inataso in baki labarin Nazli da Yazrin Ƴa’ƴan Prime minister da ƙanwar Chief Owais hindu, kinga waɗannan dana lissafa maki ƙarshene su afagen kyau da aji, cikin maza kuwa in ka cire chief owais sai wani ɗan uwansu menene ma sunanshi.....” ta faɗa tana cizon yatsa takasa tuna sunan.
“Namanta, shima a canada yake zaune, mutumin ya iya ɗaukar wanka, ga kyau da aji bayan shi sai twins sun haɗuwa sunyi kyau kamar dollars.
Dariya Aneelerh tayi, jin yadda zahra ta haƙiƙance tana bata labari ko gajiya batayi.
“Yanzu faɗa min alherin da sukayi maki naji ɗazu kince zaki fada min”
Gyara tsayuwa zahra tayi kafin tace
“Kinga da farko Hajiya saratu tayi min kyautar tsadadden leshi guda biyu, da hand bag, hada set na agogo da zobe, da turarurruka......” jinjina kai Aneelerh ta yi tana fadin”masha Allah, zahra najiye maki daɗi, kin samu na sallah”
“Bangama fada maki ba, bayan kuɗin aikin decoration da hajiya saratu ta biyamu, prime minsiter yayi mana kyautar kuɗi duk mutun ɗaya 1.5 million” waro ido waje Aneelerh tayi mahboob dake la6e jin an ambaci kuɗi sai gashi ya dawo gefen zahra Yana raira waƙa.
“In rabo ya tsago dakai kuma abun ya tabbatar saida kai to rabbine yace sai da kai in sai da kai kawai sai da kai, don haka nima Allah ne ya tsaga da rabona ashe arziƙine ke kirana......” gaba ɗaya suka sanya dariya, Aneelerh tace”mahboob yaushe ka shigo kitchen din nan”
Da murmushi akan fuskarshi yace”tun ɗazu ina la6e bakin ƙofa na kasa kunne ina sauraron aku sarkin ɗumi, yau surutun zahra yayi min rana wannan arziƙi haka, wato saboda baƙin ciki zahra ƙiri ƙiri kika hana in rakaki obie estate da yanzu hadani za’ayi rabon kuɗin nan....”
Dariya zara tayi tana fadin”ai baka ji komai ba, bayan kuɗin da prime minister yabamu, president Ya ƙara mana, duk mutun ɗaya dubu ɗari takwas” dafe ƙirji mahboob yayi kamar wanda yaji wani mugun abun
“Sannan Abokin Baba Obie, Jan kunne ya raba mana dubu ɗari biyar biyar da dollar ya bamu su”
Kallon juna mahboob da Aneelerh su kayi.
“Anya zahra dagaske kike kuwa? Wannan kuɗi haka kamar akan bishiya ake tsunkosu”
Hararar shi zahra tayi”an gaya maka kowa mai maƙone irinka, ai su a wurinsu kuɗin da suka bamu bakomai bane”
Jinjina kai mahboob yayi”Allahumma arzuƙni, Sister Yanzu ina kuɗin suke? inaso zan tayaki ƙirgawa”
Dariyar shaƙiyanci zahra tayi kafin tace”suna kwance cikin account bank dina suna bacci, dollar din da aka ba mu ne kaɗai suke a dakina kuma na 6oye su saboda nasan halinka sarai, tsaf zaka Iya zuwa ɗaki yi min halin 6era”
Dariya Aneelerh tasaki, a lokacin ta kammala yin wanke wanken, ta mayar da hankali akan fuskar zahra
Mahboob Yace”kar dai kice zakiyi min rashin mutunci wallahi sai inyi zuciya inje in nemi auran ɗaya daga cikin jikokin baba obie”
Dariya suka saki gaba dayansu bayan sun tsagaita Aneelerh ta dubi mahboob”Ya ake ciki? Kunyi magana da Ana”?
Ɗaga mata kai yai alamar eh, zahra tace me ya faru ne ko bata da lafiya”
Nan mahboob Ya kwashe komai Ya sanar dasu dangane da halin da Ana take aciki.
Shiru sukayi jikin kowa yayi sanyi, musamman Aneelerh, ranta Ya dan 6aci bata ji dadin ƙin gaya matan da tayi ba.
“Idan kuwa hakana Ana bata kyauta min ba,Yanzu har akwai abunda zata 6oye min duk irin shaƙuwar dake atsakanin mu?”
“Aunty Aneelerh please kada ranki ya 6aci, na riga da nayi mata faɗa, abun da ya dace ku harhaɗa mata kudin da zata turama ƴan uwan nata”
Zahra sarkin tausayi tace”nida da halima wallahi da sun dawo gidan nan da zama.....” wata uwar harara Mahboob Ya watsa mata”saboda ke zaki ciyar dasu ko”? Fashewa sukayi da dariya.
Aneelerh tace’baka da dama mahboob, yanzu fa ka gama fadin a harhada mata kudi aturawa ƴan uwanta shine kuma don tace su dawo nan da zama kake tada jijiyoyin wuya daga maganar taimako”
Yamutsa fuska mahboob yayi”abun da nake nufi Aunty Aneelerh, ɗan adam ba abun yarda bane, muna iya mu taimake su su kuma su butulce mana shine abunda nake jiye mana, kawai dai ƙwara in taimakon zamuyi masu mu tura masu can su ƙarata”
“Ka faɗi gaskiya mahboob, nima nayi wannan tunanin, Yanzu me yakamata muyi”? Acewar Aneelerh.
