Sashe 72
Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Girgiza kai yai”ban kaiga Yi ba, Yanzu zan shiga toilet din’
“Okey, Ka ajiye plate din idan ka fito sai kaci” ƙaƙaro murmushi yai akan face dinsa”Okay, Dad, I appreciate your care.”
Miƙewa sir mubarak Yai”Ni zan wuce Office, ka kula mun da kanka”
“Daddy Allah Ya dawo min dakai Lafiya, Allah ya tsare mun ya kare mun kai daddyna”
Yaji daɗin maganar Jazz, har saida ya dan juyo ya kalle shi kafin Ya fuce daga ɗakin”
Nauyayyar Ajiyar zuciya Jazz ya sauke, kalaman Sir mubarak sun tsaya mashi aranshi, Cikin sanyin murya ya furta”Am sorry My daddy, Na riga dana jefa kaina Cikin Tarkon da bazan Iya fidda kaina ba, addu’arka kawai nake buƙata Allah Ya bani ikon cinye jarabawar nan”!! Ya ƙare maganar tare da saukowa daga saman gadon ya ɗaura plate din hannun shi saman Table Ya nufi toilet Ya shige.
*Hajjaty the head maids💋*
A tsanake Take Yin tafiya tana nufar haɗaɗɗen garden din gidan, ta ɗauki wankan Sari Launin Ja, Hannunta biyu ruƙe da Tray na Kayan Marmari tare da mugs biyu na black tea, ta ko’ina ƙamshin turare ne ke fita a jikinta, tasha uban ado na sarƙar wuya da awarwaro, make up din fuskarta Ya ƙara mata Kyau.
Tun kafin ta ƙarasa shiga garden din idanuwanta suka hango mata, Obinna tare da babban amininsa daya kawo mashi ziyara, kallo ɗaya zaka yi mashi ka gane Inyamuri ne, fari ne fat sumar kanshi da jagirarshi dukkansu hurhurace, hatta dogon Gemunshi fari ne fat kalar na Obinna, sunyi shigar Manyan Kaya na hausawa, zaman hular kanshi zai ƙara tabbatar maka da ƙabilar shi, suna a zaune saman shimdiɗar da Hajjaty tayi masu ta alfarma, kowan nan su ya tada kanshi saman tuntun kalar na sarakuna.
Tun kafin ta ƙaraso gabansu, ƙamshin turarenta Ya daki hancinan su, abokin obinna Ya furta”masha Allah” Ya kafe ta da ido yana faman Jan gemunshi.
Zuƙunnawa tayi agabansu Ta sauke tray din, cikin girmamawa ta gaishe da abokin”sannu da zuwa, ina wuni Ya iyali” lumshe idonshi yai tare da ware su kan fuskarta, Obinna dake kallonshi ya fahimci kamar baya a hayyacinsa, hajjaty ta tafi da imaninsa, har Ya gaza buɗe baki Ya amsa mata gaisuwarta, Sai faman bin jikinta yake yi da kallon ƙurulla duk tabi ta tsargu.
“Ba ka ji tana gaishe ka ba ne”? Sai da obinna Ya ambaci hakan tukunna Ya iya motsa la66ansa wurin furta”Lafiyalou madam, fatan na same ku lafiya”? Muryarta na rawa ta furta lafiya lou
“Obie, dama matarnan tana agidan nan har yanzu? Yayi tambayar ne saboda lokacin da tazo yi masu shimfiɗa bai kaiga zuwa gidan ba.
Harara obinna ya ɗan watsa mashi a fakaice, kafin ya bashi amsar tambayar shi sai da ya fara kallon hajjaty yace”tashi ki tafi, mun gode” miƙewa ta yi tare da juya ta nufi hanyar fita garden din tsabar sauri kamar zatayi tuntube.
Bayan tafiyarta obinna ya dubi aminin nasa”shegen bisa, faɗamin waya koya maka kallon mata? Ni dai ya iya sanina dakai mace bata agabanka, sai gashi yau kana neman zauce wa saboda kaga Mace” da zolaya ya yi mashi maganar.
