Sashe 33
Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Gyaɗa kai ta yi “Shureim ka ɗauko wayar ka goge su agabana In gani” tuni yasha jinin jikin shi, ba don yaso ba ya amsa mata da toh, slowly ya juya ya nufi gadon shi ya ɗauko wayar, Kafin Ya kai mata, wayar ta hau ruri, hakan ba ƙaramin daɗi yai mashi ba, Waiwayowa yai still tana a tsaye tana kallon shi”who’s calling u”? Ta jefa mashi tambayar, Nuna mata screen ɗin wayar ya yi sunan Daddy ne Ya bayyana akai” Umarni Ta bashi ya ɗaga kiran Ya kara wayar a kunanshi, Muryar Alhaji Ubaid ce ta ratsa kunnuwanshi”Shureim Uncle ɗin ka na son ganin ka, gamu nan zamu shigo cikin gidan” muryarshi A sanyaye ya amshi mashi da toh, takaicin shi ɗaya layla taƙi tafiya, ta tsare shi da ido, adan dole sai ya goge hotunanta awayarshi.
A hankali ya zame wayar daga kunnan shi, matsawa yai kusa da ita, Bayan ya cire password Na wayar Ya miƙa mata adai dai kan Gallery ɗinshi, Ta kar6i wayar tana duba hotunan, Ta yi mamakin ganinsu kamar hauka, hada wanda ya ke a rungume da ita saman ƙirjinshi, ta6e baki layla tayi, hankalin shureim ba ƙaramin tashi yai ba ganin zata danna delete all, jikin shi har tsume ya ke yi.
“Assalamu alaikum”! Muryar zainab ce ta katse mata hanzarin ta, a sukwane ta juya tana binta da kallo, a bakin ƙofa ta tsaya”Alhaji ne ya shigo tare da kawun shureim, Shine yace nayi maki magana...” yatsina fuska layla tayi”Naji, ga ni nan zuwa” Miƙa wa shureim wayar tayi”ka tabbatar ga goge su, sannan ka fito ku gaisa da kawunka,” Amsa mata yai da toh, Bayan ya kar6i wayar, fitar ta keda wuya Ya cire memory ɗin wayar, Ya 6oye shi a cikin rigar pillow, Ajiyar zuciya ya sauke Ba ƙaramin daɗi yaji ba, don ji ya ke kamar za’a raba shi da ranshi idan akace ya goge hotunanta.
Toilet ya shiga ya wanko fuskarshi, Ya futo Ya nufi dressing mirror, cikin jerin turarurrukansa ya ɗauki ɗaya ya feshe shi a jikin shi, bayan ya ajiye ya fito daga ɗakin Ya nufi babban palourn.
*GIDAN ƊAN IYA*
Tun da ta fito daga cikin toilet ta ke a tsaye bakin wardrobe, daga ita sai Towel ɗaure a ƙirjinta, Ya sauko har saitin gwiwarta, a ƙalla Tafi ƙarfin mintuna goma, ba tare da ta motsa ba, idanuwanta na akan Jerin suturarta da ke a ninke sun sha guga, ba komai ne ya tsaida ta ba fa ce neman kayan da zasu dace da tarban Manyan baƙin su da zasu Yau, Ruwan ido take yi, duk kayan da ta ɗauko sai taga kamar ba zasu dace da ita ba, Wayarta dake a jiye saman drawer ce ta soma ringing, nan ta ke taji gabanta ya faɗi fatanta Allah yasa basu bane suka ƙaraso, Da ɗan saurinta ta nufi wayar tare da kai hannu ta ɗauketa, ko da ta duba screen ɗin wayar, babu sunan wanda ya kira, Baƙuwar number ce, kokwanto ta shiga yi akan ta ɗaga ko karta ɗaga? Don ita a tsarinta bata ɗaga baƙuwar number in dai ba wadda ta yi saving akan wayarta ba ce, kusan sau uku kiran nashigowa Yana yin rejecting ba tare da ta ɗaga shi ba, tayi kasaƙe kamar an dasa mata Aya,
Shigowa Cikin ɗakin Zahra ta yi, bakinta ɗauke da sallama, turkish gown ce a jikinta launin pink ba ƙaramin kyau tayi mata ba, tayi rolling veil saman kanta. Ganin Aneelerh a tsaye yasa tace”lafiya? Ya akai naga baki shirya ba? Ko kin manta cewa suna a hanya? Sun fa kusa isowa, Na rasa meke damunki, Ko har yanzu kewar baby junaid ɗin ce bata sake ki ba”? Harara Aneelerh ta ɗan jefa mata, Ba tare da tace koma ba, ta ɗaura wayarta saman mattress, kafin ta juya ta nufi wardrobe din Kayan da ta bari a buɗe.
