Sashe 50
Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A lokacin Aneelerh da Zahra suna zaune saman gado kowa ya dafi waya suna fira suna chatting, sun ɗauki wankan dogayen riguna
“Ba zaki leƙa wurin surukar taki ba? Kin barta a ɗaki ita kaɗai” acewar zahra
“Ɗazu da safe na shiga na gaishe ta, har ma na tarar da mami zaune suna tattaunawa shiyasa ban tsaya ba,”
“Gaskiya aneelerh ki godewa Allah, surukarki tana da mutunci ta iya magana ga faran faran da jama’a, Ni wlh ba ƙaramin burgeni take yi ba, Inasonta sosai, da ace tana da wani ɗan Bayan Yaya uzair Allah dana aure shi” har cikin zuciyarta take yin maganar,
Aneelerh na murmushi tace”Chief Owais din fa? Ko kin fasa”! farfari Zahra Tayi mata da ido
“shi wannan na dabanne, idan ana maganar ƙarauƙarau ba a maganar Zinari, My dream man inaji araina ma ya kusa dawowa ƙasar jiya har mafarkinsa nayi”
Murmushin gefen fuska Aneelerh ta saki
“Allah Ya cika maki burinki zahra, Ni na ƙosa inga fuskar Owais ɗin nan, har tambayarki nayi hotonsa kinƙi ki nuna min, bansani ba ko rowa kike yi min” dariya Zahra tayi”Ina jin fargabar zuciyarki ta buga silar ganin kyakkyawar fuskarshi, kuma kinga ke matar aure ce bana son ki kalli haramun” Sakin baki aneelerh tayi yayin da take kallonta, tama rasa bakin magana
“Fuskarshi tsadane da ita, idan har zaki Iya biyan farashi sai muyi ciniki in nuna maki” fashewa da dariya aneeleeh tayi jin wani zancen abakin zahra.
Faɗowa Ɗakin Junaid yai tun abakin ƙofa yake faman ƙwala mata kira”Mommy!mommy!” a hanzarce ta kai idonta ga ƙofar
“Babyn mommy lafiya kake ta ƙwalamun kira” tai maganar tare da sakowa daga saman gadon ta nufe shi, hannu biyi tasa ta ɗauke shi tana kallon fuskarshi
“Mommy ana kiranki, ki zo inji su abie”
“Sune sukace ka kira ni”? Ɗaga mta kai yai alamar eh ya ƙara da cewa”ke kaɗai banda Zahra”
Harara zahra Ta wurga mashi”aiko sai naje ɗan baƙin ciki, so kake kayi mun buƙulu wata’ƙil ƙudi ne za’a raba mana,
Saukowa tai daga saman gadon ta ɗauko masu mayafi a closet ita da Aneelerh ta yafa mata akanta, atare suka fuce daga ɗakin zuwa palour
Hankalin Mahboob Ba ƙaramin tashi yai ba, ganin babu zoben a ɗaki, duk yabi ya birkice ɗakin, ya tarwatsa komai, Hatta zanin gadon shi da fululluka duka yayi wurgar dasu saman tiles, ya zazzago da jerin ninkakkun kayansa na cikin wardrobe kaf dinsu Ya bazasu saman gadonshi, zufa ta ko’ina, Bawan Allah shine har ƙarkashin gado neman zobe, Cikin drawer chest, da laundry basket, kanshi harya fara yi mashi ciwo, ya tsani asara a rayuwarshi, a haukace ya tura ƙofar toilet dinsa ya shiga ciki Yana neman zoben, gaba ɗaya ya fara zaucewa, ganin babu zoben a toilet ɗin ya dawo ɗakin, yana haki zufa sai tsastsafo mashi take Yi, Idanuwanshi sunyi jawur dasu luhu luhu yakai maƙura tamkar zai rushe da kuka, jiri ne ya fara ɗibarshi a hanzarce ya koma gefen gadon shi ya zauna tare da sanya hannayenshi biyu ya tarbe kanshi Takaicin duniya ya ishe shi, bakomai yake tunawa ba face kuɗin da Aka sayi zoben, har zazza6i yai daya miƙa su dubu goma sha biyar. Ahakama kuɗin bada guminsa ya same su ba, Abokin shi ne ya siya mashi zoben saboda ya nuna yana so kuma baida kuɗi.