Tuntsirewa Inyamurin yai da dariya yana faɗin”Don kawai na gani na yaba, matar ce ba ƙaramin burgeni take yi ba, inason mace mai tsafta da iya ado, sannan kasan Ni ma’aboci son ƙamshine, gaskiya ta tafi da imanina, ka taimaka min inaso na mallake ta, dagaske nake ba wasa ba”
Da mamaki akan fuskar obinna ya ɗan zaro idona yana kallon shi, yayi mamakin jin abun da ya furta, kuma ga dukkan alamu dagaske yake har cikin ranshi.
“Amma dai zolaya ce wannan ko”?
Jan gemun shi yai tare da cewa”na ta6a yi maka zolaya akan irin wannan maganar”? Girgiza kai Obie yai” Bamu ta6a ba, sai dai nayi mamakin kalamanka, tun da muka taso baka ta6a nuna kana buƙatar mace ba, ka haramtawa kanka tara Iyali, gaba daya rayuwarka akan kasuwancinka ta ƙare”
Fuskar Inyamurin da fara’a ya yace”wannan karan dagaske nake, Inasonta da aure mutumina, ka yi min hanyar da zan samu shiga wurinta, don bana son abun ya ɗau lokaci” farin cikine tsantsa akan fuskar obinna abunda yajima yana yi mashi fata
“In sha Allah, zanyi maka ƙoƙarin yin hakan, nima nayi maka sha’awar auranta, Matar tana da hankali da natsuwa”
Cigaba da tattaunawa sukayi a tsakaninsu.
A 6angaren Hajjaty kuwa, Jikinta duk yai sanyi tun da ta baro garden din gabanta ke faɗuwa, tsigar jikinta na tashi, duk akan kallon da abokin obinna yayi mata.
Gaba ɗaya hankalin ta baya atare da ita, tafiya ta ke yi Zuciyarta nayi mata saƙe saƙe, har ta ƙaraso entry hall tana ƙoƙarin bi ta ƙofar palourn Cikin rashin sani suka bangaji juna ita da Hajiya saratu da ke ƙoƙarin fitowa daga falon, Ta kimtsa cikin shiga ta alfarma, da alama wurin aiki zataje.
Da sauri Hajjaty ta ɗago su ka yi tozali da Hajiya saratu, Rass taji gabanta Ya faɗi, Muryarta na kerma ta furta”kiyi haƙuri ban lura dake ba...” daƙyar ta ƙare maganar ganin irin ƙasƙantaccen kallon da Hajiya saratu ke watsa mata.
Tana huci ta furta”baki da hankaline? Ko makauniya ce ke? Wato tsabar nuna isa har kin kai matsayin da zaki iya haɗa kafaɗa ni ko”! Fuskarta a ɗaure tamau tayi maganar.
Hankalin Hajjaty ba ƙaramin tashi yai ba, sam bata lura da pravin dake abayan Hajiya saratu ba, Ya shirya cikin black suit, hannunshi ruƙe da wayarshi daya kara a kunnanshi, Waya yake yi amma hankinsa na akan Hajjaty da hajiya saratu
“Bada sanina na bangaje ki ba, hankalina baya atare dani”
Harara Hajiya Saratu ta watsa mata tamkar ƙwayar idonta zata faɗo ƙasa”Ƴar rainin wayau, wai bana hanaki shafa mahaukacin turaren nan a jikinki ba? Ke baki da hankaline? an gaya maki Zawarci haukane” Rai a6ace ta faɗi hakan tare da ruƙo Mayafin Sarin Hajjaty da hannunta.
Idanuwanta tuni sun ciko tab da ƙwalla.
“Wlh daga rana irin ta yau idan na kuskura na ƙara jin ƙamshin turaren ƴan borin nan naki saina sauke maki kwandon rashin mutunci akanki,”
Azafafe ta ƙare maganar, tare da ingiza hajjaty tayi taga taga zata faɗi, Pravin harya Yunƙura zai tarbeta, da sauri Ya fasa ganin matsiyacin kallon da Hajiya saratu ta watsa mashi
“Wuce muje” cike da isa ta ba shi umarni, da sauri Yabi bayanta suka nufi parking space.
Da ido hajjaty tabi su da kallo, hawaye tuni sun wanke fuskarta, jikinta na rawa ta nufi cikin gidan, masu aikine ke ta kai komo acikin babban palourn.
Ba tare data bari sunyi tozali da wani ba, tayi saurin nufar bedroom dinta, harta kusa shiga taci karo da twins sunyi shirin zuwa office.
