Sashe 115
Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Rage gudun motar tiger yai ta hanyar glass din motarsu suka hango motar major tana tafiya a hankali ga dukkan alamu sun ƙaraso inda dr jazz Yake shiyasa suka rage speed din motar, bayan major yai parking din motarsu, kusan atare suka fito shida wani matashin saurayi dukansu suna asanye cikin kakinsu na sojoji, daga bayan motarsu Tiger yai parking din tasu motar, fitowa sukayi atare shida Sir mubarak, koda su Major sukayi arba dashi a hanzarce suka buga ƙafa tare da sara mashi, Jinjina masu kai Yai yayin da yake bin gine ginen da kallo Ya ce”ina ku ka ga jazz din Ya shiga”? Ya jefa masu tambayar cikin ƙagara da sonjin amsarsu.
Major yace”Wancan gidan mai jan gate Ciki Ya shiga” yai maganar yana nuna wani katafaren gida, Da sauri Sir mubarak Ya nufi gate din, Major da Army din da suke atare kowannansu Ya zaro bindigarshi, shima Tiger Ya curo tashi pistol din, gefe da gefen sir mubarak Suka Jera sun saita bindugunsu saboda tsaro gudun kada akawo masu hari tunda basusan adadin miyagun da yake mu’amala da su ba, Cikin sanɗa suke tafiya suna bin ko’ina da kallo, ta ƙofar jikin gate din da aka bari abuɗe suka shiga, babu kowa abakin gate din tamkar anyi shara, Sir mubarak yace”Anya major akwai mutane acikin ginin nan? Naji shiru babu motsin komai, kodai kunyi kuskurene”? Girgiza kai major yai”Yalla6ai tabbas cikin ginin nan ya shigo, ba mu yi kuskure ba, akan idonmu ya fito daga cikin motarshi Ya buɗe gate kafin Ya koma ciki Yajata zuwa cikin gida”
Gyaɗa kai sir mubarak Yai”okey mu ƙarasa ciki” kaitsaye suka nufi katafaren ginin da suke tsammanin zasu samu hanyar shiga cikin gidan, adai dai bakin wata ƙofa, suka dakata A hankali Major Ya turo ƙofar cikin sa’a suka sameta abuɗe, ɗaya bayan ɗaya suke shiga, Hadadden palour ne An ƙawata shi da furniture, ga sanyin A.c ta ko’ina mai ratsa fatar jikin mutun.
Sunyi mamakin ganin babu kowa a palourn, ko motsin mutun babu, daga cikin falon akwai bene da zai kai mutun up stair, yanke shawarar haurawa saman benan sukayi, Cikin sanɗa suke tafiya kowa ya saita bindigarshi saboda tsaro, a second floor suka dakata da yin tafiyar suna bin ko’ina da kallo, ƙofofin ɗakunane ta ko’ina, Sam sun kasa motsawa saboda sunfara kokwanton anya akwai mutane agidan
Tiger yace”shirun yayi yawa, kada fa ace tarkone aka ɗana mana don mu afka”
Major yace”ai shi soja da kasada akasanshi, Idanma tarkon ne suka shirya mana to bamu bane zamu rufza aciki ba, sune zasu afka, wata’kil watan tonuwar asirin su ne Ya kama”
Sir mubarak Ya natsu Yana sauraronsu, ya rasa madafa sam bayason suyi kuskuren shiga gidan mutane, don ya fara kokwanto.
Army yace”yakamata mu fara dudduba ɗakunan nan wata’ƙil mu same shi aciki” Ya furta hakan tare dakai hannu Ya buɗe ƙofar ɗaki Ɗaya, karaf idanuwanshi suka sauka akan matasan Ƴan matan dake akwance saman bedmattress, cikin shiga ta kayan bacci”a matuƙar ruɗe ya juya yana kallon Sir mubarak Ya furta”yalla6ai ƴan matane kwance saman gado, Anya kuwa bamuyi kuskure ba”! Matsawa sukayi zuwa bakin ƙofar da Army yake a tsaye, kowan nan su Ya leƙa Sun yi mamakin ganin kyawawan ƴan mata kwance suna sharar baccinsu farare tass dasu kamar jinsin larabawa.
