Sashe 41
Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
zazzaune suke a saman dining suna Yin breakfast A tsanake shiru baka jin sautin komai saina cokulansu, kwas kwakwas kamar zasu fasa plates ɗin, sun natsu suna tura abinci a cukunnansu, Alhaji ubaid na sanye da Jallabiya Hajiya Laila dake agefensa arab gown ce a jikinta launin royal blue ansha uban make up, Alhaji musa ya ɗauki wankan tsadaddun suit sun zauna mashi, mutumin fa akwai kyau kamar shi ya tsara kanshi ya iya ɗaukar wanka ga aji, daga gefen shi Dr shureim ne cikin shigarshi ta gado wato Kayan larabawa, daddaɗan ƙamshin turarensu mai daɗin shaƙa, musamman turaren Alhaji musa fragrance ɗinsa na dabanne. A hankali ya ɗan ɗago yana duban shureim ya lura ba abincin ya ke ci ba, tun da suka zauna yake ta faman jujjuya spoon ɗin hannun shi acikin plate ɗin gabanshi, gyaran muryar da Alhaji musa yai mashi ce tasa shi ɗagowa ya kalle shi
Cikin kulawa ya ke yi mashi magana”meyasa bakasan cin abinci shureim? Na lura tun shekaran Jiya da nazo gidan nan baka ci wani abun kirki ba” Hajiya Laila ta ɗan dakata da cin abincin fuskarta a yamutse take kallon alhaji musa aranta tace”ji wani ikon Allah ko’ina ruwanshi da cin shi da shan shi? Ni narasa gane shisshigin nan da yake yiwa shureim, mutumin da bai damu da shi ba, sai yanzu ne yasan da zaman shi’
Cikin sanyin murya shureim ya kalli uncle ɗin nashi”ina ci mana, kawai ni nafi sha’awar abincin hausawa ne wannan baya min daɗi abaki” Alhajin ubaid yace”Meyasa tuntuni baka yiwa zainab magana ta girka maka ba? Kamar ba ka da bakin magana, komai naka ya zama na shiririta shureim so ka ke ka koma yaro”? shiru shureim yai shi kanshi haushin rashin ƙwarin gwiwarshi yake ji, ya koma kamar wani sakarai komai sai yadda akayi da shi.
“Kada ka damu Yayana, da zarar mun koma abuja zai dawo asalin Dr shureim ɗin da ka sani ne, Kasan matata ta iya bada tarbiya zata gyara maka ɗanka ya zama namijin gaske”
Wannan maganar ta Alhaji musa tayi matuƙar ƙona ran Hajiya layla, har dai tagaza jurewa
“Me kake nufi? Ni ban iya bada tarbiya ba kome”? Ko kallo bata ishe shi ba saima Ya ɗauki glass ɗin lemu mai sanyi yakai baki Yana kur6a.
“Haba layla, meyasa bakya iya 6oye fushin ki ne? Laifine don ya yabi matarshi? Harara ta wurgawa Alhaji ubaid tamkar ƙwayar idon zata faɗo kasa
“bansan meyasa kake goya mashi baya ba, idonka ya rufe kwata kwata baka ganin laifin shi, wannan ba adalci bane” rai a6ace ta ƙarasa maganar tare da buga table din, A fusace ta miƙe tabar dining ɗin
Miƙewa shureim yai da niyar yabi bayanta da sauri Alhaji ubaid ya dakatar dashi”dawo ka zauna” komawa yai ya zauna
“daddy bana jin daɗin hakan, kasan halina tunfil azal bana so inga ran wani daga cikin ku ya 6aci” Shureim ne yai maganar
“ka kwantar da hankalinka, In sha Allah zan sasanta tsakaninsu, Yanzu zan shiga wurinta in lallasheta” Yai maganar tare da miƙewa yabar dining din bayan tafiyar Ubaid Alhaji musa ya ɗago ya kalli shureim
“You should start preparing, Ƙarfe shabiyu zamu bar jos, already nayi magana da pilot ɗina, bana buƙatar ka tafi da komai naka, Duk wani abu da za ka buƙata za’ayi maka acan” murmushin yaƙe dr shureim ya ɗan saki
“in sha Allah Uncle yanzu zan shiga ciki In ƙara shiryawa” amsa mashi Yai da toh, Kafin miƙewar Dr shurem P.a Ɗin Alhaji musa yai sallama daga wajen palourn, Hakan yasa shi saurin miƙewa cikin takun izza ya nufi ƙofar fita daga palourn
Ajiyar zuciya dr shureim ya sauke, shi kanshi shakkar Alhaji musa yake ji, mutumin babu wasa a harkarshi.
*Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*
First bank
3196407426,
*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*
_~*BossLadiesWriters*~_
_*KURKUKUN ƘADDARA*_
_The Prisoners E13🔥💫_
*Daga alƙalamin Boss Bature*
~Middle step~
_A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._
Juyawa yai da sauri ya nufi kitchen maimakon ɗakin shi, Yana shiga ya ci karo da zainab tana goge tiles da floor wiper sam bata lura dashi ba, har saida yai mata sallama tukunna ta ɗago suka haɗa ido
Fara’a ta sakar mashi”shuraim tun jiya na ke son yin magana da kai, fargaban Iyayenka ta hanani tunkarar ka” ƙarasa shiga kitchem ɗin yai
“Aunty zainab Ya zamuyi? Uncle musa ya matsa min akan saina bishi abuja, ƙarfe sha biyu zamu bar jos, “ dafe kai ta yi da hannu ɗaya
“Naji takaicin jin haka shureim, Duk plan ɗin da muka shirya ya tashi abanza kenan”
Girgiza mata kai yai”in sha Allah komai zai tafi dai dai aunty zainab, ko da ace bana nan that will not change anything”
Damuwa ce cunkushe akan fuskarta
“How ka ke tunanin komai zai tafi dai dai bayan bamu a wuri ɗaya”?
murmushin gefen fuska ya sakar mata har dimples ɗinsa suka lotsa.
“Kin manta da waya? Ina da ita kina da ita, zamu dinga yin communicating da junanmu, hakan ma zai fi ba tare da wani ya zarge mu ba” ƙayataccen murmushi zainab ta saki
“Allah ya yi maka albarka shureim ni sam na manta da waya, amma fa zan yi missing ɗinka sosai mutumina
Murmushin fuskarshi bai washe ba yace”Ni kaina zanyi missing ɗin auntyna mai share min hawayena, amma in sha Allah zamu dinga yin waya akai akai, Inaso komai da ke faruwa a gidan nan kidinga sanya min ido, da zarar an samu update ki kirani awaya ki sanar dani, amma fa sai kinyi takatsantsan kinsan Iyayen nawa ba ƙananun mutane bane”
jinjina kai Zainab ta yi don ta gamsu da bayanin shi
“In sha Allah zan kiyaye shureim, kaima ka kula min da kanka, “ idanuwansu duk sun ciko da ƙwalla, don ba ƙaramin ƙaunar juna su ke yi ba, tana jinshi tamkar Ɗanta, shima Yana jinta tamkar mahaifiyarsa, sun jima a kitchen ɗin sunayin magana kafin daga bisani yai mata sallah.
Ba tare da 6ata lokaci ba, Dr shureim Ya fara shirye shiryen tafiya abuja, bai canza komai na suturar jikinsa ba, Iya turarurrukansa kaɗai ya feshe jikinsa, sannan ya warware Ɗaurin larabawan dake akanshi, Ya sharce lallausar sumar kanshi Ya gyarata tsaf yabi da mayukansa ya shafe ta, Kafin barinsa ɗakin saida yai Nafila Ya roƙi Allah da ya tsare shi ya kare shi daga sharrin mutun sharrin zuciya da duk wani abun cutarwa, ya kuma roƙi Allah da ya sa silar komawarshi gidan uncle din shi abuja rayuwar shi ta canza ya dawo kamar yadda yake ada, addu’o’i sosai shureim yayiwa kanshi, Bayan ya kammala ya zaro memory ɗinshi da ya 6oye a cikin rigar pillow ya zaura shi awayarsa, Hankalin sa Ya ɗan kwanta zai samu natsuwar cigaba da kallon hotunan Abar ƙaunarsa awayarsa.