*Boss Bature✍️ Mu haɗu monday Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*
First bank
3196407426,
*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*
_~*BossLadiesWriters*~_
_*KURKUKUN ƘADDARA*_
~Middle step~
_The Prisoners E16🔥💫_
*Daga alƙalamin Boss Bature*
Kusan a tare Aneelerh da zahra su ka shigo palourn, a saman carpet kowan nan su yai zaman cin tuwo Junaid na azaune gefenta, tun da su ka zauna idanuwan su Mami da Abie na akan su, at same time suka haɗa baki wurin gaishe dasu cikin girmamawa, fuskokinsu Uncle abdallah da fara’a suka amsa masu.
Bayan kowan nan su Ya natsu, Hajiya adama ta soma magana cikin nutsastsiyar murya
“Dama jiyane Aneelerh ta ke faɗamin dangane da tada zancen 6acewarsu tajuddeen da za’ayi, a gaskiya naji daɗin jin hakan sosai, Kuma na yabama zahra da ta kawo wannan shawarar ta yi tunani mai kyau” Tun da ta fara magana sun natsu suna sauraronta, Zahra sai faman washe baki take yi jin anyabi shawararta, tana matuƙar son taga An yabeta.
Bayan Hajiya adama ta ƙare magana Uncle abdallah Ya ɗaura da cewa”yanzu haka abun da mu ke tattaunawa akai kenan, Ni kaina Naji daɗin tunanin nan da akayi abune mai kyau da buƙatar atada zancen 6acewar su ya dawo sabo, wata’ƙil ta silar hakan Allah ya agaza mana Muji ɗuriyarsu duk da bamu da tabbacin ko suna araye don ni har yau bana ji araina cewa babu su a doron duniyar nan!”
Numfasawa Abie Yai Kafin ya ɗaura da nashi jawabin”In sha Allahu muna sa ran wannan Karan zamuci nasara, dama dalilin taruwar mu anan don kowa Ya bada tashi shawarar” Bayan Kammala Maganar abie, Uncle ɗan Iya Ya soma magana
“Na riga nayi magana da Ziyad babban ɗan jarida ne, Tun ranar da muka Yi magana da Aneelerh, ta turo min hotunansu already na tura mashi su, da duk wasu bayanai da za’a buƙata, Ya ce min in sha Allah cikin weekend da zamu shiga komai za’a fara yaɗa labarinsu” Murmushine Ya bayyana akan fuskokinsu da alama sun ji daɗin Jin hakan
Uncle abdalla yace”Wai kana Nufin Ziyad ɗan Gidan senate Lateef”?
Jinjina kai Uncle ɗan Iya yayi”ƙwarai kuwa, Ziyad yanzu ae shi ke jan Ragamar Companynsu Na jarida mai suna Obinna News Network (ONT) Yaron Akwai hazaƙa Kullum ne saina bibiyi Labaransu a shafinsu, ƙwararrune a 6angaren Aikin Jarida, duk wani labari da zaiyi trending a social media Sune na farko da zasu fara buga shi a shafinsu”
Uncle abdalla Yace”Allah sarki, Uzair Da tajuddeen Sunci burin yin Aiki a companynsu, suna son Yin aiki tare da Ziyad Allah bai nufa ba” cikin karyayyiyar Murya Uncle abdallah ya ƙarasa maganar, jikin kowan nan su Yai sanyi
“Nima a bakin uzair na ta6a jin labarin Ziyad ɗin nan shahararran ɗan Jarida, “ Acewar Hajiya adama
Uncle ɗan Iya na murmushi yace”Allah sarki, ae muna mutunci da Iyayensu, lokacin da ace nasan suna da burin yin aiki da shi ai dana haɗasu, Yadda Taj da uzair suke da hazaƙa a 6angaren Jarida tabbas da suna atare ba ƙaramin Cigaba za’a samu a ƙasar nan ba, don shima Ziyad ɗin Akwai ƙwalwa Bashi da tsoro gaskiya tsirararta yake faɗin ta” murmushi kowannan su Ya saki.
