← Book details Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 145 OF 152

Sashe 145

Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Cike da nishaɗi suke bin waƙar suna dariya fararen hakoransu kamar gonar auduga, ita kanta ummin america ba ƙaramin burgeta sukayi ba, Kamar sakarya haka tasaki baki tana kallonsu, a ƙarshe saita bar masu filin rawar ta koma gefe ɗaya tamkar dj ta goya hannayenta saman kirjinta tana kallonsu ɗaya bayan ɗaya fuskarta ɗauke da ƙayataccen murmushi, sun bata mamaki, daga kunna masu waƙa har sun haddace ta, aranta ta ayyana lallai yaran suna da kaifin basira, yanayin yadda sukeyin rawar suna jujjuya qugunansu yafi komai tafiya da hankalinta, musamman unaisah da parveen sunfi zaƙewa sai kuma uban gayya Sajeed dama shine yafara koya masu rawa tun agidan kurkukun ƙaddara, salon rawarshi kalar ta ƴan club ce, da aji yake yinta hannun shi ruƙe dana Azeezarshi Sun tsunduma suna tiƙar rawa ko gajiya basayi.
Da ƙarfi Sajeed Yace Aunty Ummi ki canza mana wata waƙar mai daɗi”
Da sauri ta ɗauki wayar ta kunna masu waƙar alen walker.
Unaisah na soma jin taken waƙar tayi saurin kamawa tafara bi saboda tasanta tun da jimawa, sajeed ma ya iya waƙar, atare suka haɗa baki suna bin waƙar
Lost in your mind, I wanna know
Am I losin’ my mind?
Never let me go
If this night is not forever, at least we are together
I know I’m not alone
I know I’m not alone
Anywhere, whenever
Apart but still together
I know I’m not alone
I know I’m not alone
I know I’m not alone
I know I’m not alone
Unconscious mind, l’m wide awake
Wanna feel one last time
Take my pain away.......”

Abun da basu sani ba, tun ɗazu boss man Ya shigo ɗakin, yana daga tsaye bakin kofar Ya goya hannayenshi saman kirjinshi, ɗaya bayan ɗaya yake binsu da kallo kafin ya tsayar da idanuwanshi akan Unaisah da ta zaƙe tanata jujjuya qugu tana bin waƙar, tsabar mamakine Ya hanashi yi masu sallama, bai ta6a tsammanin zata Iya yin rawa har haka ba,Yarinyar da kullum take acikin damuwa.
Ummin america tana faman wurwurga eye balls dinta akansu karaf idanuwanta suka hango mata boss man dake atsaye yana kalonsu, da sauri ta kashe sautin, ta kama yin ƴan kame kame, su kuwa prisoners koda ta kashe sautin basu lura da shi ba, a shagwa6e Jemimah ta bubbuga ƙafa tana fadin”wayyo Allah aunty ummi, meyasa kika kashe mana abun, ni wallahi bangaji ba, dan Allah ki sake kunna mana muyi rawa mu girgije” ta faɗa tana karkaɗa ƙaramin qugunta, gaba ɗaya suka tuntsire da dariya.

Banda ummi data kame kanta

“Please aunty ummi ki kunna mana mu ƙarasa yin rawar” acewar parveen
idanuwanta akan fuskar boss dake tsaye yana kallonsu, Sun juya mashi baya shiyasa basusan da zaman shi ba, ita kadaice take Iya ganin shi.

A wayance tace”nifa ba don wani abu na kunna maku sauti ba, kawai na fahimci kuna acikin yanayi na damuwa shiyasa nayi ƙoƙarin don in sanyaku nishaɗi, kuma Alhamdulillah naga canji atare daku....” tunkan ta ƙare maganar, Boss man ya ɗaga hannayenshi yai clapping da ƙarfi haɗi da furta”Sannunku da ƙoƙari” a firgice suka waiwayo baya suna dubanshi kamar wadanda suka ga dodo.
Unaisah hada dafe ƙirji tana fadin”Boss tun yaushe ka shigo dakin nan”?
“Tun time da kika fara rawa ina atsaye ina kallonki” wata irin kunyace ta kamata da sauri ta juya ta nufi saman gado ta haye ta kifa kanta jikin pillow tana dariya.

Hakan da tayi yayi matuƙar bashi dariya.