Atare suka ɗago suna kallonta, muryarta na rawa ta furta”ina kwananku kun tashi lafiya”
Harara Zayn ya watsa mata”ji wata tambayar rainin wayau nan, taya zaki tambayi mun tashi lafiya? Bayan gamu kin gan mu a tsaye kan ƙafafunmu”
Zaid yace”Zayn, please watch your tongue Hajjaty tamkar uwa take agare mu,” a harzuƙe yace”what! ƴar aikin ce zata zama uwar mu? oh Ko dan saboda tana ƴar india? To ai mu ba indiyawa bane ubanmu ne ɗan can, Nifa baki burgeni saboda ban yadda dake ba, ina zargin hada ke ake cin amanar mahaifiyar mu”
Afirgice Hajjaty ta zazzare ido tana duban fuskar zayn da yayi mata, tuni zufa ta soma tsastsafo mata.
“Pls zayn ya isa haka, idan ba zaka girmamata ba, bai kamata kana gaya mata magana akan idonta ba” yai maganar tare da jan hannun Zayn suka nufi hanyar fita palourn.
Ba zata Iya jure wulaƙancinsu ba, da sauri ta nufi bedroom dinta, tana shiga ta faɗa saman gado ta fashe da matsanancin kuka tamkar ranta zai fita.
Hajiya saratu tuni ta shige cikin mota, pravin na atsaye ya ruƙe murfin motar”Lafiya? Ba zaka shigo bane”? Tayi maganar tana dubanshi ganin yaƙi motsawa Ya kafe ta da ido.
“Bana so na 6ata maki lokaci, Ki tafi kawai Ni zanje a motata” da mamaki akan fuskarta tace”saboda me”?
“Cikina ne Ya 6aci ina buƙatar shiga toilet, “ yai maganar yana shafa flat stomach dinsa
Ta6e baki tai sam bata kawo komai aranta ba tace”Okey, saina dawo” duƙowa ya yi saitin fuskarta ya manna mata peck a fore head dinta”Ki kulamin da kanki My wife, zanyi missing dinki, Ni kona minti ɗaya banaso kiyi nesa dani” kwa6e fuska tayi
“kalaman ka ba zasu hanani tafiya office ba, sai dai su 6ata min lokacina, pls ka kula min da kanka,” murmushin yaƙe ya sakar mata, Aranshi bai ji daɗin maganarta ba, halinta ne bata Iya kalaman soyayyaba kuma ba ta cika son yana yi mata ba.
“please take care of ur self, ayi aiki lafiya”ya ƙare maganar tare da tura murfin motar ya rufe mata ita.
Security din dake zaune a driver seat na motar yaja ta suka nufi shantalelen titin da zai fiddasu daga estate din.
Shu’umin murmushine Ya bayyana akan fuskar Pravin, Jiki na rawa Ya juya ya nufi entry hall, adai dai lokacin twins sun fito hannunsu ruƙe cikin na juna suka ci karo da shi.
Gaba daya suka tsareshi da ido suna kallon shi
Fuskarshi da fara’a ya furta”Kyawawan samarina har Kun kammala Shiryawa za’a tafi office,” zaid ne yai ƙoƙarin faɗin”daddy, ina kwana ka tashi Lafiya” Ya amsa mashi da lafiyalou My son, kafin ya maida dubanshi ga Zayn da ya haɗe rai.
“Lafiya zayn ka tsare ni da ido? Ko ba ka da lafiya ne”? Basarwa yai”lafiyata qalou daddy, just nayi missing dinka ne, amma ya akai daddy naga ka dawo gida? Ba aiki zakaje ba”?
“Key ɗin mota ɗina na bari a ɗaki, shi zanje na ɗauko” zayn yace”bari na ɗauko maka key din” yai maganar yana ƙoƙarin juyawa a hanzarce pravin ya damƙi hannunsa”bana so ku makara yakamata ku wuce ku tafi office, zanje na ɗauko da kaina, Ku kulamin da kanku,’ bai jira amsar su ba, yabi ta gefensu ya nufi cikin falon.
“Zaid sai da na faɗa maka matarcan baƙar munafuka ce, saboda ita daddy yayi mana ƙaryar zai je ya ɗauko car key a ɗaki” Yana huci yayi maganar
Zaid yace”please bro, ka yi mashi kyakkyawan zato, bai kamata kana zarginsu ba”
“Okey, Ka ajiye plate din idan ka fito sai kaci” ƙaƙaro murmushi yai akan face dinsa”Okay, Dad, I appreciate your care.”
