Sashe 5
Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
"Ba zamu iya jurewa rashinki atare damu ba Angel, wlh muna ƙaunarki fiye da yarda muke son kanmu, bamu son wani abu ya same ki, saboda mu kike ƙoƙarin jefa kan ki ga halaka taya ba zamu yi kuka ba? Angel ke uwace agare mu, Kin fiye mana iyayenmu da su ka yi watsi damu, Dan Allah Angel karki bari mu rasa ki" Sosai suka sanya mata kuka
Itama ta fashe masu da matsanancin kuka mai cin rai tamkar ana zare ranta Cikin muryar kuka take magana
"Shiga prison Ya zamar mun dole, Idan har ban je ba rayuwar mu tana a cikin haɗari, sannan Alƙawari ne na ɗauka Dole na cika shi ku daina raunata mun zuciyata kada kusa Na gaza......" Kasa ƙarasa maganar ta yi saboda raɗaɗin da ta ke ji a cikin zuciyarta.
Tsawon lokaci suna kallon kallo a tsakanin su kafin ta tsagaita da yin kukan tace da batul"Ga amanar jemimah, Ki rungume mun ita a ƙirjin ki har sai ta yi bacci, da zarar na dawo zan kar6i abuna" cikin sanyin murya batul ta amsa mata da cewa In sha Allah zan bata kyakkyawar kulawa har ki dawo Angel, murmushin yaƙe ta ƙaƙaro kan fuskarta tare da kallon su Parveen da ke atsaitsaye tace"Zan tafi ba za ku rungume ni a jikin ku ba"? Jin haka yasa da sauri suka matso kusa da ita, Ɗaya bayan ɗaya suka dinga rungumeta a ƙirjin su, kamar karsu sake ta, a ƙarshe Ta Soma tafiya tana ja da baya tana kallon su idanuwansu akanta, Jiki amace ta juya tare da buɗe ƙofar ɗakin tsohuwa tamira, Da gudun gaske Cikin duhu ta nufi sashen toilet ɗinsu tana faɗowa Hasken sauran fitilun dake a cikin toilets Ya haskaka idanuwanta, buɗe ƙofar toilet ɗin ta yi tare da shigewa Ciki. Yatsun hannunta na kerma ta sanya jamlock ta datse ƙofa don kar su yi gigin cewa zasu bi bayanta, A jikin ƙofar ta jingina bayanta sosai ta fashe da kuka gudun kada su ji sautin kukanta yasa ta toshe bakinta da tafin hannunta, tsawon mintuna goma shabiyar tana sharar ƙwalla kamar ruwan hawayenta zasu ƙare sai da tayi mai isarta kafin ta soma tafiya tana tunkarar Tagar da zata dura, har zata gifta tukunyar fulawar nan ta ɗan dakata da yin tafiya kafin a hankali ta kalli inda ta ke a jingine jikin bango, duk da halin da take aciki na fargaba sai da tayi mamakin ganin an maida tukunyar a mazauninta na asali, shiyasa ɗazu tsohuwa Zafreen bata samu damar ganin ƙofar ba saboda an toshe ta, ajiyar zuciya ta sauke tare da lumshe idunuwanta daga bisani ware su sosai akan furen Danish da ganyayyakin shi su ka bubbuɗe gwanin ban sha'awa, Kyakkyawar fuskarshi ta ke imagining acikin idanuwanta, aranta kuwa tana ayyana koya Zata Ganshi a yanzu daya koma Giant? Da wannan tunanin Angel Ta ƙarasa gaban glass window ɗin Ta janyo bokitin Ta haye sama A hankali ta 6a66ako glass ɗin tare da curo shi ta dire shi ƙasa kafin ta daddage ta haura Saman tagar bakinta ɗauke da Bismillah.