Rai amatuƙar 6ace sir mubarak ya dubi Major”kace min nan jazz ya shigo to yana ina? Waɗannan ƴan matan alamace dake nuna cewa Gidan wani ne muka faɗo”
Tuni major yasha jinin jikinshi, Muryarshi adabarbarce ya furta”yalla6ai wallahi da idona naganshi Ya shigo gidan nan, Ga army nan ka tambaye shi, ai tare dashi muka shigo, kuma shima yaga jazz din” Yai maganar yana nuna army da hannun shi
Kallon Army sir Mubarak Yai, da kakkausar murya ya furta”idan har kukasa naji kunya wallahi zakuji ajikin ku ne” hankalinsu ba ƙaramin tashi yai ba, Jin abunda yace masu, Guntun tsoki Yaja tare da juyawa da niyar Ya fuce daga gidan, kwatsam ba zato ba tsammani, kunnuwansu suka soma Jiyo masu shessheƙar Kukan mace cikin murya mai ƙaraji take fasa ƙara tana fadin”Bana so! Ka ƙyaleni Nace maka banaso, Ni ka ƙyaleni, ka sake ni ka rabu dani....” sautin gigitacciyar ƙarar data fasa gaba ɗaya Ya cika ginin, Kallon juna sojojin sukayi kafin da gudun gaske suka nufi Hanyar da suke jiyo sautin kukan Yarinyar, Sir mubarak kamar zai yi tuntube, cikin zafin nama suka haɗa ƙarfi wurin bangaje ƙofar ɗakin, A tsiyace ƙofar ta bude, Hankalin sir mubarak Idan yai dubu to ya tashi, A matuƙar gigice sojojin suke kallon abun da ke faruwa, Lamarin yai matuƙar ɗaga hankulansu, musamman Sir mubarak Ya gaza yadda da abunda idanuwanshi suke nuna mashi, Tuni zufa ta soma wanke fuskarshi,
Sam baiji motsin shigowar mutane ɗakin Ba, Ya duƙufa akan abunda Yake aikatawa, Rigar shaddar shi da wandonshi gaba daya suna asaman floor, Singlet ce kaɗai a jikinshi sai gajeran wando Fari, Ya haɗa uban gumi, matashiyar yarinyar daya danne saman gado sai kuka take Yi, tana bugun bayanshi da hannayenta, A wahalce take harba ƙafafuwanta cikin fitar hayyaci kamar ranta zai fita, ta gama galabaita, tuntana kukan neman agaji har muryarta tafara disashewa, wani irin kukan kura sir mubarak Yai cikin zazzafan taku Ya kutsa kai Cikin ɗaki, da hannayenshi biyu ya damƙo wuyar singlet din Jazz da ƙarfin gaske Ya wurgar dashi kasa gaba ɗaya ya kife kanshi ya daki tiles, Jiki na kerma ya ɗago yana dubansu ɗaya bayan ɗaya kafin ya tsayar da idanuwanshi akan fuskar Sir mubarak dake tsaye kanshi tamkar mayunwacin zaki, hankalinshi yai matuƙar tashi da ganinsu duk yabi ya ruɗe ya susuce, jikinshi ya hauyin kerma, sai faman zazzare idanuwanshi yake Yi, Muryarshi na kakarwa ya furta”daddy....” bai ƙarasa maganar da zaiyi ba, Sir mubarak Ya damƙo wuyanshi ya ɗago dashi tsaye cikin rauni na murya ta wanda ya karaya yake fadin”Jazz ka kasheni, Ka cuceni, dama abunda kake aikawata kenan? Ƴan mata kuke tarawa acikin gida, donku lalata rayuwarsu sannan ku kashe su? Nasha kama ka kanayin waya kana fadin kaji ashe mutanene kajin, Inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un” cikin jin ƙunar rai yace”Wallahi baka isa ka ɗaura min hawan jini baa, Kafin ka kasheni ni zan fara kasheka don ubanka, Mugu azzalumi fasiƙi, Jazz ka bani mamaki, ka cuce ni kuma ka cuci mahaifiyarka,’ Cikin shessheƙar kuka Sir mubarak Yake furta maganar, Ya shaƙe wuyan Jazz sai faman mutsu mutsu yake Yi, don ya ƙwaci kansa.