Miƙewa sir mubarak Yai”Ni zan wuce Office, ka kula mun da kanka”
“Daddy Allah Ya dawo min dakai Lafiya, Allah ya tsare mun ya kare mun kai daddyna”
Yaji daɗin maganar Jazz, har saida ya dan juyo ya kalle shi kafin Ya fuce daga ɗakin”
Nauyayyar Ajiyar zuciya Jazz ya sauke, kalaman Sir mubarak sun tsaya mashi aranshi, Cikin sanyin murya ya furta”Am sorry My daddy, Na riga dana jefa kaina Cikin Tarkon da bazan Iya fidda kaina ba, addu’arka kawai nake buƙata Allah Ya bani ikon cinye jarabawar nan”!! Ya ƙare maganar tare da saukowa daga saman gadon ya ɗaura plate din hannun shi saman Table Ya nufi toilet Ya shige.
*Hajjaty the head maids💋*
A tsanake Take Yin tafiya tana nufar haɗaɗɗen garden din gidan, ta ɗauki wankan Sari Launin Ja, Hannunta biyu ruƙe da Tray na Kayan Marmari tare da mugs biyu na black tea, ta ko’ina ƙamshin turare ne ke fita a jikinta, tasha uban ado na sarƙar wuya da awarwaro, make up din fuskarta Ya ƙara mata Kyau.
Tun kafin ta ƙarasa shiga garden din idanuwanta suka hango mata, Obinna tare da babban amininsa daya kawo mashi ziyara, kallo ɗaya zaka yi mashi ka gane Inyamuri ne, fari ne fat sumar kanshi da jagirarshi dukkansu hurhurace, hatta dogon Gemunshi fari ne fat kalar na Obinna, sunyi shigar Manyan Kaya na hausawa, zaman hular kanshi zai ƙara tabbatar maka da ƙabilar shi, suna a zaune saman shimdiɗar da Hajjaty tayi masu ta alfarma, kowan nan su ya tada kanshi saman tuntun kalar na sarakuna.
Tun kafin ta ƙaraso gabansu, ƙamshin turarenta Ya daki hancinan su, abokin obinna Ya furta”masha Allah” Ya kafe ta da ido yana faman Jan gemunshi.
Zuƙunnawa tayi agabansu Ta sauke tray din, cikin girmamawa ta gaishe da abokin”sannu da zuwa, ina wuni Ya iyali” lumshe idonshi yai tare da ware su kan fuskarta, Obinna dake kallonshi ya fahimci kamar baya a hayyacinsa, hajjaty ta tafi da imaninsa, har Ya gaza buɗe baki Ya amsa mata gaisuwarta, Sai faman bin jikinta yake yi da kallon ƙurulla duk tabi ta tsargu.
“Ba ka ji tana gaishe ka ba ne”? Sai da obinna Ya ambaci hakan tukunna Ya iya motsa la66ansa wurin furta”Lafiyalou madam, fatan na same ku lafiya”? Muryarta na rawa ta furta lafiya lou
“Obie, dama matarnan tana agidan nan har yanzu? Yayi tambayar ne saboda lokacin da tazo yi masu shimfiɗa bai kaiga zuwa gidan ba.
Harara obinna ya ɗan watsa mashi a fakaice, kafin ya bashi amsar tambayar shi sai da ya fara kallon hajjaty yace”tashi ki tafi, mun gode” miƙewa ta yi tare da juya ta nufi hanyar fita garden din tsabar sauri kamar zatayi tuntube.
Bayan tafiyarta obinna ya dubi aminin nasa”shegen bisa, faɗamin waya koya maka kallon mata? Ni dai ya iya sanina dakai mace bata agabanka, sai gashi yau kana neman zauce wa saboda kaga Mace” da zolaya ya yi mashi maganar.
Tuntsirewa Inyamurin yai da dariya yana faɗin”Don kawai na gani na yaba, matar ce ba ƙaramin burgeni take yi ba, inason mace mai tsafta da iya ado, sannan kasan Ni ma’aboci son ƙamshine, gaskiya ta tafi da imanina, ka taimaka min inaso na mallake ta, dagaske nake ba wasa ba”
Da mamaki akan fuskar obinna ya ɗan zaro idona yana kallon shi, yayi mamakin jin abun da ya furta, kuma ga dukkan alamu dagaske yake har cikin ranshi.