A gefen gadon shi ya zauna yana daddana wayar shi, Lokaci ya ke jira ya cika.
**DAULAR OBIE ESTATE**
A Hankali Jigunannun Motocinsu su ke kunno kai saman shantalelen titin obie estete, gaba da baya Sojoji ne ke tafiya akan ƙafafuwansu, Hannayensu ruƙe da bindigu, Motar farko mallakin Sir mubarak ce, motar dake a biye da ita zungureriya ƙirar Navigator limousine wadda cikinta tamkar bedroom ya ke saboda tsabar haɗuwarta, Dattijon arziƙi ne hakimce acikin motar tare da Jikokinsu tagawaye zain da zaid sai Dr Jazz shalelensa, Motar da ke abiye da tasu Danƙareriyar gaske mai numfashi mallakin Senate president Lateef Obinna ce, Yayin da motar ƙarshe Ta pravin Obinna ce, gayu mutanan Allah su kansu motocin da dattaku ake yin driving ɗinsu a tsanake cikin ƙwarewa, sautin karatun kur’ani mai girma ne ya karaɗe ko’ina, Ƙirar Ahmad suleiman mai matuƙar ratsa sassan jiki, daga motar dattijon arziƙi ƙirar ke fitowa, ƙa’ida ne a lokacin da suka fito zasu tafi masallaci sai yasa an kunna masa ƙirar Ahmed suleima haka zalika idan zasu dawo daga masallaci sai an kunna masu karatun wani sa’in Idan ƙirar takai mashi karo har bi yake yi yana lumshe ido, A yanzu haka dawowarsu kenan daga masallacin Juma’a.
Sannu A hankali su ke tunkarar Moto park ɗinsu, kusan atare motocin suka Yi parking at same time, Da azama sojoji su ke bubbuɗe masu mota, A hankali Obie Ya sauko ƙafarshi dake sanye cikin takalma kalar na sarakuna, Jikinsa Jallabiya ce daga sama Ya ɗaura alkebba haɗaɗɗar gaske sai ƙyalli ta ke Yi, ɗaya bayan ɗaya su ke fito daga Cikin motocin, gaba ɗayansu haɗaɗɗun Jallabiyoyi ne a jikin su daga Iyayen Har ƴa’ƴan.
“Mu shiga ciki ko”? Obie ne Yai masu maganar, Zaid da zayn Sai faman sunnar dakai ƙasa suke yi kamar marasa gaskiya, mamakin hakan yasa Mahaifinsu pravin tanka masu
“Lafiya”? Kafin su yi yunƙurin bashi amsa Sir Mubarak ya tari numfashin su
“Zaku ci ƙaniyarku ne, ƙananun Ƴan iska masu kwana da wando, har ni zaku dinga kakkaucema wa? Kun raina ni ko”? Fuskar shi a ɗaure ya ke yi masu magana, sir mubarak mutunne mai fusatacciyar zuciya abu kaɗan ke hasala shi sai da ta wani 6angaren yana da sauƙin kai.
Dr jazz Yana ruƙe da hannun Obie dariya ce ƙumshe abakinsa, ya ƙi bari ta kubce masa gudun kada Ya ji saukar mari daga Sir mubarak, Twins kuwa Duk sun sha jinin jikinsu sai faman noƙe kai suke yi haɗi da sosa ƙeyarsu.