Zuƙunna tayi a jikin bangon da ta faɗo, wani irin Sanyi ne ya mamaye sassan Jikinta, Ga tsoro daya mamaye zuciyarta, Biji biji take ƙarewa doguwar hanyar kallo, duhu sosai babu haske sai dai da alamun haske a ƙarshen hanyar Inda Babban filin nan ya ke.
miƙewa Tayi tsare tare da Sanya hannayenta Biyu ta ruƙo duguwar sumar kanta tare da nannaɗeta ta jefar da ita saman gadon Bayanta, tunawa da addu'oin da ta karanta a jiya da tayi fitar nan yasa a yanzu ma ta soma ambaton su acikin zuciyarta, A yayin da take tafiya tana nufar cikin kurkukun........
*Boss Bature✍️ Mu haɗu Monday Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game neman ƙarin Bayani Ya tuntu6i Layina na whatsapp 08103884440 banda Kira just message😊*
_~*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*~_
*KURKUKUN ƘADDARA*
_The Prisoners 2🔥💫_
*Daga alƙalamin Hafsat Bature*
~Middle step~
_A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._
Bayin Allah su Batul zullumi da fargabar Halin da Angel zata shiga Ya hana su runtsa a daren ranar, A ɗakin tsohuwa Tamira su ka zazzauna saman floor, zuciyarsu na harbawa da faɗuwar gaba, Sun yi shiru kowa da a bun da ya ke saƙawa acikin ranshi. Deeja ce tai ƙoƙarin tunasar dasu akan su yi mata addu’a. Su ka amsa mata da toh, nan fa kowan nan su ya soma karanto addu’o’in da Angel ta koya ma su.
Dare ya nutsa sosai Azeeza tuni ta koma bacci, a saman ƙirjin Gabriel ta kwantar da kanta, Hannun shi na dafe da bayanta kamar zai mai da ta cikin sa.
Jemimah tana a kwance saman cinyoyin Batul ta ƙi yin bacci, ba yadda ba su yi da ita ba akan ta runtse idon ta ta yi bacci amma ta kafe akan sai Genie ɗinta ta dawo, a ƙarshe ma da su ka matsa mata sai ta sanya masu kuka, Tsananin tausayinta ne ya kama su, Haris yace ku bita a hankalin ni banga laifin ta ba, saboda ita yarinya ce ta saba kwana rungume da Angel dole taji ba daɗi, Rarrashin ta ya kama ta mu yi, Amsa mashi su ka yi da toh, atare su ka haɗu suna rarrashin jemimah daƙyar su ka shawo kanta.
Parveen sai hammah ta ke yi Ga yunwa ga Bacci, Naufal da ke zaune a gefenta Yace da ita Ki kwanta ki yi bacci mana, Kin ishe ni da hammah” harara ta ɗan jefa mashi tare da cewa”in yi bacci fa ka ce? Sai kace bansan ciwon kaina ba, Ta ya zan iya runtsawa bayan yan uwar mu tana acikin kurkuku....” ta6e la66ansa Yai”Naji daɗi da ki ka yi Hankali” bata tanka mashi ba sai ma ɗaura kanta da ta yi asaman laps ɗinshi.
“Batul mu tashi mu bi Genie mu ɗauko ta” Muryar Jemimah ce ta yi maganar Fuskar ta ta yi sumtum saboda kukan da tasha, Lallashinta Batul ta yi” Ki yi haƙuri kin ji, In sha Allah zata dawo Cikin Mu, Badajimawa ba,” Zumbura ba ki ta ɗanyi “Toh idan ta dawo zamu gudu ko”? gaba ɗaya hankalinsu Haris ya dawo kanta
Murmushi Batul ta sakar mata”Eh mana da zarar ta dawo zamu gudu mubar kurkuku....” tunkan ta kai ƙarshen maganar Jemimah ta katse ta da cewa”Zamu koma gidan daddyn Genie Ko? In da zamu sakata mu wala mu yi rayuwar mu babu takura Allah yasa genie ɗin mu ta dawo da wuri na ƙosa muje inga gidan daddyn ta”
farin cikin da su ka gani akan fuskar jemimah a yayin da ta ke yin maganar yai matuƙar karya masu Zuciya, Har sai da suka ji hawaye sun cika idanuwansu, cikin rauni na murya Deeja tace da ita
“Jemimah Pray for Her! Tana buƙatar addu’ar mu, mu dage da yi mata addu’a har sai ta dawo Cikin mu” jinjina kai jemimah ta yi tare da cewa”tom zan mata addu’a” ta ambaci hakan tare da lumshe idanuwanta, acikin zuciyarta tana ambaton Ya Allah ka dawo min da Genie ɗita in dai kana son farin ciki na....”