“Yakamata ka gayyato mana shi agidan nan, tunda kowa nasan ganin shi, Ko da ya ke nasan zaiyi wuya ya iya samun lokacin zuwa sai dai mu muje inda Yake” Abie ne yai maganar
“In dai ziyad ne baku da matsala, mutunne mai sauƙin kai, zan Gayyace zuwa gidan nan”
Tun da suka fara magana sai Yanzu ummi tasa baki”kaga daga nan Idan Yazo sai mu bashi auran zahra....” tunkan ta ƙarasa magana zahra dake chatting da wayarta A sukwane ta ɗago Girarta a haɗe tana kallon fuskar mami.
Hakan da ta yi ba ƙaramin dariya ya basu ba, Uncle ɗan Iya yace”kin kawo shawara mai kyau, Ni kaina nayi tunanin hakan don yaron akwai farin Jinin ƴan mata ita kanta zahra nasan zata ƙyasa” Kifa kai zahra tayi saman cinyoyinta, takaicin Duniya ya isheta, ita da ta ke da burin mallakar Uban gayyar family ɗin su kuma suna yi mata zancen Ziyad.
“Akwai Kyauta ta musamman da zan ba Aneelerh, nasan Itama zata taimaka mana sosai” Hajiya adama ce ta yi maganar idonta Akan uncle abdallah.
“Na baro ta a mota, jiya na manta ban shigo da ita gidan ba, Bari naje na ɗauko” yai maganar yana yunƙurin miƙewa Sai ga Mahboob Kamar an wurgoshi Rai a6ace yake Tafiya Fuskar shi a haɗe babu mutunci.
“Ka koma ka zauna Ga mahboob nan, ka bashi key ɗin motar ya ɗauko maka” Karaf acikin kunnanshi Maganar ta sauka, Har ƙara sauri yake yi don yabar falon
Ɗaga murya Uncle ɗan Iya yai”Kai Mahboob zonan” Cak Ya tsaya da yin tafiyar fuskarshi A murtuke ya Juyo Ya nufi inda suke zazzaune saman sofa.
Zuƙunnawa Yai ƙasa Ya ɗago da fuska Yana kallon Abie ɗin nasu
Rai a6ace yace dashi”Mahboob ba ka ga munyi baƙi bane a gidan namu”?
Hannu yasa ya ɗan sosa ƙeyarshi Muryarshi ƙasa ƙasa Ya furta
“Bana Jin ɗaɗi jiya shiyasa ban samu damar zuwa ganin su ba,”
Wani kallo Da Ummi ke wurga mashi daga inda take zaune saman Sofa kamar zata kifa masa mari, Hakan yasa shi yin sauri kallon Uncle Abdallah Ya furta”sannunku da zuwa, ya gajiyar tafiya, ya kuma aka baro mutanan can”
fuskar uncle abdalla asake ya amsa mashi”lafiyalou Mahboob, ya school ko an kammala” fuskar shi ba yabo ba fallasa ya ce”diploma ce na kammala”
Ganin yanayin fuskarshi babu walwala Uncle abdalla yace “Ko dai har yanzu ba lafiyane? Naga kamar baka acikin natsuwarka”
Sai lokacin Ya ɗan sakin murmushin yaƙe “Bakomai, ai naji sauƙi” Iya abunda ya furta kenan, Baby Junaid ya tsareshi da ido, Dariya ce ƙumshe a cikin bakinshi don ya fahimci damuwar rashin zoban shi ce ta sanya shi shiga wannan halin, Cikin kunne yai ma Aneelerh raɗa”Mommy zoben yake nema, kalli idonshi ki gani sunyi jawur, Allah bani bashi mommy sai ya zubar da hawayensa”
Ƙiris ya rage Aneelerh ta saki dariya yayin da take sauraron muryar junaid, ita kanta ta lura da 6acin ran da ke akan fuskar Mahboob.
“zai baka Key ɗin mota, saƙo zaka ɗauko mashi” Fuska a ɗaure uncle ɗan Iya yai mashi maganar, tare da kallon uncle Abdalla
“Bashi key ɗin motar,” acewar ɗan Iya, ciro key ɗin uncle abdallah yayi kafin ya miƙa ma Mahboob, Ya sanya hannu biyu ya kar6a.
Yunƙurawa yai ya miƙe ya fuce daga ɗakin yana ƙunƙuni.