“Zahra zo Ki tayani zabar kayan da zan sanya, Ruwan ido Ya hana ni ɗauka tun ɗazu” murmushi zahra ta saki yayin da take tunkarar wardrobe ɗin”Aunty aneelerh, shiga za ki yi ta mutunci, ta kece raini, Lace ko shadda su zasu fi dacewa, “ Ta yi maganar tare da Kai hannu cikin wardrobe ɗin kayan ta janyo mata wani haɗaɗɗan lace launin golden colour, ta miƙa ma Aneelerh, Fuskarta ɗauke da murmushi ta kar6i Kayan da zahra ta miƙa mata”na yadda ke ƙwararriyace a6angaren iya zabar kayan da zasu dace da mutun, nafi karfin 15 mins ina neman wanda zasu dace dani na kasa, sai da ki ka zo” Zahra tace”kada ki manta aikina ne, burina kiyi kyau auntyna, surukanki su ganki a mutuncenki, bari naje na ɗauko maki sarƙar da zata dace da kayan, ‘ amsa mata Aneelerh tayi da toh, Wuce wa zahra tayi agaban drawer chest Ta zuƙunna ta dauko mata jewelry box dinta, Ta buɗe ta lalubo mata necklace da earrings launin Lace ɗinta, maida box dinta tayi kafin ta miƙe ta daura mata su gaban mirror.
“Aunty aneelerh, Ga su nan saman mirror, Pls Ki shirya da wuri, Ni zan je na taya su mami shirya masu abincin”
Amsa mata ta yi da toh ta ƙara da yi mata godiya, Bayan fitar zahra, Aneelerh ta shirya tsaf cikin Lace ɗinta, riga da skirt, sun yi bala’in yi mata kyau, sun ɗan kama jikinta, shape ɗinta ya fito sosai, Kamar a jikinta aka ɗinka kayan, a gaban mirror ta zauna tana yin make up, lip gloss ta shafa ma la66anta, Ta ɗan shafa hoda, ta ɗauki brush tana gyara jagirarta, ‘ Sumar kanta Ta sauko har saman bayanta, ƙarar Shigowar text a wayarta ne yasa ta ɗan kalli 6angaren da wayar take ajiye saman gado, sai lokacin ta tuna da baƙuwar number da ake ta kiranta ɗazu, sai da ta fara Ɗaura dan kwalin leshin Kafin ta miƙe ta nufi wayar ta ɗauke ta, Da yatsan hannunta ta janyo sakon A hankali ya buɗe, Ta yi mamakin ganin Sunanta da aka rubuta da manyan haruffa, menene ma’anar sakon? Just Aneelerh? Wanene wannan? Kiran number ta soma ƙoƙarin Yi sai dai taƙi shiga, A ƙarshe ta hakura ta daurata saman pillow, Gaban Mirror ta koma ta ɗauki jerin turarurruka tana feshe jikin ta da su, tunawa da baby junaid ɗinta yasa ta ɗan saki murmushi, tayi missing ɗinshi sosai, yau tun da safe Mahboob Yaje kai shi school, Bayan ta haɗa da shi da kuɗin fetur, kusan sati biyu da fara zuwanshi makarantar, kullum da fara’a yake tafiya, yana zumuɗi, da zarar an kaishi Ya ke saka masu rigima sai sun dawo dashi gida, Har atashi daga school ɗin Yana yin kuka, Fuskarshi jawur ake dawo mata da shi. Malaman makarantar har sun canza mashi suna daga Junaid zuwa babyn mommy, saboda sunanta da yake yawan kira masu.