ɗaura idanuwanshi yayi akan fuskar ummin america sai faman ƙyafƙyafta idanuwanta take yi.

“Ummi Amanar da muka baki kenan? A matsayinki na mamansu kin tarasu akan idonki suke tiƙar ruwa, ke da kanki kika kunna masu sauti, ƙiri ƙiri so kike ki maida mana ƴa’ƴa ƴan rawa ko”?

A ruɗe ta furta”I’m sorry Sir if I offended you, but I didn’t have any bad intentions. I was just trying to make them happy because I noticed they were worried about their brother’s illness. That’s why I tried to cheer them up......” aladabce tayi maganar, tana matuƙar girmama boss man saboda karamcin da yake yi mata, yafi sakar mata fuska akan sauran jami’an isod.

“Kada ki damu babu komai nima nayi maganarne kawai bawai ina nufin hakan ba, ai nasan ba zaki ta6a yin abunda zai 6ata masu tarbiyaba ba, yau dinma kinyine donki ɗebe masu kewa kuma naji dadin hakan Na yaba da tunaninki, tunda gashi nagani da idona kin taimaka masu da kika sanya su nishaɗi, Na jinjina maki” ya faɗa hadi da yi mata alamar jinjina da yatsanshi.
Ƙayataccen murmushi tasakar mashi”nagode da ka fahimce ni”
Mayar da dubanshi yayi akan su sajeed dake tsaye suna kallonsu
“Ay min afwa na katse maku jin daɗin ku, nima ba laifina bane laifin sheikh imam ne daya buƙaci son ganinku don haka in akwai mai ƙorafi ya tanadi abunsa idan munje gabanshi sai ku faɗa mashi” da zolaya yayi masu maganar, murmushi kowan nan su yasaki.
Unaisah jin an ambaci sunan sheikh Imam da kuma maganar yana son ganinsu yasa tayi sauri saukowa daga saman gadon,
A kunyace ta kalli boss man tana faman noƙe kai tace”mu tafi boss”
Ruƙo hannunta yai acikin nashi, da sauri Batool ta ruƙe ɗayan hannun nashi sukayi gaba su naufal suna abiye da bayansu, gaba ɗayansu suka nufi falon hada Ummin America.

A tsakiyar falon su ka dakata da yin tafiyar Boss Man yace”Ku jira anan bari naje na sanar dashi” harya kama hanya zai tafi Unaisah ta kwala mashi kira, a hanzarce ya juya yana kallonta.

Sosa kai ta ɗanyi da hannunta kafin tace”am..dama inaso ne na tambayeka awani hali danish dinmu Yake aciki ne”?

“Ya dawo mutun” wani irin farin cikine Ya lullu6esu, musamman unaisah bakinta yaƙi rufuwa
“sai dai babu ƙarfi a jikin shi, bai iya yin komai ko yatsan hannun shi bai iya ɗagawa” lokaci ɗaya murna ta koma ciki jin abun da Boss man Yace.
jikinsu duk yai sanyi, Unaisah tace”baida lafiyane”? Ɗaga mata kai yai alamar eh, ya ƙara da cewa”kada ki sanya damuwa aranku, zaiji sauƙi in sha Allah, addu’arku yake buƙata”
Cike da zumuɗi tace”zan Iya binka zuwa ɗakin nashi”
Jim ya danyi kafin yace”No, ki tsaya tare da ƴan uwanki, zuwa anjima za’a baku damar ku ganshi” jiki asanyaye ta amsa mashi da toh.
juyawa boss man yayi da sauri Ya haye upstairs.
Ajiyar zuciya kowannansu ya sauke, ummi dake atsaye harta fara gajiya, wuri ta samu saman sofa ta zauna tare da ɗaura ƙafarta ɗaya bisa ɗaya, taci gaba da danna wayar hannunta.
“Mu zauna kafin malamin Ya ƙaraso acewar Unaisah”
Amsa mata su ka yi da toh, kowa ya samu wuri Ya zauna, sanyin A.c sai ratsa fatar jikinsu Yake Yi, sunyi shiru babu mai yin magana acikin su, sai faman ƙyafƙyafta idanuwansu suke Yi, duk sun ƙagara da son ganin malamin

Tsawon mintuna ƙalilan, suka soma jiyo takun takalmansu, a hanzarce su unaisah suka kai dubansu gare su.