Kafin dawowar Mahboob Junaid Ya miƙe da sauri Ya nufi ɗakin Mommyn shi don Ya duba zoben da su ka 6oye.
“Ba zaki leƙa wurin surukar taki ba? Kin barta a ɗaki ita kaɗai” acewar zahra
“Ɗazu da safe na shiga na gaishe ta, har ma na tarar da mami zaune suna tattaunawa shiyasa ban tsaya ba,”
“Gaskiya aneelerh ki godewa Allah, surukarki tana da mutunci ta iya magana ga faran faran da jama’a, Ni wlh ba ƙaramin burgeni take yi ba, Inasonta sosai, da ace tana da wani ɗan Bayan Yaya uzair Allah dana aure shi” har cikin zuciyarta take yin maganar,
Aneelerh na murmushi tace”Chief Owais din fa? Ko kin fasa”! farfari Zahra Tayi mata da ido
“shi wannan na dabanne, idan ana maganar ƙarauƙarau ba a maganar Zinari, My dream man inaji araina ma ya kusa dawowa ƙasar jiya har mafarkinsa nayi”
Murmushin gefen fuska Aneelerh ta saki
“Allah Ya cika maki burinki zahra, Ni na ƙosa inga fuskar Owais ɗin nan, har tambayarki nayi hotonsa kinƙi ki nuna min, bansani ba ko rowa kike yi min” dariya Zahra tayi”Ina jin fargabar zuciyarki ta buga silar ganin kyakkyawar fuskarshi, kuma kinga ke matar aure ce bana son ki kalli haramun” Sakin baki aneelerh tayi yayin da take kallonta, tama rasa bakin magana
“Fuskarshi tsadane da ita, idan har zaki Iya biyan farashi sai muyi ciniki in nuna maki” fashewa da dariya aneeleeh tayi jin wani zancen abakin zahra.
Faɗowa Ɗakin Junaid yai tun abakin ƙofa yake faman ƙwala mata kira”Mommy!mommy!” a hanzarce ta kai idonta ga ƙofar
“Babyn mommy lafiya kake ta ƙwalamun kira” tai maganar tare da sakowa daga saman gadon ta nufe shi, hannu biyi tasa ta ɗauke shi tana kallon fuskarshi
“Mommy ana kiranki, ki zo inji su abie”
“Sune sukace ka kira ni”? Ɗaga mta kai yai alamar eh ya ƙara da cewa”ke kaɗai banda Zahra”
Harara zahra Ta wurga mashi”aiko sai naje ɗan baƙin ciki, so kake kayi mun buƙulu wata’ƙil ƙudi ne za’a raba mana,
Saukowa tai daga saman gadon ta ɗauko masu mayafi a closet ita da Aneelerh ta yafa mata akanta, atare suka fuce daga ɗakin zuwa palour
Hankalin Mahboob Ba ƙaramin tashi yai ba, ganin babu zoben a ɗaki, duk yabi ya birkice ɗakin, ya tarwatsa komai, Hatta zanin gadon shi da fululluka duka yayi wurgar dasu saman tiles, ya zazzago da jerin ninkakkun kayansa na cikin wardrobe kaf dinsu Ya bazasu saman gadonshi, zufa ta ko’ina, Bawan Allah shine har ƙarkashin gado neman zobe, Cikin drawer chest, da laundry basket, kanshi harya fara yi mashi ciwo, ya tsani asara a rayuwarshi, a haukace ya tura ƙofar toilet dinsa ya shiga ciki Yana neman zoben, gaba ɗaya ya fara zaucewa, ganin babu zoben a toilet ɗin ya dawo ɗakin, yana haki zufa sai tsastsafo mashi take Yi, Idanuwanshi sunyi jawur dasu luhu luhu yakai maƙura tamkar zai rushe da kuka, jiri ne ya fara ɗibarshi a hanzarce ya koma gefen gadon shi ya zauna tare da sanya hannayenshi biyu ya tarbe kanshi Takaicin duniya ya ishe shi, bakomai yake tunawa ba face kuɗin da Aka sayi zoben, har zazza6i yai daya miƙa su dubu goma sha biyar. Ahakama kuɗin bada guminsa ya same su ba, Abokin shi ne ya siya mashi zoben saboda ya nuna yana so kuma baida kuɗi.
