← Book details Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 128 OF 152

Sashe 128

Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Ya laluba hannu ya damƙo wayar, murmushin mugunta ya saki kafin ya ɗaga kiran.

Ko sallama babu hajiya saratu tace”pravin ina ka shiga? Ina ta kira baka picking! Ba zaka dawo daki ka kwanta ba ne”?

Tun daga kan muryarta ya fahimci babu natsuwa atare da ita
“Me zan dawo nayi maki? Ni da bani da amfani awajenki”?
Muryarta tamkar zata fashe mashi da kuka tace’kaga ni ba wannan na tambayeka ba, ina son ganinka ka, pravin, hankalina ba akwance yake ba, nasan kaga abunda ya faru ɗazu”

Tuntsirewa yayi da dariyar mugunta, ran hajiya saratu ya 6aci matuƙar masifa ta soma zazzaga mashi sai da tayi mai isarta tukunna ya katse ta da cewa”saratu kenan, kefa da kanki kikace nine ɗan kwali ke ce hula, hakan na nufin kece namiji ko? To meyasa kike neman mace donta baki kariya? A tunanina ni yakamata inji tsoro bake ba, shi namiji da jarumta aka san shi bada ragwantaka ba”!

Takaicin duniya ya ishi hajiya saratu, cikin lalama tace”pravin dan Allah ka dawo ɗaki, idan saboda abun da na fada maka ne ya 6ata maka rai, zan baka haƙuri”

“Bana buƙatar haƙurin ki saratu, lokacin daya dace ki lallasheni ki tarairayeni ki bani hakuri bakiyi ba till now da buƙatar kan ki ce ko? An gaya maki ni shashashane bansan ciwon kaina ba”?

Shiru bata tanka mashi ba, kuma tana sauraronshi.

“Ko gobe kada kiyi tunanin zan dawo gida, ni yanzu haka ma gani akwance tare da wadda tafi ki iya tarairayar miji.....”tsawar da ta daka mashi ce ta sanya shi yin shiru, tamkar zata fasa mashi screen din wayarshi”ya isa haka! Ya isa! Kada ka ƙara maimaita min maganar da kayi idan ba so kake ranka ya 6aci ba......” bata ƙare maganar ba, yai rejecting kiran, Ya jefar da wayar saman mattress, Ya janyo hajjaty a jikinshi, ya daura hannunshi saman sumar kanta, har cikin ranshi yana ƙara jin ƙaunarta, bai da tamkarta a duniyar nan, saboda kyautata mashin da take Yi, yana matuƙar ƙaunarta, kiss ya manna mata saman forehead nata, kafin ya cusa kanshi gefen wuyanta, ƙamshin turarenta ya daki hancinsa ahaka bacci yai awon gaba da shi.

Jefar da wayar hannunta tayi saman gado, ranta ya 6aci matuƙa pravin ya ƙona mata rai, kishine da ita, gani take kamar dagaske ne abun da ya faɗa mata yana can shida wata suna sheƙe ayarsu, kokwanton maganarshi take Yi, ta riga ta yarda da pravin tasan bazai Iya cin amanarta ba, wata’kil ya faɗa mata hakanne don ya huce raɗaɗin abunda tayi mashi.

Damuwace ƙarara akan fuskar hajiya saratu, adaddafe ta nufi gado ta haye ta kwanta idanuwanta suna fuskantar ceilling, babu alamun zata runtsa adaren Yau.

*Hajiya Turai💔*

Safa da marwa take Yi acikin ɗakinta, Hannunta ruƙe da wayarta, night gown ce a jikinta.

Fuskarta tayi jawur tamkar wadda tasha kuka, musamman kumatuntu, green eyes dinta kuwa sun ciza launinsu, tarasa ina zata tsoma ranta taji daɗi, since wuraren ƙarfe goma take kiran layin dr.jazz babu alamun zai ɗaga, gashi har dare ya nutsa bai dawo gida ba, ta kira layin Sir mubarak kusan sau talatin shima Bai daga ba tamkar ta fasa ihu haka take ji.

“Mom” kamar daga sama taji an ambaci sunanta, tsabar ruɗi sai taji kamar muryar jazz ne.