Yayin da sojojin suke a kewaye da gadon da yarinyar take, duk tabi ta tsorata jikinta sai kerma yake Yi, short gown ce a jikinta, yalwatacciyar baƙar sumar kanta duk ta rufe gefe da gefen fuskarta, tamkar wadda tasha gudu sai faman yin haki take Yi.
Sautin ƙarar da jazz Ya fasane Ya janyo hankulansu ga duban shi, wani irin radadin azabane Ya ziyarce shi sakamakon buga kanshi da sir mubarak Yai jikin Mirror din dakin, gaba ɗaya madubin Ya zube, Jini Ya wanke fuskar Jazz hatta gaban farar shirt din jikinshi Yayi ca6a ca6a da jinin shi, daddafe kanshi yai da hannu bibbiyu cikin mawuyacin hali Yake sambatu “Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un! Daddy ka kashe ni, Na shiga uku na bani na lalace, daddy ka rabani da rayuwata”
Yarinyar dake zaune saman gadon, ganin yadda suka raunata shi yasa ta fasa ƙara da ƙarfi ta furta”yaya Jazz, Wayyo Allah na kun kashe min shi, mugaye azzumai baiyi maku laifin komai ba amma kuna cutar min dashi” Da gudun gaske ta duro daga saman gadon ta kife ƙasa, sam babu natsuwa atare da ita, da rarrafe ta ƙarasa gabanshi, Ta sanya hannu biyu ta ɗago dakanshi ta daura saman laps dinta, Cikin shessheƙar kuka take fadin”Wallahi Allah bazai barku ba, Ku baku da burin daya wuce ku cutar da rayuwar waɗanda basu ji ba basu gani ba, Sai Allah ya saka mashi, ku dukanku sai kun shiga wuta” ta fada tana nuna su da yatsan hannunta, kallon juna sojojin sukayi, sunyi matuƙar girgiza da jin kalaman Yarinyar, sun fara kokwanton Anya kuwa Zargin da sukeyi mashi gaskiya ne? Tayaya yarinyar da ake cutar da rayuwarta, kuma take fada don an ta6a mutumin dake ƙoƙarin rabata da mutuncinta!! Fashewa tayi da kuka Hannayenta tuni sun 6aci da jinin dr jazz tana kuka tana ambaton sunanshi”yaya jaz dan Allah kada ka mutu kabarmu, wallahi idan ka mutu nima saina kashe kaina”
Zuciyar sir mubarak ce ta soma harbawa da ƙarfin gaske, Jiri ya soma ƙoƙarin kwasarshi, Gaba ɗaya ya gama rikicewa, Hankalinshi atashe Yake kallon Kwalaben alluran dake ajiye saman bedside drawer tare da sirinji, hada magunguna, Adaddafe Ya nufi drawer din da niyar Ya duba kwalaban don ganin na menene, sautin ringin wayar Jazz ne Ya dakatar da shi, da sauri ya daura rinannun idanuwanshi inda yake jiyo sautin daga cikin aljihun wandon shaddarshine, Major ne yai saurin daukar wandon Ya binciko wayar cikin aljihun, Ya miƙa ma sir mubarak, yatsun hannun shi na kerma ya ruƙe wayar, batare daya duba sunan mai kira ba Yai picking call din Ya sanya kiran handsfree.
Sautin muryar mutumin dayaji tayi matuƙar gigitar dashi, har baisan sa’adda Ya saki wayar jazz ta fadi saman floor, sojojin dake atare dashi duk sun sha jinin jikinsu, kallon kallo suka soma Yi a tsakaninsu, cikin matsanancin tashin hankali, sautin shessheƙar kukan matashiyar ya cika dakin, dr jazz tuni Ya jima da sumewa.