“Gabriel Ka tada azeeza ta tashi Mu haɗu mu duka wurin yi mata addu’a ba yadda za’ae muna acikin tashin hankalin nan ita tana bacci, ko dai jemimah da ta ke ƙarama a cikin mu ta kasa runtsawa balle ita” Rubina ce ta yi maganar, Girgiza mata kai Gabriel yai alamar Bazai tayar da ita ba
“I’m sorry to say I can’t wake her I don’t want to worry her, Just Let her sleep.” ɗaure fuska Rubina ta yi jin a bun da yace, ita haushinta yadda suka tashi hankalin su akan Angel amma ita Azeeza ta lafe jikin shi Hankalin ta kwance ta ke sharar bacci.
“Akwai matsala fa! Dare Yana ƙara nutsawa babu alamun Angel zata dawo” Sarah ce ta yi maganar tana daga zaune Ta jingina bayanta jikin bango, Ta saki dogayen ƙafafuwanta ƙasa.
“Duka yaushe ta tafi da har za ki fara tunanin akwai matsala! Pls mu yi mata fatan Alkhairi, Ni gajan haƙuri ke bana so” acewar Haris.
To jama’a abu fa kamar wasa A ƙalla Angel ta ɗauki tsawon awanni babu ita babu alamarta, Idanuwansu sun kaɗa sunyi jawur dasu ga bacci ga yunwa ga zullumin rashin ta atare da su, sun dage sai addu’a Su ke Yi mata, Ba zato ba tsammani Hasken Ɗakin su ya gauraye ko’ina, ta jikin ƙofar ɗakin tsohuwa da bata ƙarasa datsewa ba su ka hango hasken da ke kurɗaɗowa, Hankalinsu Ba ƙarami tashi yai ba, A kiɗime su ka mimmiƙe tsaye hatta Azeeza da ke bacci sai da ta farka tana faman murza idanuwanta da yatsun hannayenta.
kallon kallo suka shiga jefawa junansu fuskokinsu ɗauke da matsananciya damuwa
“Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un;’ shine kalmar da ta fara fitowa abakunansu Deeja, Yayin da su ke a tsaitsaye cirko cirko, Bakomai ne ya tayar masu da hankali ba face ganin Safiya ta yi ba tare da Angel ta dawo ba. Nan ta ke ransu ya basu cewar wani abu ya faru da ƴar uwarsu.................
Shine meke Faruwane ata 6angaren Angel!?
Ai tun lokacin data watsa da gudu ta nufi Cikin kurkuku, Sautin kururuwa
Mai ƙaraji da gurnani ya cika kunnuwanta, ga wani azababben San yi da ya addabe ta, kamar jaura ta gifta Cikin duhu ta ke gudu
Adai dai lokacin da ta ɗaura ƙafarta saman ground floor ɗin nan Inda ke kewaye da dogayen benaye Ba zato Ba tsammani idanuwanta su ka sauka akan ƙafafuwan Tsohuwa Zafreen Lamarin yai matuƙar gigitar da ita, sam Ba ta yi tsammanin Zata ci karo da wani abu ba ita kawai ta sanyawa ranta cewa Danish ne kaɗai mutumin da zata haɗu da shi.
Mummunar faɗuwa gabanta yai, ƙirjinta ya hau bugu da ƙarfi da ƙarfi A firgice ta ɗago da idonta akan tsohuwa zafreen da ke a ruƙe da sanda, Kasancewar Filin Yana da Fitilu masu haske can saman silin ya gauraye ko’ina, daga ƙasa har sama shigar Jajayen kaya ne a jikinta kamar kullum Fuskarta na asanye da takuntumi.