A firgice ta juyo don ganin wanene, Yana daga tsaye bakin ƙofar ɗaki, cikin shiga ta kayan bacci ya zura hannayenshi cikin aljihun wandonshi, matashin saurayi ne kamanninshi sak dana Sir mubarak.

“Ibad kai ma baka yi bacci ba”? Muryarshi da kalasa ya furta” How can I sleep, Mom? Jazz hasn’t come home yet. na jaraba kiran layukan wayarsu duk akashe, bansani ba shi jazz ko aikin kwana yake yi a asibiti, nazo ne naji ko sun faɗa maki meya hana su dawowa gida”?

Ta lura da yanayin shi tsantsar damuwace akan face dinsa, batayi mamaki ba saboda ƙaunar da suke yi ma Jazz, sun dauke shi tamkar shaƙiƙinsu

“Ibad, I don’t know why they haven’t come home yet, I’ve been trying their phones since 10 o’clock, and nobody is picking up. I’m really worried, inajin fargabar ace wani abun ne ya faru da su” tuni idanuwanta sun ciko tab da ƙwalla.

Ruƙo hannunta Ibad yai”haba mommy, kada ki zubda hawayenki please, ki kwantar da hankalin ki, Everything is going to be okay. They’ll come home safely.”

girgiza mashi kai tai”basu ta6a yi min haka ba ibad, daga jazz din har daddyn naku, kullum ne idan zasu kai dare awaje, sai sun kira awaya sun faɗa min, amma yau shiru babu wanda ya tuntu6eni” muryarta na rawa ta furta maganar, tausayinta duk ya kama ibad, jinta yake yi tamkar mahaifiyarsu data rasu.

Gyaran muryar da akayi masu ne Ya janyo hankulansu ga duban shi, tafiya yake yi yana tunkarosu tamkar baisan da su ba, Hannun shi ruƙe da apple laptop dinshi, daga shi sai short a jikinshi, Ƙirar jikinshi da komai kalar na daddynsu ne, sai dai shi yafi ibad da daddynsu hasken fata nashi chocolate colour ne mai kyan gaske, sumar kanshi tasha gyara luf ta kwanta saman bayanshi, Yana da kirar karfi kamar ɗan wrestling, wani irin daddaɗan kamshin turarene ke fita sako da lungu na jikinshi, komai nashi da aji yake yin shi, mutunne shi maiji da kanshi, baida wasa a aikinshi, yana ruƙe da muƙamin CEO na babban Companynsu dake a ƙasar canada.

Kafafuwanshi suna asanye da slippers, magana ya somayi tamkar baisan furtata

“Mom, yanzu major ya kira ni awaya, ya fadamin suna atare da jazz wani aiki ne mai muhimmanci ya tsayar da su, so they couldn’t come home tonight. But they’ll be back early tomorrow”

Ajiyar zuciya ta sauke, har cikin ranta taji dadin jin hakan, Murmushi Ibad ya saki yana fadin”mun samu nutsuwa yanzu, Mom ki koma daki ki kwanta, ƙarfe 3 fa ta buga, gobe nasan zakiyi ramuwar bacci, murmushi tasakar mashi”bari na koma ciki, mu kwana lafiya My Sons,” ta faɗa tare da juyawa ta nufi ɗakinta, saman gado ta haye idanuwanta suna fuskantar ceilling, bakomai take jimawa ba face kwanan da za ta yi ba tare da mijinta ba, sun saba faranta ma junansu kafin su runtsa yau kuma babu shi atare da ita, ga kuma ɗanta da take jin kewarshi,
Pillow ta janyo ta rungume a ƙirjinta.

“Babban yaya nan fa ba kasar canada bace, taya zaka dinga yi mana yawo da short a tsakar falo? Kai ala dole ga bature ko? Ko kunyar mommy baka ji,” Ibad ne ya fada da zolaya.

Ko kallo bai ishe shi ba, saman Sofa mai mazaunin mutun uku ya kishingiɗa kanshi saman sofa hand, Ya daura laptop dinsa saman flat stomach dinsa.