Daga waje tajiyo muryar Zahra tana kwaɗa mata kira”Aunty Aneelerh! “ girgiza kai tayi aranta tace”Ko yaushe ne zahra zata daina Yi min irin wannan kiran talaucin kamar zata ƙararmin da sunana”
Zahra na shigowa ɗakin ta Waro ido waje tana fadin”Wow!!! Tabarakallahu Ahsanul khaliqin Aunty aneelern kinga yadda ki kai kyau? Kamar wadda zata shiga gasar miss world,” harara Aneelerh ta jefa mata fuskarta asake tace”Naji na gode Da yabo, ni dai yanzu faɗa min Kiran menene kike yi min”? Watsa hannu Zahra Tayi”dama ummi ne ta aiko ni zaki ci abinci yanzu ko sai anjima idan sunzo”?
“Yunwa nake Ji zahra, ba zan Iya jira sai sun zo ba, ki samu plate ki zuba min dambun shinkafa, Ki haɗo min da lemu mai sanyi, “
“Toh, Amma kafin nan mu ɗanyi selfy mana” ta yi maganar tare da Kunna camera din iphone nata, ta ɗaga Wayar Tare da ɗaura kanta saman kafaɗar Aneelerh, gaba ɗaya suka saki murmushi, ‘ kusan hotuna Biyar tayi masu atsaye kafin Ta nufi hanyar fita ɗakin tana faɗin”Idan surukan naki sunzo zamu ƙara yin wasu hotunan tare, Hakan Yana ƙara danƙon zumunci,” fuskar Aneelerh ɗauke da murmushi ta ke bin Bayan Zahra da kallo, gefen gadon ta zauna tana Jiran dawowarta.
*EVIL FOREST*
Tun da garin Allah Ya waye Masu a cikin ƙurmin dajin, Kowan nan su Ya farka, Da wata irin matsiyaciyar yunwa, suna zazzaune abakin bishiya sun jingina bayan su, Sai hamma suke Yi, Jiya basu ci abinci da yawa ba kafin Kwanta, sauran Kayan marmarin da suka rage ne su ka sha, dan ma suna da jumurin yunwa, Hankalin su ba akwance Yake ba, Danish Yaƙi farkawa daga bacci, tsawon awanni tun daren Jiya da Angel ta sanya shi yin bacci yake ta yi, Ko motsi Ba ya yi numfashinsa ne kaɗai ke fita, tun suna sa ran zai farka har sun fara tunanin Anya kuwa Lafiya? Baccin ya wuce na hankali, domin kuwa tuni safiya ta jima da wuce wa sun shiga tsakar rana. Sun tsare shi da ido suna kallon shi, A saman shimfiɗar da Angel ta yi mashi, ya ke a kwance sun ƙudundune shi da bargo, tuntuni su ka so su tada shi daga bacci amma Angel ta hana su, ita aganinta bai kamata su takura mashi ba, tsawon wata ɗaya baya runtsawa kullum shine yin gadinsu, Na yau kawai Ya samu ya runtsa ai bai kamata su katse mashi hutun shi ba.
“Angel Yunwa mu ke Ji” Parveen ce Ta yi maganar, Fuskarta A kumbure ga miyan bacci a gefe da gefen bakinta, sumar kanta A haukace take babu gyara kamar Ƴar mahaukaciya, Angel da ke Fuskantar su tana zaune daga gefen shimfiɗar Danish, fuskarta sam babu walwala, abun ya fara damunta ganin yaƙi farkawa fatanta Allah yasa baccin lafiya ne ya ke yi.
“Genie we are feeling hungry, pls cikina kukan Yunwa yake mini” Jemimah ce tayi maganar, tamkar zata fashe da kuka, idon Angel akan fuskokinsu, Batul sai hamma take Yi, tana faman yamutsa fuskarta.