A fusace Ya daka masu tsawa har saida suka ɗan razana atare su ka ɗago da fararen idanuwansu akan fuskarshi” Ina magana kuna kallona? Saboda tsabar fitsara”? Da sauri suka sunnar da kawunansu ƙasa, Alkunyace ta hana Pravin sanya baki, Gyaran murya senate Lateef Ya yi ma ɗan uwan nashi, Ya juya yana duban shi, cikin muryan Manyantaka Ya soma magana
“Aymasu afwa, Yarane su har yanzu, basu mallaki hankalin su ba, Sai ana haƙuri da su”
Cikin kulawa ya ke yi mashi magana”meyasa bakasan cin abinci shureim? Na lura tun shekaran Jiya da nazo gidan nan baka ci wani abun kirki ba” Hajiya Laila ta ɗan dakata da cin abincin fuskarta a yamutse take kallon alhaji musa aranta tace”ji wani ikon Allah ko’ina ruwanshi da cin shi da shan shi? Ni narasa gane shisshigin nan da yake yiwa shureim, mutumin da bai damu da shi ba, sai yanzu ne yasan da zaman shi’
Cikin sanyin murya shureim ya kalli uncle ɗin nashi”ina ci mana, kawai ni nafi sha’awar abincin hausawa ne wannan baya min daɗi abaki” Alhajin ubaid yace”Meyasa tuntuni baka yiwa zainab magana ta girka maka ba? Kamar ba ka da bakin magana, komai naka ya zama na shiririta shureim so ka ke ka koma yaro”? shiru shureim yai shi kanshi haushin rashin ƙwarin gwiwarshi yake ji, ya koma kamar wani sakarai komai sai yadda akayi da shi.
“Kada ka damu Yayana, da zarar mun koma abuja zai dawo asalin Dr shureim ɗin da ka sani ne, Kasan matata ta iya bada tarbiya zata gyara maka ɗanka ya zama namijin gaske”
Wannan maganar ta Alhaji musa tayi matuƙar ƙona ran Hajiya layla, har dai tagaza jurewa
“Me kake nufi? Ni ban iya bada tarbiya ba kome”? Ko kallo bata ishe shi ba saima Ya ɗauki glass ɗin lemu mai sanyi yakai baki Yana kur6a.
“Haba layla, meyasa bakya iya 6oye fushin ki ne? Laifine don ya yabi matarshi? Harara ta wurgawa Alhaji ubaid tamkar ƙwayar idon zata faɗo kasa
“bansan meyasa kake goya mashi baya ba, idonka ya rufe kwata kwata baka ganin laifin shi, wannan ba adalci bane” rai a6ace ta ƙarasa maganar tare da buga table din, A fusace ta miƙe tabar dining ɗin
Miƙewa shureim yai da niyar yabi bayanta da sauri Alhaji ubaid ya dakatar dashi”dawo ka zauna” komawa yai ya zauna
“daddy bana jin daɗin hakan, kasan halina tunfil azal bana so inga ran wani daga cikin ku ya 6aci” Shureim ne yai maganar
“ka kwantar da hankalinka, In sha Allah zan sasanta tsakaninsu, Yanzu zan shiga wurinta in lallasheta” Yai maganar tare da miƙewa yabar dining din bayan tafiyar Ubaid Alhaji musa ya ɗago ya kalli shureim
“You should start preparing, Ƙarfe shabiyu zamu bar jos, already nayi magana da pilot ɗina, bana buƙatar ka tafi da komai naka, Duk wani abu da za ka buƙata za’ayi maka acan” murmushin yaƙe dr shureim ya ɗan saki
“in sha Allah Uncle yanzu zan shiga ciki In ƙara shiryawa” amsa mashi Yai da toh, Kafin miƙewar Dr shurem P.a Ɗin Alhaji musa yai sallama daga wajen palourn, Hakan yasa shi saurin miƙewa cikin takun izza ya nufi ƙofar fita daga palourn
Ajiyar zuciya dr shureim ya sauke, shi kanshi shakkar Alhaji musa yake ji, mutumin babu wasa a harkarshi.