Itama ta fashe masu da matsanancin kuka mai cin rai tamkar ana zare ranta Cikin muryar kuka take magana
"Shiga prison Ya zamar mun dole, Idan har ban je ba rayuwar mu tana a cikin haɗari, sannan Alƙawari ne na ɗauka Dole na cika shi ku daina raunata mun zuciyata kada kusa Na gaza......" Kasa ƙarasa maganar ta yi saboda raɗaɗin da ta ke ji a cikin zuciyarta.
Tsawon lokaci suna kallon kallo a tsakanin su kafin ta tsagaita da yin kukan tace da batul"Ga amanar jemimah, Ki rungume mun ita a ƙirjin ki har sai ta yi bacci, da zarar na dawo zan kar6i abuna" cikin sanyin murya batul ta amsa mata da cewa In sha Allah zan bata kyakkyawar kulawa har ki dawo Angel, murmushin yaƙe ta ƙaƙaro kan fuskarta tare da kallon su Parveen da ke atsaitsaye tace"Zan tafi ba za ku rungume ni a jikin ku ba"? Jin haka yasa da sauri suka matso kusa da ita, Ɗaya bayan ɗaya suka dinga rungumeta a ƙirjin su, kamar karsu sake ta, a ƙarshe Ta Soma tafiya tana ja da baya tana kallon su idanuwansu akanta, Jiki amace ta juya tare da buɗe ƙofar ɗakin tsohuwa tamira, Da gudun gaske Cikin duhu ta nufi sashen toilet ɗinsu tana faɗowa Hasken sauran fitilun dake a cikin toilets Ya haskaka idanuwanta, buɗe ƙofar toilet ɗin ta yi tare da shigewa Ciki. Yatsun hannunta na kerma ta sanya jamlock ta datse ƙofa don kar su yi gigin cewa zasu bi bayanta, A jikin ƙofar ta jingina bayanta sosai ta fashe da kuka gudun kada su ji sautin kukanta yasa ta toshe bakinta da tafin hannunta, tsawon mintuna goma shabiyar tana sharar ƙwalla kamar ruwan hawayenta zasu ƙare sai da tayi mai isarta kafin ta soma tafiya tana tunkarar Tagar da zata dura, har zata gifta tukunyar fulawar nan ta ɗan dakata da yin tafiya kafin a hankali ta kalli inda ta ke a jingine jikin bango, duk da halin da take aciki na fargaba sai da tayi mamakin ganin an maida tukunyar a mazauninta na asali, shiyasa ɗazu tsohuwa Zafreen bata samu damar ganin ƙofar ba saboda an toshe ta, ajiyar zuciya ta sauke tare da lumshe idunuwanta daga bisani ware su sosai akan furen Danish da ganyayyakin shi su ka bubbuɗe gwanin ban sha'awa, Kyakkyawar fuskarshi ta ke imagining acikin idanuwanta, aranta kuwa tana ayyana koya Zata Ganshi a yanzu daya koma Giant? Da wannan tunanin Angel Ta ƙarasa gaban glass window ɗin Ta janyo bokitin Ta haye sama A hankali ta 6a66ako glass ɗin tare da curo shi ta dire shi ƙasa kafin ta daddage ta haura Saman tagar bakinta ɗauke da Bismillah.
Zuƙunna tayi a jikin bangon da ta faɗo, wani irin Sanyi ne ya mamaye sassan Jikinta, Ga tsoro daya mamaye zuciyarta, Biji biji take ƙarewa doguwar hanyar kallo, duhu sosai babu haske sai dai da alamun haske a ƙarshen hanyar Inda Babban filin nan ya ke.
miƙewa Tayi tsare tare da Sanya hannayenta Biyu ta ruƙo duguwar sumar kanta tare da nannaɗeta ta jefar da ita saman gadon Bayanta, tunawa da addu'oin da ta karanta a jiya da tayi fitar nan yasa a yanzu ma ta soma ambaton su acikin zuciyarta, A yayin da take tafiya tana nufar cikin kurkukun........