*EX-PRISONERS💔*
Gaba ɗayansu sun hallara a dining room, domin cin abincin Dinner dinsu, mutun ɗaya ne ke babu acikinsu, Yana can dakin shi, mazan suna fuskantar matan, sunyi shiga kala ɗaya wandon jeans da farar shirt,matan kuma dogayen rigunane a jikinsu, Aunty ummi ce kaɗai ta banbanta dasu, riga da skirt ne ajikinta sun matseta, shape din jikinta Ya bayyana muraran, babu mayafi akanta, sa6anin su Batul da sukayi rolling veils.
Major yace”Wancan gidan mai jan gate Ciki Ya shiga” yai maganar yana nuna wani katafaren gida, Da sauri Sir mubarak Ya nufi gate din, Major da Army din da suke atare kowannansu Ya zaro bindigarshi, shima Tiger Ya curo tashi pistol din, gefe da gefen sir mubarak Suka Jera sun saita bindugunsu saboda tsaro gudun kada akawo masu hari tunda basusan adadin miyagun da yake mu’amala da su ba, Cikin sanɗa suke tafiya suna bin ko’ina da kallo, ta ƙofar jikin gate din da aka bari abuɗe suka shiga, babu kowa abakin gate din tamkar anyi shara, Sir mubarak yace”Anya major akwai mutane acikin ginin nan? Naji shiru babu motsin komai, kodai kunyi kuskurene”? Girgiza kai major yai”Yalla6ai tabbas cikin ginin nan ya shigo, ba mu yi kuskure ba, akan idonmu ya fito daga cikin motarshi Ya buɗe gate kafin Ya koma ciki Yajata zuwa cikin gida”
Gyaɗa kai sir mubarak Yai”okey mu ƙarasa ciki” kaitsaye suka nufi katafaren ginin da suke tsammanin zasu samu hanyar shiga cikin gidan, adai dai bakin wata ƙofa, suka dakata A hankali Major Ya turo ƙofar cikin sa’a suka sameta abuɗe, ɗaya bayan ɗaya suke shiga, Hadadden palour ne An ƙawata shi da furniture, ga sanyin A.c ta ko’ina mai ratsa fatar jikin mutun.
Sunyi mamakin ganin babu kowa a palourn, ko motsin mutun babu, daga cikin falon akwai bene da zai kai mutun up stair, yanke shawarar haurawa saman benan sukayi, Cikin sanɗa suke tafiya kowa ya saita bindigarshi saboda tsaro, a second floor suka dakata da yin tafiyar suna bin ko’ina da kallo, ƙofofin ɗakunane ta ko’ina, Sam sun kasa motsawa saboda sunfara kokwanton anya akwai mutane agidan
Tiger yace”shirun yayi yawa, kada fa ace tarkone aka ɗana mana don mu afka”
Major yace”ai shi soja da kasada akasanshi, Idanma tarkon ne suka shirya mana to bamu bane zamu rufza aciki ba, sune zasu afka, wata’kil watan tonuwar asirin su ne Ya kama”
Sir mubarak Ya natsu Yana sauraronsu, ya rasa madafa sam bayason suyi kuskuren shiga gidan mutane, don ya fara kokwanto.
Army yace”yakamata mu fara dudduba ɗakunan nan wata’ƙil mu same shi aciki” Ya furta hakan tare dakai hannu Ya buɗe ƙofar ɗaki Ɗaya, karaf idanuwanshi suka sauka akan matasan Ƴan matan dake akwance saman bedmattress, cikin shiga ta kayan bacci”a matuƙar ruɗe ya juya yana kallon Sir mubarak Ya furta”yalla6ai ƴan matane kwance saman gado, Anya kuwa bamuyi kuskure ba”! Matsawa sukayi zuwa bakin ƙofar da Army yake a tsaye, kowan nan su Ya leƙa Sun yi mamakin ganin kyawawan ƴan mata kwance suna sharar baccinsu farare tass dasu kamar jinsin larabawa.