“Amma dai zolaya ce wannan ko”?
Jan gemun shi yai tare da cewa”na ta6a yi maka zolaya akan irin wannan maganar”? Girgiza kai Obie yai” Bamu ta6a ba, sai dai nayi mamakin kalamanka, tun da muka taso baka ta6a nuna kana buƙatar mace ba, ka haramtawa kanka tara Iyali, gaba daya rayuwarka akan kasuwancinka ta ƙare”
Fuskar Inyamurin da fara’a ya yace”wannan karan dagaske nake, Inasonta da aure mutumina, ka yi min hanyar da zan samu shiga wurinta, don bana son abun ya ɗau lokaci” farin cikine tsantsa akan fuskar obinna abunda yajima yana yi mashi fata
“In sha Allah, zanyi maka ƙoƙarin yin hakan, nima nayi maka sha’awar auranta, Matar tana da hankali da natsuwa”
Cigaba da tattaunawa sukayi a tsakaninsu.
A 6angaren Hajjaty kuwa, Jikinta duk yai sanyi tun da ta baro garden din gabanta ke faɗuwa, tsigar jikinta na tashi, duk akan kallon da abokin obinna yayi mata.
Gaba ɗaya hankalin ta baya atare da ita, tafiya ta ke yi Zuciyarta nayi mata saƙe saƙe, har ta ƙaraso entry hall tana ƙoƙarin bi ta ƙofar palourn Cikin rashin sani suka bangaji juna ita da Hajiya saratu da ke ƙoƙarin fitowa daga falon, Ta kimtsa cikin shiga ta alfarma, da alama wurin aiki zataje.
Da sauri Hajjaty ta ɗago su ka yi tozali da Hajiya saratu, Rass taji gabanta Ya faɗi, Muryarta na kerma ta furta”kiyi haƙuri ban lura dake ba...” daƙyar ta ƙare maganar ganin irin ƙasƙantaccen kallon da Hajiya saratu ke watsa mata.
Tana huci ta furta”baki da hankaline? Ko makauniya ce ke? Wato tsabar nuna isa har kin kai matsayin da zaki iya haɗa kafaɗa ni ko”! Fuskarta a ɗaure tamau tayi maganar.
Hankalin Hajjaty ba ƙaramin tashi yai ba, sam bata lura da pravin dake abayan Hajiya saratu ba, Ya shirya cikin black suit, hannunshi ruƙe da wayarshi daya kara a kunnanshi, Waya yake yi amma hankinsa na akan Hajjaty da hajiya saratu
“Bada sanina na bangaje ki ba, hankalina baya atare dani”
Harara Hajiya Saratu ta watsa mata tamkar ƙwayar idonta zata faɗo ƙasa”Ƴar rainin wayau, wai bana hanaki shafa mahaukacin turaren nan a jikinki ba? Ke baki da hankaline? an gaya maki Zawarci haukane” Rai a6ace ta faɗi hakan tare da ruƙo Mayafin Sarin Hajjaty da hannunta.
Idanuwanta tuni sun ciko tab da ƙwalla.
“Wlh daga rana irin ta yau idan na kuskura na ƙara jin ƙamshin turaren ƴan borin nan naki saina sauke maki kwandon rashin mutunci akanki,”
Azafafe ta ƙare maganar, tare da ingiza hajjaty tayi taga taga zata faɗi, Pravin harya Yunƙura zai tarbeta, da sauri Ya fasa ganin matsiyacin kallon da Hajiya saratu ta watsa mashi
“Wuce muje” cike da isa ta ba shi umarni, da sauri Yabi bayanta suka nufi parking space.
Da ido hajjaty tabi su da kallo, hawaye tuni sun wanke fuskarta, jikinta na rawa ta nufi cikin gidan, masu aikine ke ta kai komo acikin babban palourn.
Ba tare data bari sunyi tozali da wani ba, tayi saurin nufar bedroom dinta, harta kusa shiga taci karo da twins sunyi shirin zuwa office.