Zahra tayi karaf ta kar6e dacewa”kowa ya kawo abunda yake dashi hada kai mahboob nakama sai yafi yawa tunda kaine jagaba atafiyar”
Harararta yayi”zahra ki daina wannan maganar, ni bawai bazan bada ba, idan na bada ai ba faduwa nayi ba, duk wanda ya taimaki wani shima Allah zai ji ƙansa, ga lada da mutun zai samu, kawai dai ni bani da kuɗinne Yanzu.....” ya fada yana soso keyarshi.
da zolaya zahra tace”hmmm, Ana fa ba musulma bace, ta ina zamu samu lada idan muka taimake ta”?
Banza yayi da ita baice komai ba, Aneelerh tace”babu ruwanmu da wannan, don Allah zamuyi da kyakkyawar niya, kidaina wannan tunanin” gyaɗa kai zahra tayi”shikenan naji, zan bata wani abu cikin kuɗin dana samu, Mahboob Idan kana da acct number dinta ka tura min” Aneelerh tace”Ina da ita, Idan muka koma ɗaki zan tura maki, Nima zan sanya nawa kudin”
Farin ciki ne tsantsa akan fuskar mahboob, Yaji daɗi zasu taimaki Ana batare da ko sisin shi ba.
“Allah yabarmun ku sisters dina, zahra Allah ya baki miji nagari mai sonki mai ƙaunarki, and aunty Aneelerh ubangiji Allah ya bayyanar mana da mijinki da ƴan uwansa , Allah ya raya mana baby junaid dinmu....” addu’o’i yadinga yi masu suna amsa mashi da ameen, kafin Ya juya zai fuce daga kitchen din
“Mahboob” kiran sunanshi da Aneelerh tayine ya dakatar da shi daga yin tafiyar ya waiwayo yana kallonta
“Please idan ka fita ka faɗama su mami, zuwa anjima Hajiya adama zata zo kawo mana baby junaid nasan bata sanar da ita ba”
“Aunty Aneelerh ashe yau muna da babban baƙo agidan namu, mutumina zai dawo, zamu dasa daga inda muka tsaya”
Murmushi Aneelerh tasaki, zahra tace”wallahi har na kosa in ganshi,Yau zaisha daƙuna duk saina sale mashi fatarshi” Aneelerh na murmushi tace”inaso zamu shirya masu abincin da zasu ci, tun da Ana bata jin dadin zuciyarta mubarta ta huta sai muyi aikin atare”
Zahra tace”Lafiyalou, dama na kwana biyu banyi girki ba, har cake zan haɗama baby junaid dina”
Sun jima suna yin fira a kitchen kafin daga bisani suka fuce zuwa ɗakin domin yin sallar azhar da aka fara kira.
*OBIE ESTATE🌃*
Idan muka koma 6angaren dattijon arziƙi, tunda garin Allah ya waye Hankalinshi ba akwance Yake ba, gaba ɗaya yabi ya furgice masu sun rasa gane kanshi, ko jiya da dare bai runtsa ba, sambatu yadinga yi masu yana firgita yana fadin ga macijij nan zai sare shi, Ina owais dinshi Yana gani za’a cutar da shi bazai kashe macijin ba, mutun biyu da suka taya shi kwana a ɗaki his excellency Deen ne tare da His excellency abdul razak, su kansu basu yi bacciba jiya saboda halin da baban nasu yake aciki, hatta sallar asuba agida sukayi ta yaƙi fita daga ɗaki, kuma ya hana su tafi subarshi, bawan Allah ba ƙaramin jiki yaji ba, hada ruɗun tsufa ke damun shi, daƙyar suka samu nasarar sanya shi yin baccin dole.
A yanzu haka Yana daga kwance saman gadonshi Ya ɗaura kanshi kan pillow, deen da Abdul razak suna a zaune saman arm chairs din dakin idanuwansu akan fuskar baba obie.
Jin motsin buɗe kofane Yaja hankalinsu ga kallon mai shigowa
Senate lateef ne, fuskarshi babu walwala.
Daren jiya da damuwar abunda ya faru ya kwana
Miƙa masu hannu yai suka gaisa da ƴan uwan nashi
Kafin ya dubi baban nasu dake kwance kan gado yace”Bacci yake yi ko idon shi biyu”?
His excellency Deen ne yace”bacci yake yi, daƙyar muka samu Ya runtsa” ajiyar zuciya senate lateef ya sauke kafin yace”banji dadin abunda ya faru jiya ba, gashi har yana neman zautar mana da mahaifinmu, wai taya ma akai har maciji ya shigo part din nan”? Rai amatuƙar 6ace yayi maganar
His excellency Abdul razak Yace”abun da yafi ɗaura min kai shi Owais din Yace ba maciji bane mutunne ya rikiɗa....”tunkan Ya ƙare maganar Senate lateef yace”inko dagaske ne wannan maganar to kuwa ba mutun bane dama, Aljani ne sannan ita wannan ifritun yarinyar mai kasada dana gani atare da shi wacece ita!”? Kafin wani ya bashi amsa sallamar Pravin ta katse masu hanzarinsu,
Shigowa yai cikin shiga ta black suit.
Cikin girmamawa pravin ya gaishe da su, bayan sun amsa masu fuskokinsu babu walwala, pravin ya soma yin magana
“Baba bashi da lafiya ne? naga da asuba bai halarcin masallaci ba”
“Baka ga abun da ya faru jiya bane”? Acewar senate lateef.
“Nagani, kar dai ace shi ne ya hana shi sukuni”? Cikin nuna kulawa yayi maganar.