Rai amatuƙar 6ace sir mubarak ya dubi Major”kace min nan jazz ya shigo to yana ina? Waɗannan ƴan matan alamace dake nuna cewa Gidan wani ne muka faɗo”
Tuni major yasha jinin jikinshi, Muryarshi adabarbarce ya furta”yalla6ai wallahi da idona naganshi Ya shigo gidan nan, Ga army nan ka tambaye shi, ai tare dashi muka shigo, kuma shima yaga jazz din” Yai maganar yana nuna army da hannun shi
Kallon Army sir Mubarak Yai, da kakkausar murya ya furta”idan har kukasa naji kunya wallahi zakuji ajikin ku ne” hankalinsu ba ƙaramin tashi yai ba, Jin abunda yace masu, Guntun tsoki Yaja tare da juyawa da niyar Ya fuce daga gidan, kwatsam ba zato ba tsammani, kunnuwansu suka soma Jiyo masu shessheƙar Kukan mace cikin murya mai ƙaraji take fasa ƙara tana fadin”Bana so! Ka ƙyaleni Nace maka banaso, Ni ka ƙyaleni, ka sake ni ka rabu dani....” sautin gigitacciyar ƙarar data fasa gaba ɗaya Ya cika ginin, Kallon juna sojojin sukayi kafin da gudun gaske suka nufi Hanyar da suke jiyo sautin kukan Yarinyar, Sir mubarak kamar zai yi tuntube, cikin zafin nama suka haɗa ƙarfi wurin bangaje ƙofar ɗakin, A tsiyace ƙofar ta bude, Hankalin sir mubarak Idan yai dubu to ya tashi, A matuƙar gigice sojojin suke kallon abun da ke faruwa, Lamarin yai matuƙar ɗaga hankulansu, musamman Sir mubarak Ya gaza yadda da abunda idanuwanshi suke nuna mashi, Tuni zufa ta soma wanke fuskarshi,
Sam baiji motsin shigowar mutane ɗakin Ba, Ya duƙufa akan abunda Yake aikatawa, Rigar shaddar shi da wandonshi gaba daya suna asaman floor, Singlet ce kaɗai a jikinshi sai gajeran wando Fari, Ya haɗa uban gumi, matashiyar yarinyar daya danne saman gado sai kuka take Yi, tana bugun bayanshi da hannayenta, A wahalce take harba ƙafafuwanta cikin fitar hayyaci kamar ranta zai fita, ta gama galabaita, tuntana kukan neman agaji har muryarta tafara disashewa, wani irin kukan kura sir mubarak Yai cikin zazzafan taku Ya kutsa kai Cikin ɗaki, da hannayenshi biyu ya damƙo wuyar singlet din Jazz da ƙarfin gaske Ya wurgar dashi kasa gaba ɗaya ya kife kanshi ya daki tiles, Jiki na kerma ya ɗago yana dubansu ɗaya bayan ɗaya kafin ya tsayar da idanuwanshi akan fuskar Sir mubarak dake tsaye kanshi tamkar mayunwacin zaki, hankalinshi yai matuƙar tashi da ganinsu duk yabi ya ruɗe ya susuce, jikinshi ya hauyin kerma, sai faman zazzare idanuwanshi yake Yi, Muryarshi na kakarwa ya furta”daddy....” bai ƙarasa maganar da zaiyi ba, Sir mubarak Ya damƙo wuyanshi ya ɗago dashi tsaye cikin rauni na murya ta wanda ya karaya yake fadin”Jazz ka kasheni, Ka cuceni, dama abunda kake aikawata kenan? Ƴan mata kuke tarawa acikin gida, donku lalata rayuwarsu sannan ku kashe su? Nasha kama ka kanayin waya kana fadin kaji ashe mutanene kajin, Inna lillahi wa’inna ilaihirraji’un” cikin jin ƙunar rai yace”Wallahi baka isa ka ɗaura min hawan jini baa, Kafin ka kasheni ni zan fara kasheka don ubanka, Mugu azzalumi fasiƙi, Jazz ka bani mamaki, ka cuce ni kuma ka cuci mahaifiyarka,’ Cikin shessheƙar kuka Sir mubarak Yake furta maganar, Ya shaƙe wuyan Jazz sai faman mutsu mutsu yake Yi, don ya ƙwaci kansa.
Yayin da sojojin suke a kewaye da gadon da yarinyar take, duk tabi ta tsorata jikinta sai kerma yake Yi, short gown ce a jikinta, yalwatacciyar baƙar sumar kanta duk ta rufe gefe da gefen fuskarta, tamkar wadda tasha gudu sai faman yin haki take Yi.