*Boss Bature✍️ Mu haɗu monday Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*
First bank
3196407426,
*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*
_~*BossLadiesWriters*~_
_*KURKUKUN ƘADDARA*_
~Middle step~
_The Prisoners E16🔥💫_
*Daga alƙalamin Boss Bature*
Kusan a tare Aneelerh da zahra su ka shigo palourn, a saman carpet kowan nan su yai zaman cin tuwo Junaid na azaune gefenta, tun da su ka zauna idanuwan su Mami da Abie na akan su, at same time suka haɗa baki wurin gaishe dasu cikin girmamawa, fuskokinsu Uncle abdallah da fara’a suka amsa masu.
Bayan kowan nan su Ya natsu, Hajiya adama ta soma magana cikin nutsastsiyar murya
“Dama jiyane Aneelerh ta ke faɗamin dangane da tada zancen 6acewarsu tajuddeen da za’ayi, a gaskiya naji daɗin jin hakan sosai, Kuma na yabama zahra da ta kawo wannan shawarar ta yi tunani mai kyau” Tun da ta fara magana sun natsu suna sauraronta, Zahra sai faman washe baki take yi jin anyabi shawararta, tana matuƙar son taga An yabeta.
Bayan Hajiya adama ta ƙare magana Uncle abdallah Ya ɗaura da cewa”yanzu haka abun da mu ke tattaunawa akai kenan, Ni kaina Naji daɗin tunanin nan da akayi abune mai kyau da buƙatar atada zancen 6acewar su ya dawo sabo, wata’ƙil ta silar hakan Allah ya agaza mana Muji ɗuriyarsu duk da bamu da tabbacin ko suna araye don ni har yau bana ji araina cewa babu su a doron duniyar nan!”
Numfasawa Abie Yai Kafin ya ɗaura da nashi jawabin”In sha Allahu muna sa ran wannan Karan zamuci nasara, dama dalilin taruwar mu anan don kowa Ya bada tashi shawarar” Bayan Kammala Maganar abie, Uncle ɗan Iya Ya soma magana
“Na riga nayi magana da Ziyad babban ɗan jarida ne, Tun ranar da muka Yi magana da Aneelerh, ta turo min hotunansu already na tura mashi su, da duk wasu bayanai da za’a buƙata, Ya ce min in sha Allah cikin weekend da zamu shiga komai za’a fara yaɗa labarinsu” Murmushine Ya bayyana akan fuskokinsu da alama sun ji daɗin Jin hakan
Uncle abdalla yace”Wai kana Nufin Ziyad ɗan Gidan senate Lateef”?
Jinjina kai Uncle ɗan Iya yayi”ƙwarai kuwa, Ziyad yanzu ae shi ke jan Ragamar Companynsu Na jarida mai suna Obinna News Network (ONT) Yaron Akwai hazaƙa Kullum ne saina bibiyi Labaransu a shafinsu, ƙwararrune a 6angaren Aikin Jarida, duk wani labari da zaiyi trending a social media Sune na farko da zasu fara buga shi a shafinsu”
Uncle abdalla Yace”Allah sarki, Uzair Da tajuddeen Sunci burin yin Aiki a companynsu, suna son Yin aiki tare da Ziyad Allah bai nufa ba” cikin karyayyiyar Murya Uncle abdallah ya ƙarasa maganar, jikin kowan nan su Yai sanyi
“Nima a bakin uzair na ta6a jin labarin Ziyad ɗin nan shahararran ɗan Jarida, “ Acewar Hajiya adama
Uncle ɗan Iya na murmushi yace”Allah sarki, ae muna mutunci da Iyayensu, lokacin da ace nasan suna da burin yin aiki da shi ai dana haɗasu, Yadda Taj da uzair suke da hazaƙa a 6angaren Jarida tabbas da suna atare ba ƙaramin Cigaba za’a samu a ƙasar nan ba, don shima Ziyad ɗin Akwai ƙwalwa Bashi da tsoro gaskiya tsirararta yake faɗin ta” murmushi kowannan su Ya saki.