*Boss Bature✍️ Mu haɗu Monday Idan Allah Ya kai mu da rai da lafiya don jin yadda zata Kaya Game neman ƙarin Bayani Ya tuntu6i Layina na whatsapp 08103884440 banda Kira just message😊*
_~*✊💋BOSS LADIES WRITERS💋✊*~_
*KURKUKUN ƘADDARA*
_The Prisoners 2🔥💫_
*Daga alƙalamin Hafsat Bature*
~Middle step~
_A heart-wrenching story of love, romance, and redemption, set against a backdrop of betrayal and cruelty💔._
Bayin Allah su Batul zullumi da fargabar Halin da Angel zata shiga Ya hana su runtsa a daren ranar, A ɗakin tsohuwa Tamira su ka zazzauna saman floor, zuciyarsu na harbawa da faɗuwar gaba, Sun yi shiru kowa da a bun da ya ke saƙawa acikin ranshi. Deeja ce tai ƙoƙarin tunasar dasu akan su yi mata addu’a. Su ka amsa mata da toh, nan fa kowan nan su ya soma karanto addu’o’in da Angel ta koya ma su.
Dare ya nutsa sosai Azeeza tuni ta koma bacci, a saman ƙirjin Gabriel ta kwantar da kanta, Hannun shi na dafe da bayanta kamar zai mai da ta cikin sa.
Jemimah tana a kwance saman cinyoyin Batul ta ƙi yin bacci, ba yadda ba su yi da ita ba akan ta runtse idon ta ta yi bacci amma ta kafe akan sai Genie ɗinta ta dawo, a ƙarshe ma da su ka matsa mata sai ta sanya masu kuka, Tsananin tausayinta ne ya kama su, Haris yace ku bita a hankalin ni banga laifin ta ba, saboda ita yarinya ce ta saba kwana rungume da Angel dole taji ba daɗi, Rarrashin ta ya kama ta mu yi, Amsa mashi su ka yi da toh, atare su ka haɗu suna rarrashin jemimah daƙyar su ka shawo kanta.
Parveen sai hammah ta ke yi Ga yunwa ga Bacci, Naufal da ke zaune a gefenta Yace da ita Ki kwanta ki yi bacci mana, Kin ishe ni da hammah” harara ta ɗan jefa mashi tare da cewa”in yi bacci fa ka ce? Sai kace bansan ciwon kaina ba, Ta ya zan iya runtsawa bayan yan uwar mu tana acikin kurkuku....” ta6e la66ansa Yai”Naji daɗi da ki ka yi Hankali” bata tanka mashi ba sai ma ɗaura kanta da ta yi asaman laps ɗinshi.
“Batul mu tashi mu bi Genie mu ɗauko ta” Muryar Jemimah ce ta yi maganar Fuskar ta ta yi sumtum saboda kukan da tasha, Lallashinta Batul ta yi” Ki yi haƙuri kin ji, In sha Allah zata dawo Cikin Mu, Badajimawa ba,” Zumbura ba ki ta ɗanyi “Toh idan ta dawo zamu gudu ko”? gaba ɗaya hankalinsu Haris ya dawo kanta
Murmushi Batul ta sakar mata”Eh mana da zarar ta dawo zamu gudu mubar kurkuku....” tunkan ta kai ƙarshen maganar Jemimah ta katse ta da cewa”Zamu koma gidan daddyn Genie Ko? In da zamu sakata mu wala mu yi rayuwar mu babu takura Allah yasa genie ɗin mu ta dawo da wuri na ƙosa muje inga gidan daddyn ta”
farin cikin da su ka gani akan fuskar jemimah a yayin da ta ke yin maganar yai matuƙar karya masu Zuciya, Har sai da suka ji hawaye sun cika idanuwansu, cikin rauni na murya Deeja tace da ita
“Jemimah Pray for Her! Tana buƙatar addu’ar mu, mu dage da yi mata addu’a har sai ta dawo Cikin mu” jinjina kai jemimah ta yi tare da cewa”tom zan mata addu’a” ta ambaci hakan tare da lumshe idanuwanta, acikin zuciyarta tana ambaton Ya Allah ka dawo min da Genie ɗita in dai kana son farin ciki na....”