Sheikh imam ne agaba, daga bayanshi boss man ne tare da Big Guy.

Tunkafin Ya ƙaraso cikin falon Yake binsu da kallo, hannunshi ruƙe da cazbaharshi, a tsakiyar sofa set din suka dakata da yin tafiyar, ummi sam bata lura da su ba, hankalinta na akan wayarta da take dannawa.
Cikin girmama su unaisah suka sauko daga saman sofa, suka dawo kan carpet, atare suka haɗa baki wurin gaishe da shi, hakan ba ƙaramin burge shi yayi ba, sai faman sakin murmushi yake,
“Masha Allah, kyawawan ƴan mata da samari, fatan na sameku lafiya” amsa mashi sukayi da lafiyalou.
“Alhamdulillah, ubangiji Allah ya Albarkaci rayuwarku...” kafin Sheikh Ya ƙare maganar, Boss man Ya kira sunan ummi, a hankali ta ɗago tana kallon shi”bakiga sheikh imam bane”? Adabarbarce ta mamaita sunan malamin da boss Ya kira mata, kasancewar Ya juya mata baya bata samu damar ganin fuskarshi ba, Jin muyarta yasa sheikh imam yin saurin juyowa baya don ganin wacece..........”

Wani irin mugun bugu zuciyar ummi tayi lokacin da idanuwanta su ka yi tozali da fuskar sheikh imam, tsabar firgita har wayar hannunta sai da ta kubce mata, sheikh imam kuwa tunda ya tsayar da kwayar idanuwansa akan fuskarta bai ko ƙyafta ba, wani irin kallo yake binta dashi mai wuyar fassaruwa, lamarin ya ɗaurewa boss man kai, shi da big guy tare da Unaisah gaba ɗaya Hankalinsu na akansu babu wanda yayi yunƙurin dakatar dasu daga kallon da suke jefawa junansu tsawon mintuna ganin abun nasu ba mai ƙarewa bane yasa Boss man yin gyaran murya, adabarbarce ummi ta soma ƙoƙarin tattara natsuwarta duk tabi ta ruɗe kamar wadda taga wani mugun abu.
Da sauri ta zuƙunna tare dakai yatsun hannunta dake kerma da niyar ta ɗauki wayarta data faɗi kan floor, sai dai kafin ta kai ga yin hakan sheikh imam ya rigata ɗaukar wayartata, lokaci ɗaya ta miƙe ta juya da gudu ta nufi cikin falon sai da tafara taka stairs sautin shessheƙar kukanta ya karaɗe falon.....

Hankalinsu Batool ba ƙaramin tashi yayi ba, Jin sautin kukan aunty umminsu ya jefa su cikin yanayi na damuwa.

da mamaki akan fuskar Boss man Ya furta”Sheikh meke faruwa? Ko kasan ta ne”?

Shiru ya ɗanyi jim yana jujjuya wayar ummi dake a hannunshi na tsawon sakanni, kafin ya soma magana da karyayyar murya”bansanta ba, Yau na fara ganinta” ya faɗa tare da juyowa yana fuskantarsu
Da alamun ruɗu akan fuskar big guy yace”amma meyasa kuka dauki lokaci kuna kallon juna kai da ita? Sannan meyasa ta watsa da gudu tana kuka”?
Fuskar sheikh imam babu walwala Yace”dan Allah kubar maganar nan, kasan dai bazanyi maka ƙarya ba geme geme dani, nima abun da yasa nake kallonta saboda kallon da take yi min, kuka kuma da take yi wata’ƙil nayi mata kama da wani ne da ta rasa a rayuwarta”

Jinjina kai big guy yayi badan Ya gamsu da bayanin shi ba.

“Ga wayarta ku ruƙe mata” ya faɗa yana miƙa ma Boss man, wanda yayi zugudum yana kallon yadda jikin sheikh imam ke tsuma sun fahimci da akwai wani abu da ya 6oye masu wanda baison su sani dangane da ganin ummin america da yayi.

Cikin sanyin murya Unaisah tace”Ni zan kai mata wayar,” ta fada tare dakai hannu ta kar6e phone din daga hannun sheikh imam, ta nufi cikin falon da sauri.
Chapter 145 · 0% Book details