*Boss Bature✍️ Mu haɗu gobe Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game son cigaban littafin kurkukun ƙaddara 500 ne zai tura ta acct number dina Ga bank details da za ki tura kuɗin*
First bank
3196407426,
*Bature Hafsat Muhammad, za’a tura evidence of payment ta phone number ɗina 08169856268 Banda kira whatsapp kawai*
_~*BossLadiesWriters*~_
_*KURKUKUN ƘADDARA*_
_The Prisoners E13🔥💫_
*Daga alƙalamin Boss Bature*
~Middle step~
_A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._
Juyawa yai da sauri ya nufi kitchen maimakon ɗakin shi, Yana shiga ya ci karo da zainab tana goge tiles da floor wiper sam bata lura dashi ba, har saida yai mata sallama tukunna ta ɗago suka haɗa ido
Fara’a ta sakar mashi”shuraim tun jiya na ke son yin magana da kai, fargaban Iyayenka ta hanani tunkarar ka” ƙarasa shiga kitchem ɗin yai
“Aunty zainab Ya zamuyi? Uncle musa ya matsa min akan saina bishi abuja, ƙarfe sha biyu zamu bar jos, “ dafe kai ta yi da hannu ɗaya
“Naji takaicin jin haka shureim, Duk plan ɗin da muka shirya ya tashi abanza kenan”
Girgiza mata kai yai”in sha Allah komai zai tafi dai dai aunty zainab, ko da ace bana nan that will not change anything”
Damuwa ce cunkushe akan fuskarta
“How ka ke tunanin komai zai tafi dai dai bayan bamu a wuri ɗaya”?
murmushin gefen fuska ya sakar mata har dimples ɗinsa suka lotsa.
“Kin manta da waya? Ina da ita kina da ita, zamu dinga yin communicating da junanmu, hakan ma zai fi ba tare da wani ya zarge mu ba” ƙayataccen murmushi zainab ta saki
“Allah ya yi maka albarka shureim ni sam na manta da waya, amma fa zan yi missing ɗinka sosai mutumina
Murmushin fuskarshi bai washe ba yace”Ni kaina zanyi missing ɗin auntyna mai share min hawayena, amma in sha Allah zamu dinga yin waya akai akai, Inaso komai da ke faruwa a gidan nan kidinga sanya min ido, da zarar an samu update ki kirani awaya ki sanar dani, amma fa sai kinyi takatsantsan kinsan Iyayen nawa ba ƙananun mutane bane”
jinjina kai Zainab ta yi don ta gamsu da bayanin shi
“In sha Allah zan kiyaye shureim, kaima ka kula min da kanka, “ idanuwansu duk sun ciko da ƙwalla, don ba ƙaramin ƙaunar juna su ke yi ba, tana jinshi tamkar Ɗanta, shima Yana jinta tamkar mahaifiyarsa, sun jima a kitchen ɗin sunayin magana kafin daga bisani yai mata sallah.
Ba tare da 6ata lokaci ba, Dr shureim Ya fara shirye shiryen tafiya abuja, bai canza komai na suturar jikinsa ba, Iya turarurrukansa kaɗai ya feshe jikinsa, sannan ya warware Ɗaurin larabawan dake akanshi, Ya sharce lallausar sumar kanshi Ya gyarata tsaf yabi da mayukansa ya shafe ta, Kafin barinsa ɗakin saida yai Nafila Ya roƙi Allah da ya tsare shi ya kare shi daga sharrin mutun sharrin zuciya da duk wani abun cutarwa, ya kuma roƙi Allah da ya sa silar komawarshi gidan uncle din shi abuja rayuwar shi ta canza ya dawo kamar yadda yake ada, addu’o’i sosai shureim yayiwa kanshi, Bayan ya kammala ya zaro memory ɗinshi da ya 6oye a cikin rigar pillow ya zaura shi awayarsa, Hankalin sa Ya ɗan kwanta zai samu natsuwar cigaba da kallon hotunan Abar ƙaunarsa awayarsa.