In a husky voice ya furta”ibad! Ina buƙatar abun sha”

Ruƙe qugu Ibad yai sam baya gajiya da zolayar yayan nashi duk da tazarar shekarun dake atsakaninsu, domin kuwa Zaki ba ƙaramin mutun bane

“nan fa ba canada bace, Nigeria ce daddy Ya hana ana aikena idan dare yayi” yamutsa fuska Zaki Yai Ibad ya fara hayaƙa shi.

Calmly ya furta”Don’t make me repeat myself” kama kunne ibad yai”sorry big bro, na tuna kada ka hanani silallan kashewa” ya fada tare da nufar frigde Ya bude ya dauko mashi coke mai sanyi, ya dawo Ya daura mashi saman sofa table din gabanshi.

“Babban yaya gashi na kawo, Ni zan cire maka murfin?” banza yai mashi tamkar baiji me yace ba.

Bottle opener yaje ya dauko ya zuƙunna agaban table din Ya soma kiciniyar bude murfin, sai nishi yake yi, sam bai saba da wahala ba, ibad mugun sangartacce ne yayanshi ya 6ata shi da hutu, dogon tsoki zaki Yaja, ya yunkura ya miƙe Ya ajiye laptop din gefe ɗaya, ya kai hannu ya kar6e coke din da bottle opener din, sau ɗaya ya murɗa murfin ya cire.

Washe baki Ibad Yai”babban yaya ba za ka yi bacci ba? kana buƙatar hutu fa, kai kullum aiki baka gajiya”!

Banza yai dashi baice komai ba, a tsanake yake kur6ar coke din me sanyi, Ibad ya ƙura mashi ido yana kallon bakinsa har haɗiyar yawu yake yi.

Janye coke din yai daga bakinshi, Ya galla mashi harara”meyasa kake kallona kana haɗiyar yawu kamar wani maye? Idan so kake kasha bakasan inda zaka dauko bane”

Kwa6e mashi fuska ibad yai”Ai ni nafi so kasha ka rage min”

Sakin baki yai galala yana dubanshi”oh dole sai na baka ragowa na zaka sha” ɗaga mashi gira yai alamar eh.

Babu musu Ya miƙa mashi, don ya san rigimar ibad idan har ba bashi ragowar yai ba to kuwa zasu kwana azaune”

Yana sha yana kallon fuskar Zaki, aiku sarkin ɗumi.

“Big bro, where’s my sister pretty ? You told me she came back to Nigeria. When can we see her? Should we go to their house, or will she come to ours? (Babban yaya Ina sister pretty dina? Ba ka ce min ta dawo Nigeria ba, to yaushe zamu haɗu da ita? mu zamuje gidansu ko ita zata zo gidanmu?)

Dafe kanshi yai da hannu ɗaya”Ibad, I don’t like making noise, Please go to your room, lie down on your bed, and sleep.”

“Shikenan zanje na kwanta amma kafin nan inaso ka fadamin gaskiya, dagaske babu soyayya atsakaninku”?

Ji yake tamkar ya dauki laptop din gefenshi Ya kwalama ibad saman kanshi, Ya takura mashi.

“Ka yi shiru bakace min komai ba”!

Miƙewa zaki yai ya dauki laptop dinsa Ya nufi sashen bedroom dinsu, da sauri Ibad Yabi bayanshi, har yakusa shiga dakin ya ɗan dakata da yin tafiyar, in a cool voice ya soma magana

“Ibad, she is married and even has a daughter, And she loves her husband. But there is no love between me and her. taimakon da nayi mata dan Allah nayi shi”

Da mamaki Ibad yace”babban yaya kana nufin duk tsawon shekarun data dauka a canada a gidanka, da auranta? To ya akai ta gudu tabar mijinta da ƴarta? kuma take rayuwa agidanmu harma kuke rungume juna ai ina ganinku idan kuna shan soyayya....” kafin ya ƙare maganar, afusace zaki ya waiwayo da niyar ya kwaɗa mashi laptop din hannunshi da gudu Ibad Yabar wajen yana dariya.
Chapter 128 · 0% Book details