“Ki jaraba Tada shi mana, wata’ƙil Ya farka, Tun da kinga mu bamu san kan dajin nan ba, balle mu ce zamu shiga ciki mu nemo abinci” Naufal ne yai maganar muryarshi da kasala.
“Ni zan Iya zuwa na nemo mana abincin sai mu ci” Gabriel Ne yai maganar, hannunshi ɗaya asaman sumar kan Azeeza da ke kwance saman ƙirjin shi.
A hankali ya zame wayar daga kunnan shi, matsawa yai kusa da ita, Bayan ya cire password Na wayar Ya miƙa mata adai dai kan Gallery ɗinshi, Ta kar6i wayar tana duba hotunan, Ta yi mamakin ganinsu kamar hauka, hada wanda ya ke a rungume da ita saman ƙirjinshi, ta6e baki layla tayi, hankalin shureim ba ƙaramin tashi yai ba ganin zata danna delete all, jikin shi har tsume ya ke yi.
“Assalamu alaikum”! Muryar zainab ce ta katse mata hanzarin ta, a sukwane ta juya tana binta da kallo, a bakin ƙofa ta tsaya”Alhaji ne ya shigo tare da kawun shureim, Shine yace nayi maki magana...” yatsina fuska layla tayi”Naji, ga ni nan zuwa” Miƙa wa shureim wayar tayi”ka tabbatar ga goge su, sannan ka fito ku gaisa da kawunka,” Amsa mata yai da toh, Bayan ya kar6i wayar, fitar ta keda wuya Ya cire memory ɗin wayar, Ya 6oye shi a cikin rigar pillow, Ajiyar zuciya ya sauke Ba ƙaramin daɗi yaji ba, don ji ya ke kamar za’a raba shi da ranshi idan akace ya goge hotunanta.
Toilet ya shiga ya wanko fuskarshi, Ya futo Ya nufi dressing mirror, cikin jerin turarurrukansa ya ɗauki ɗaya ya feshe shi a jikin shi, bayan ya ajiye ya fito daga ɗakin Ya nufi babban palourn.
*GIDAN ƊAN IYA*
Tun da ta fito daga cikin toilet ta ke a tsaye bakin wardrobe, daga ita sai Towel ɗaure a ƙirjinta, Ya sauko har saitin gwiwarta, a ƙalla Tafi ƙarfin mintuna goma, ba tare da ta motsa ba, idanuwanta na akan Jerin suturarta da ke a ninke sun sha guga, ba komai ne ya tsaida ta ba fa ce neman kayan da zasu dace da tarban Manyan baƙin su da zasu Yau, Ruwan ido take yi, duk kayan da ta ɗauko sai taga kamar ba zasu dace da ita ba, Wayarta dake a jiye saman drawer ce ta soma ringing, nan ta ke taji gabanta ya faɗi fatanta Allah yasa basu bane suka ƙaraso, Da ɗan saurinta ta nufi wayar tare da kai hannu ta ɗauketa, ko da ta duba screen ɗin wayar, babu sunan wanda ya kira, Baƙuwar number ce, kokwanto ta shiga yi akan ta ɗaga ko karta ɗaga? Don ita a tsarinta bata ɗaga baƙuwar number in dai ba wadda ta yi saving akan wayarta ba ce, kusan sau uku kiran nashigowa Yana yin rejecting ba tare da ta ɗaga shi ba, tayi kasaƙe kamar an dasa mata Aya,
Shigowa Cikin ɗakin Zahra ta yi, bakinta ɗauke da sallama, turkish gown ce a jikinta launin pink ba ƙaramin kyau tayi mata ba, tayi rolling veil saman kanta. Ganin Aneelerh a tsaye yasa tace”lafiya? Ya akai naga baki shirya ba? Ko kin manta cewa suna a hanya? Sun fa kusa isowa, Na rasa meke damunki, Ko har yanzu kewar baby junaid ɗin ce bata sake ki ba”? Harara Aneelerh ta ɗan jefa mata, Ba tare da tace koma ba, ta ɗaura wayarta saman mattress, kafin ta juya ta nufi wardrobe din Kayan da ta bari a buɗe.