Atare suka ɗago suna kallonta, muryarta na rawa ta furta”ina kwananku kun tashi lafiya”
Harara Zayn ya watsa mata”ji wata tambayar rainin wayau nan, taya zaki tambayi mun tashi lafiya? Bayan gamu kin gan mu a tsaye kan ƙafafunmu”
Zaid yace”Zayn, please watch your tongue Hajjaty tamkar uwa take agare mu,” a harzuƙe yace”what! ƴar aikin ce zata zama uwar mu? oh Ko dan saboda tana ƴar india? To ai mu ba indiyawa bane ubanmu ne ɗan can, Nifa baki burgeni saboda ban yadda dake ba, ina zargin hada ke ake cin amanar mahaifiyar mu”
Afirgice Hajjaty ta zazzare ido tana duban fuskar zayn da yayi mata, tuni zufa ta soma tsastsafo mata.
“Pls zayn ya isa haka, idan ba zaka girmamata ba, bai kamata kana gaya mata magana akan idonta ba” yai maganar tare da jan hannun Zayn suka nufi hanyar fita palourn.
Ba zata Iya jure wulaƙancinsu ba, da sauri ta nufi bedroom dinta, tana shiga ta faɗa saman gado ta fashe da matsanancin kuka tamkar ranta zai fita.
Hajiya saratu tuni ta shige cikin mota, pravin na atsaye ya ruƙe murfin motar”Lafiya? Ba zaka shigo bane”? Tayi maganar tana dubanshi ganin yaƙi motsawa Ya kafe ta da ido.
“Bana so na 6ata maki lokaci, Ki tafi kawai Ni zanje a motata” da mamaki akan fuskarta tace”saboda me”?
“Cikina ne Ya 6aci ina buƙatar shiga toilet, “ yai maganar yana shafa flat stomach dinsa
Ta6e baki tai sam bata kawo komai aranta ba tace”Okey, saina dawo” duƙowa ya yi saitin fuskarta ya manna mata peck a fore head dinta”Ki kulamin da kanki My wife, zanyi missing dinki, Ni kona minti ɗaya banaso kiyi nesa dani” kwa6e fuska tayi
“kalaman ka ba zasu hanani tafiya office ba, sai dai su 6ata min lokacina, pls ka kula min da kanka,” murmushin yaƙe ya sakar mata, Aranshi bai ji daɗin maganarta ba, halinta ne bata Iya kalaman soyayyaba kuma ba ta cika son yana yi mata ba.
“please take care of ur self, ayi aiki lafiya”ya ƙare maganar tare da tura murfin motar ya rufe mata ita.
Security din dake zaune a driver seat na motar yaja ta suka nufi shantalelen titin da zai fiddasu daga estate din.
Shu’umin murmushine Ya bayyana akan fuskar Pravin, Jiki na rawa Ya juya ya nufi entry hall, adai dai lokacin twins sun fito hannunsu ruƙe cikin na juna suka ci karo da shi.
Gaba daya suka tsareshi da ido suna kallon shi
Fuskarshi da fara’a ya furta”Kyawawan samarina har Kun kammala Shiryawa za’a tafi office,” zaid ne yai ƙoƙarin faɗin”daddy, ina kwana ka tashi Lafiya” Ya amsa mashi da lafiyalou My son, kafin ya maida dubanshi ga Zayn da ya haɗe rai.
“Lafiya zayn ka tsare ni da ido? Ko ba ka da lafiya ne”? Basarwa yai”lafiyata qalou daddy, just nayi missing dinka ne, amma ya akai daddy naga ka dawo gida? Ba aiki zakaje ba”?
“Key ɗin mota ɗina na bari a ɗaki, shi zanje na ɗauko” zayn yace”bari na ɗauko maka key din” yai maganar yana ƙoƙarin juyawa a hanzarce pravin ya damƙi hannunsa”bana so ku makara yakamata ku wuce ku tafi office, zanje na ɗauko da kaina, Ku kulamin da kanku,’ bai jira amsar su ba, yabi ta gefensu ya nufi cikin falon.
“Zaid sai da na faɗa maka matarcan baƙar munafuka ce, saboda ita daddy yayi mana ƙaryar zai je ya ɗauko car key a ɗaki” Yana huci yayi maganar
Zaid yace”please bro, ka yi mashi kyakkyawan zato, bai kamata kana zarginsu ba”