“Yakamata ka gayyato mana shi agidan nan, tunda kowa nasan ganin shi, Ko da ya ke nasan zaiyi wuya ya iya samun lokacin zuwa sai dai mu muje inda Yake” Abie ne yai maganar
“In dai ziyad ne baku da matsala, mutunne mai sauƙin kai, zan Gayyace zuwa gidan nan”
Tun da suka fara magana sai Yanzu ummi tasa baki”kaga daga nan Idan Yazo sai mu bashi auran zahra....” tunkan ta ƙarasa magana zahra dake chatting da wayarta A sukwane ta ɗago Girarta a haɗe tana kallon fuskar mami.
Hakan da ta yi ba ƙaramin dariya ya basu ba, Uncle ɗan Iya yace”kin kawo shawara mai kyau, Ni kaina nayi tunanin hakan don yaron akwai farin Jinin ƴan mata ita kanta zahra nasan zata ƙyasa” Kifa kai zahra tayi saman cinyoyinta, takaicin Duniya ya isheta, ita da ta ke da burin mallakar Uban gayyar family ɗin su kuma suna yi mata zancen Ziyad.
“Akwai Kyauta ta musamman da zan ba Aneelerh, nasan Itama zata taimaka mana sosai” Hajiya adama ce ta yi maganar idonta Akan uncle abdallah.
“Na baro ta a mota, jiya na manta ban shigo da ita gidan ba, Bari naje na ɗauko” yai maganar yana yunƙurin miƙewa Sai ga Mahboob Kamar an wurgoshi Rai a6ace yake Tafiya Fuskar shi a haɗe babu mutunci.
“Ka koma ka zauna Ga mahboob nan, ka bashi key ɗin motar ya ɗauko maka” Karaf acikin kunnanshi Maganar ta sauka, Har ƙara sauri yake yi don yabar falon
Ɗaga murya Uncle ɗan Iya yai”Kai Mahboob zonan” Cak Ya tsaya da yin tafiyar fuskarshi A murtuke ya Juyo Ya nufi inda suke zazzaune saman sofa.
Zuƙunnawa Yai ƙasa Ya ɗago da fuska Yana kallon Abie ɗin nasu
Rai a6ace yace dashi”Mahboob ba ka ga munyi baƙi bane a gidan namu”?
Hannu yasa ya ɗan sosa ƙeyarshi Muryarshi ƙasa ƙasa Ya furta
“Bana Jin ɗaɗi jiya shiyasa ban samu damar zuwa ganin su ba,”
Wani kallo Da Ummi ke wurga mashi daga inda take zaune saman Sofa kamar zata kifa masa mari, Hakan yasa shi yin sauri kallon Uncle Abdallah Ya furta”sannunku da zuwa, ya gajiyar tafiya, ya kuma aka baro mutanan can”
fuskar uncle abdalla asake ya amsa mashi”lafiyalou Mahboob, ya school ko an kammala” fuskar shi ba yabo ba fallasa ya ce”diploma ce na kammala”
Ganin yanayin fuskarshi babu walwala Uncle abdalla yace “Ko dai har yanzu ba lafiyane? Naga kamar baka acikin natsuwarka”
Sai lokacin Ya ɗan sakin murmushin yaƙe “Bakomai, ai naji sauƙi” Iya abunda ya furta kenan, Baby Junaid ya tsareshi da ido, Dariya ce ƙumshe a cikin bakinshi don ya fahimci damuwar rashin zoban shi ce ta sanya shi shiga wannan halin, Cikin kunne yai ma Aneelerh raɗa”Mommy zoben yake nema, kalli idonshi ki gani sunyi jawur, Allah bani bashi mommy sai ya zubar da hawayensa”
Ƙiris ya rage Aneelerh ta saki dariya yayin da take sauraron muryar junaid, ita kanta ta lura da 6acin ran da ke akan fuskar Mahboob.
“zai baka Key ɗin mota, saƙo zaka ɗauko mashi” Fuska a ɗaure uncle ɗan Iya yai mashi maganar, tare da kallon uncle Abdalla
“Bashi key ɗin motar,” acewar ɗan Iya, ciro key ɗin uncle abdallah yayi kafin ya miƙa ma Mahboob, Ya sanya hannu biyu ya kar6a.
Yunƙurawa yai ya miƙe ya fuce daga ɗakin yana ƙunƙuni.
Kafin dawowar Mahboob Junaid Ya miƙe da sauri Ya nufi ɗakin Mommyn shi don Ya duba zoben da su ka 6oye.