“Gabriel Ka tada azeeza ta tashi Mu haɗu mu duka wurin yi mata addu’a ba yadda za’ae muna acikin tashin hankalin nan ita tana bacci, ko dai jemimah da ta ke ƙarama a cikin mu ta kasa runtsawa balle ita” Rubina ce ta yi maganar, Girgiza mata kai Gabriel yai alamar Bazai tayar da ita ba
“I’m sorry to say I can’t wake her I don’t want to worry her, Just Let her sleep.” ɗaure fuska Rubina ta yi jin a bun da yace, ita haushinta yadda suka tashi hankalin su akan Angel amma ita Azeeza ta lafe jikin shi Hankalin ta kwance ta ke sharar bacci.
“Akwai matsala fa! Dare Yana ƙara nutsawa babu alamun Angel zata dawo” Sarah ce ta yi maganar tana daga zaune Ta jingina bayanta jikin bango, Ta saki dogayen ƙafafuwanta ƙasa.
“Duka yaushe ta tafi da har za ki fara tunanin akwai matsala! Pls mu yi mata fatan Alkhairi, Ni gajan haƙuri ke bana so” acewar Haris.
To jama’a abu fa kamar wasa A ƙalla Angel ta ɗauki tsawon awanni babu ita babu alamarta, Idanuwansu sun kaɗa sunyi jawur dasu ga bacci ga yunwa ga zullumin rashin ta atare da su, sun dage sai addu’a Su ke Yi mata, Ba zato ba tsammani Hasken Ɗakin su ya gauraye ko’ina, ta jikin ƙofar ɗakin tsohuwa da bata ƙarasa datsewa ba su ka hango hasken da ke kurɗaɗowa, Hankalinsu Ba ƙarami tashi yai ba, A kiɗime su ka mimmiƙe tsaye hatta Azeeza da ke bacci sai da ta farka tana faman murza idanuwanta da yatsun hannayenta.
kallon kallo suka shiga jefawa junansu fuskokinsu ɗauke da matsananciya damuwa
“Innalillahi wa’inna ilaihirraji’un;’ shine kalmar da ta fara fitowa abakunansu Deeja, Yayin da su ke a tsaitsaye cirko cirko, Bakomai ne ya tayar masu da hankali ba face ganin Safiya ta yi ba tare da Angel ta dawo ba. Nan ta ke ransu ya basu cewar wani abu ya faru da ƴar uwarsu.................
Shine meke Faruwane ata 6angaren Angel!?
Ai tun lokacin data watsa da gudu ta nufi Cikin kurkuku, Sautin kururuwa
Mai ƙaraji da gurnani ya cika kunnuwanta, ga wani azababben San yi da ya addabe ta, kamar jaura ta gifta Cikin duhu ta ke gudu
Adai dai lokacin da ta ɗaura ƙafarta saman ground floor ɗin nan Inda ke kewaye da dogayen benaye Ba zato Ba tsammani idanuwanta su ka sauka akan ƙafafuwan Tsohuwa Zafreen Lamarin yai matuƙar gigitar da ita, sam Ba ta yi tsammanin Zata ci karo da wani abu ba ita kawai ta sanyawa ranta cewa Danish ne kaɗai mutumin da zata haɗu da shi.
Mummunar faɗuwa gabanta yai, ƙirjinta ya hau bugu da ƙarfi da ƙarfi A firgice ta ɗago da idonta akan tsohuwa zafreen da ke a ruƙe da sanda, Kasancewar Filin Yana da Fitilu masu haske can saman silin ya gauraye ko’ina, daga ƙasa har sama shigar Jajayen kaya ne a jikinta kamar kullum Fuskarta na asanye da takuntumi.