A gefen gadon shi ya zauna yana daddana wayar shi, Lokaci ya ke jira ya cika.
**DAULAR OBIE ESTATE**
A Hankali Jigunannun Motocinsu su ke kunno kai saman shantalelen titin obie estete, gaba da baya Sojoji ne ke tafiya akan ƙafafuwansu, Hannayensu ruƙe da bindigu, Motar farko mallakin Sir mubarak ce, motar dake a biye da ita zungureriya ƙirar Navigator limousine wadda cikinta tamkar bedroom ya ke saboda tsabar haɗuwarta, Dattijon arziƙi ne hakimce acikin motar tare da Jikokinsu tagawaye zain da zaid sai Dr Jazz shalelensa, Motar da ke abiye da tasu Danƙareriyar gaske mai numfashi mallakin Senate president Lateef Obinna ce, Yayin da motar ƙarshe Ta pravin Obinna ce, gayu mutanan Allah su kansu motocin da dattaku ake yin driving ɗinsu a tsanake cikin ƙwarewa, sautin karatun kur’ani mai girma ne ya karaɗe ko’ina, Ƙirar Ahmad suleiman mai matuƙar ratsa sassan jiki, daga motar dattijon arziƙi ƙirar ke fitowa, ƙa’ida ne a lokacin da suka fito zasu tafi masallaci sai yasa an kunna masa ƙirar Ahmed suleima haka zalika idan zasu dawo daga masallaci sai an kunna masu karatun wani sa’in Idan ƙirar takai mashi karo har bi yake yi yana lumshe ido, A yanzu haka dawowarsu kenan daga masallacin Juma’a.
Sannu A hankali su ke tunkarar Moto park ɗinsu, kusan atare motocin suka Yi parking at same time, Da azama sojoji su ke bubbuɗe masu mota, A hankali Obie Ya sauko ƙafarshi dake sanye cikin takalma kalar na sarakuna, Jikinsa Jallabiya ce daga sama Ya ɗaura alkebba haɗaɗɗar gaske sai ƙyalli ta ke Yi, ɗaya bayan ɗaya su ke fito daga Cikin motocin, gaba ɗayansu haɗaɗɗun Jallabiyoyi ne a jikin su daga Iyayen Har ƴa’ƴan.
“Mu shiga ciki ko”? Obie ne Yai masu maganar, Zaid da zayn Sai faman sunnar dakai ƙasa suke yi kamar marasa gaskiya, mamakin hakan yasa Mahaifinsu pravin tanka masu
“Lafiya”? Kafin su yi yunƙurin bashi amsa Sir Mubarak ya tari numfashin su
“Zaku ci ƙaniyarku ne, ƙananun Ƴan iska masu kwana da wando, har ni zaku dinga kakkaucema wa? Kun raina ni ko”? Fuskar shi a ɗaure ya ke yi masu magana, sir mubarak mutunne mai fusatacciyar zuciya abu kaɗan ke hasala shi sai da ta wani 6angaren yana da sauƙin kai.
Dr jazz Yana ruƙe da hannun Obie dariya ce ƙumshe abakinsa, ya ƙi bari ta kubce masa gudun kada Ya ji saukar mari daga Sir mubarak, Twins kuwa Duk sun sha jinin jikinsu sai faman noƙe kai suke yi haɗi da sosa ƙeyarsu.
A fusace Ya daka masu tsawa har saida suka ɗan razana atare su ka ɗago da fararen idanuwansu akan fuskarshi” Ina magana kuna kallona? Saboda tsabar fitsara”? Da sauri suka sunnar da kawunansu ƙasa, Alkunyace ta hana Pravin sanya baki, Gyaran murya senate Lateef Ya yi ma ɗan uwan nashi, Ya juya yana duban shi, cikin muryan Manyantaka Ya soma magana
“Aymasu afwa, Yarane su har yanzu, basu mallaki hankalin su ba, Sai ana haƙuri da su”