Sautin ƙarar da jazz Ya fasane Ya janyo hankulansu ga duban shi, wani irin radadin azabane Ya ziyarce shi sakamakon buga kanshi da sir mubarak Yai jikin Mirror din dakin, gaba ɗaya madubin Ya zube, Jini Ya wanke fuskar Jazz hatta gaban farar shirt din jikinshi Yayi ca6a ca6a da jinin shi, daddafe kanshi yai da hannu bibbiyu cikin mawuyacin hali Yake sambatu “Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un! Daddy ka kashe ni, Na shiga uku na bani na lalace, daddy ka rabani da rayuwata”
Yarinyar dake zaune saman gadon, ganin yadda suka raunata shi yasa ta fasa ƙara da ƙarfi ta furta”yaya Jazz, Wayyo Allah na kun kashe min shi, mugaye azzumai baiyi maku laifin komai ba amma kuna cutar min dashi” Da gudun gaske ta duro daga saman gadon ta kife ƙasa, sam babu natsuwa atare da ita, da rarrafe ta ƙarasa gabanshi, Ta sanya hannu biyu ta ɗago dakanshi ta daura saman laps dinta, Cikin shessheƙar kuka take fadin”Wallahi Allah bazai barku ba, Ku baku da burin daya wuce ku cutar da rayuwar waɗanda basu ji ba basu gani ba, Sai Allah ya saka mashi, ku dukanku sai kun shiga wuta” ta fada tana nuna su da yatsan hannunta, kallon juna sojojin sukayi, sunyi matuƙar girgiza da jin kalaman Yarinyar, sun fara kokwanton Anya kuwa Zargin da sukeyi mashi gaskiya ne? Tayaya yarinyar da ake cutar da rayuwarta, kuma take fada don an ta6a mutumin dake ƙoƙarin rabata da mutuncinta!! Fashewa tayi da kuka Hannayenta tuni sun 6aci da jinin dr jazz tana kuka tana ambaton sunanshi”yaya jaz dan Allah kada ka mutu kabarmu, wallahi idan ka mutu nima saina kashe kaina”
Zuciyar sir mubarak ce ta soma harbawa da ƙarfin gaske, Jiri ya soma ƙoƙarin kwasarshi, Gaba ɗaya ya gama rikicewa, Hankalinshi atashe Yake kallon Kwalaben alluran dake ajiye saman bedside drawer tare da sirinji, hada magunguna, Adaddafe Ya nufi drawer din da niyar Ya duba kwalaban don ganin na menene, sautin ringin wayar Jazz ne Ya dakatar da shi, da sauri ya daura rinannun idanuwanshi inda yake jiyo sautin daga cikin aljihun wandon shaddarshine, Major ne yai saurin daukar wandon Ya binciko wayar cikin aljihun, Ya miƙa ma sir mubarak, yatsun hannun shi na kerma ya ruƙe wayar, batare daya duba sunan mai kira ba Yai picking call din Ya sanya kiran handsfree.
Sautin muryar mutumin dayaji tayi matuƙar gigitar dashi, har baisan sa’adda Ya saki wayar jazz ta fadi saman floor, sojojin dake atare dashi duk sun sha jinin jikinsu, kallon kallo suka soma Yi a tsakaninsu, cikin matsanancin tashin hankali, sautin shessheƙar kukan matashiyar ya cika dakin, dr jazz tuni Ya jima da sumewa.
*EX-PRISONERS💔*
Gaba ɗayansu sun hallara a dining room, domin cin abincin Dinner dinsu, mutun ɗaya ne ke babu acikinsu, Yana can dakin shi, mazan suna fuskantar matan, sunyi shiga kala ɗaya wandon jeans da farar shirt,matan kuma dogayen rigunane a jikinsu, Aunty ummi ce kaɗai ta banbanta dasu, riga da skirt ne ajikinta sun matseta, shape din jikinta Ya bayyana muraran, babu mayafi akanta, sa6anin su Batul da sukayi rolling veils.