“Zahra zo Ki tayani zabar kayan da zan sanya, Ruwan ido Ya hana ni ɗauka tun ɗazu” murmushi zahra ta saki yayin da take tunkarar wardrobe ɗin”Aunty aneelerh, shiga za ki yi ta mutunci, ta kece raini, Lace ko shadda su zasu fi dacewa, “ Ta yi maganar tare da Kai hannu cikin wardrobe ɗin kayan ta janyo mata wani haɗaɗɗan lace launin golden colour, ta miƙa ma Aneelerh, Fuskarta ɗauke da murmushi ta kar6i Kayan da zahra ta miƙa mata”na yadda ke ƙwararriyace a6angaren iya zabar kayan da zasu dace da mutun, nafi karfin 15 mins ina neman wanda zasu dace dani na kasa, sai da ki ka zo” Zahra tace”kada ki manta aikina ne, burina kiyi kyau auntyna, surukanki su ganki a mutuncenki, bari naje na ɗauko maki sarƙar da zata dace da kayan, ‘ amsa mata Aneelerh tayi da toh, Wuce wa zahra tayi agaban drawer chest Ta zuƙunna ta dauko mata jewelry box dinta, Ta buɗe ta lalubo mata necklace da earrings launin Lace ɗinta, maida box dinta tayi kafin ta miƙe ta daura mata su gaban mirror.
“Aunty aneelerh, Ga su nan saman mirror, Pls Ki shirya da wuri, Ni zan je na taya su mami shirya masu abincin”
Amsa mata ta yi da toh ta ƙara da yi mata godiya, Bayan fitar zahra, Aneelerh ta shirya tsaf cikin Lace ɗinta, riga da skirt, sun yi bala’in yi mata kyau, sun ɗan kama jikinta, shape ɗinta ya fito sosai, Kamar a jikinta aka ɗinka kayan, a gaban mirror ta zauna tana yin make up, lip gloss ta shafa ma la66anta, Ta ɗan shafa hoda, ta ɗauki brush tana gyara jagirarta, ‘ Sumar kanta Ta sauko har saman bayanta, ƙarar Shigowar text a wayarta ne yasa ta ɗan kalli 6angaren da wayar take ajiye saman gado, sai lokacin ta tuna da baƙuwar number da ake ta kiranta ɗazu, sai da ta fara Ɗaura dan kwalin leshin Kafin ta miƙe ta nufi wayar ta ɗauke ta, Da yatsan hannunta ta janyo sakon A hankali ya buɗe, Ta yi mamakin ganin Sunanta da aka rubuta da manyan haruffa, menene ma’anar sakon? Just Aneelerh? Wanene wannan? Kiran number ta soma ƙoƙarin Yi sai dai taƙi shiga, A ƙarshe ta hakura ta daurata saman pillow, Gaban Mirror ta koma ta ɗauki jerin turarurruka tana feshe jikin ta da su, tunawa da baby junaid ɗinta yasa ta ɗan saki murmushi, tayi missing ɗinshi sosai, yau tun da safe Mahboob Yaje kai shi school, Bayan ta haɗa da shi da kuɗin fetur, kusan sati biyu da fara zuwanshi makarantar, kullum da fara’a yake tafiya, yana zumuɗi, da zarar an kaishi Ya ke saka masu rigima sai sun dawo dashi gida, Har atashi daga school ɗin Yana yin kuka, Fuskarshi jawur ake dawo mata da shi. Malaman makarantar har sun canza mashi suna daga Junaid zuwa babyn mommy, saboda sunanta da yake yawan kira masu.
Daga waje tajiyo muryar Zahra tana kwaɗa mata kira”Aunty Aneelerh! “ girgiza kai tayi aranta tace”Ko yaushe ne zahra zata daina Yi min irin wannan kiran talaucin kamar zata ƙararmin da sunana”
Zahra na shigowa ɗakin ta Waro ido waje tana fadin”Wow!!! Tabarakallahu Ahsanul khaliqin Aunty aneelern kinga yadda ki kai kyau? Kamar wadda zata shiga gasar miss world,” harara Aneelerh ta jefa mata fuskarta asake tace”Naji na gode Da yabo, ni dai yanzu faɗa min Kiran menene kike yi min”? Watsa hannu Zahra Tayi”dama ummi ne ta aiko ni zaki ci abinci yanzu ko sai anjima idan sunzo”?
“Yunwa nake Ji zahra, ba zan Iya jira sai sun zo ba, ki samu plate ki zuba min dambun shinkafa, Ki haɗo min da lemu mai sanyi, “
“Toh, Amma kafin nan mu ɗanyi selfy mana” ta yi maganar tare da Kunna camera din iphone nata, ta ɗaga Wayar Tare da ɗaura kanta saman kafaɗar Aneelerh, gaba ɗaya suka saki murmushi, ‘ kusan hotuna Biyar tayi masu atsaye kafin Ta nufi hanyar fita ɗakin tana faɗin”Idan surukan naki sunzo zamu ƙara yin wasu hotunan tare, Hakan Yana ƙara danƙon zumunci,” fuskar Aneelerh ɗauke da murmushi ta ke bin Bayan Zahra da kallo, gefen gadon ta zauna tana Jiran dawowarta.
*EVIL FOREST*
Tun da garin Allah Ya waye Masu a cikin ƙurmin dajin, Kowan nan su Ya farka, Da wata irin matsiyaciyar yunwa, suna zazzaune abakin bishiya sun jingina bayan su, Sai hamma suke Yi, Jiya basu ci abinci da yawa ba kafin Kwanta, sauran Kayan marmarin da suka rage ne su ka sha, dan ma suna da jumurin yunwa, Hankalin su ba akwance Yake ba, Danish Yaƙi farkawa daga bacci, tsawon awanni tun daren Jiya da Angel ta sanya shi yin bacci yake ta yi, Ko motsi Ba ya yi numfashinsa ne kaɗai ke fita, tun suna sa ran zai farka har sun fara tunanin Anya kuwa Lafiya? Baccin ya wuce na hankali, domin kuwa tuni safiya ta jima da wuce wa sun shiga tsakar rana. Sun tsare shi da ido suna kallon shi, A saman shimfiɗar da Angel ta yi mashi, ya ke a kwance sun ƙudundune shi da bargo, tuntuni su ka so su tada shi daga bacci amma Angel ta hana su, ita aganinta bai kamata su takura mashi ba, tsawon wata ɗaya baya runtsawa kullum shine yin gadinsu, Na yau kawai Ya samu ya runtsa ai bai kamata su katse mashi hutun shi ba.
“Angel Yunwa mu ke Ji” Parveen ce Ta yi maganar, Fuskarta A kumbure ga miyan bacci a gefe da gefen bakinta, sumar kanta A haukace take babu gyara kamar Ƴar mahaukaciya, Angel da ke Fuskantar su tana zaune daga gefen shimfiɗar Danish, fuskarta sam babu walwala, abun ya fara damunta ganin yaƙi farkawa fatanta Allah yasa baccin lafiya ne ya ke yi.
“Genie we are feeling hungry, pls cikina kukan Yunwa yake mini” Jemimah ce tayi maganar, tamkar zata fashe da kuka, idon Angel akan fuskokinsu, Batul sai hamma take Yi, tana faman yamutsa fuskarta.
“Ki jaraba Tada shi mana, wata’ƙil Ya farka, Tun da kinga mu bamu san kan dajin nan ba, balle mu ce zamu shiga ciki mu nemo abinci” Naufal ne yai maganar muryarshi da kasala.
“Ni zan Iya zuwa na nemo mana abincin sai mu ci” Gabriel Ne yai maganar, hannunshi ɗaya asaman sumar kan Azeeza da ke kwance saman ƙirjin shi.