Sashe 9
Kurkukun Kaddara Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
A haukace Batul ta nufi table ɗin da ke ɗauke da Tunkunyar shayin nan ta ɗaɗɗago shi da hannu biyu, tana haki ta nufi tsohuwa zafreen da ta duƙufa asaman su Rubina, ta daddage ta buga mata shi, Ko gizau batayi ba, Komawa ta yi tare da ɗauko kujerar table ɗin ta dawo ta kuma buga mata ita saman kanta, still bata ɗago ba.
A fujajan ta koma cikin ɗakin tana neman abunda zata ƙwala mata, Duk ta bi ta haukace sai waige waige ta ke yi fuskarta sharkaf da hawaye, har zata juya ta wutsiyar idonta ta hango Rigar wuƙa da ke a so ke a tsakanin littattafan cikin Book shelves ɗin ɗakin.
Tsohuwar ajiye ce wuƙar da tsohuwa Tamira ta ba Danish Kyautarta a lokacin da ya buƙaci yana son datse sumar kan shi, ashe ya maida mata ita shiyasa ko lokacin da Angel ta yi mashi magiya akan ya bata wuƙar Yaƙi bata saboda bata atare da shi, da gudu Batul ta nufi book shelves din ta zura hannu ta ɗauko rigar wukar ta zaro ta Jikinta har salƙi ya ke yi saboda tsabar kaifinta, wuƙar sihiri ce mai haɗarin gaske, Cikin zafin nama ta watsa aguje bata nufi ko’ina ba sai kan Tsohuwa Zafreen a lokacin ta gama da su Rubina juyowar da za ta yi ke da wuya Batul ta daddage ta Luma mata wuƙar Cikin idonta, kafin ta yi wani yunƙurin yin amfani da sihirinta Batul ta ja wuƙar Tun daga kan idonta har zuwa saman wuyanta ta tsartsarga mata Jikinta, Wani irin ƙarfine yazo mata, Dama jinin ta akan akaifa ya ke, Zuciyar ta bushe, Gaba ɗaya tsohuwa zafreen ta gigice saboda azabar zafin da taji na shigar wuƙar, Ta yi ƙoƙarin Buge Batul sai dai Allah bai bata Ikon Yin hakan ba, ba ƙaramin Illah Batul ta yi mata ba, Sai dai duk da haka wani abun mamaki babu ɗigon Jini da ya fito daga idonta, duk inda Batul ta fasa mata da wuƙar kamar ana ɗinke fatar wurin haka ta dinga haɗewa tamkar ba’a ta6a tsaga ta ba.
So ta ke ta lalubo sandar hannunta saboda ƙarfin sihirinta yana a jikin sandar, Idan har babu ita Sauran sihirin da ke a jikinta ba lallai Ya iya yi mata tasiri ba, Daƙyar ta samu ta yi wurgi da Batul gefe ɗaya gaba ɗaya ta kife ƙasa kanta ya daku, wuƙar hannunta ta kufce mata, yunƙurawa zafreen ta yi tare da miƙewa tsaye Jikinta na kakarwa ta soma tafiya tana tunkararta, so ta ke kawai ta kashe ta har Lahira, Cikin fitar hayyaci Batul ta miƙe zaune daga kwancen da ta ke a ƙasa, Ja da baya ta dinga Yi har sai da ta ƙurewa bango.
Tuni tsohuwa zafreen ta cimmata, tafin ƙafarta ta ɗaura saman Yatsun hannun Batul ta murjesu, tsabar raɗaɗin da Batul ta ji ne yasa ta fashe da matsanancin ku ka na fitar hayyaci, wata irin zufa ta soma tsasstafo mata
“Kafin ki kashe Ni, Ni zan fara kashe ki, Dabba kawai, Kin yi kuskure da ki ka soka mini wuƙa A cikin idona, Angaya maki cewa Ni Mutunce da zan mutu farat ɗaya? Tana huci ta yi tambayar, janye tafin ƙafarta tayi daga kan yatsun hannun Batul ta ɗaura ƙafar saman jikinta da ƙarfi ta danna shi tare da murza ƙafar, Jini ne ya soma gangarowa ta cikin bakin batul Nan ta ke Numfashinta ya soma kokawar ɗaukewa.....
Ba zato ba tsammani tsohuwa Zafreen Taji an buge mata kanta da ƙarfi gaba ɗaya ta kife ƙasa, ta baya aka shammace ta, A hanzar ce ta ɗago don ta ga wanene, a matuƙar ruɗe ta ke kallon fuskarta, Ba kowa bace face TSOHUWA TAMIRA.
“Ban yi mamakin ganin ki ba Dama na jima da zargin cewa ba ki atare damu Tamira!” zafreen ce tayi maganar muryarta akausashe, saboda tsabar 6acin rai facial musles din tsohuwa tamira har kerma su ke yi, Hankalinta yai matuƙar tashi ganin yadda zafreen ta lalata rayuwar Yaran da ta raina gaba ɗaya ta gama da rayuwarsu, ta yi danasanin zuwan da ta yi amakare da duk hakan bata faru ba, idanuwanta sun yi jawur dasu tamkar garwashin wuta, wani irin hu ci ta ke futarwa
Yunƙurawa tsohuwa zafreen ta yi tare da miƙewa tsaye, Ido cikin ido su ke kallon juna babu sassauci akan fuskokin kowannan su.
“Ni dama ba ki ta6a burgeni ba, Muguwa azzaluma baƙar kafura, Ban ta6a ganin dabba Jahila daƙiƙiya irin ki ba, Wai ke baki da hankali ne? Ke fa mutunce waɗannan yaran da kika lalata rayuwar su mutanene fa ba dabbo bi ba, Laifin me su ka yi maki da har su ka cancanci wannan hukuncin daga gare ki”? Rai amutuƙar 6ace ta jefa mata tambayar.
Ɗaure fuska tsohuwa zafreen Ta yi, idanuwanta sun kaɗa jawur dasu, Babu ko alamun imani akan fuskarta
Tana magana tana huci kamar mayun waciyar zakanya” Ni kike gayawa magana? Ka da ki manta ke bakowa bace a gidan kurkukun nan face ƙasƙantacciya mai rainon Yara, dole Ki yi mini biyayya saboda ni ke agaba da ke, Nafi ƙarfin ki Tamira nesa ba kusa ba, Idan har kina son ki tsira da ranki to ki gaggauta barin wajen nan tunkafin In yi maki mummunar Ill......”Bata kai ga ƙarasa maganar ba, tsohuwa Tamira ta daka mata tsawa har saida ta furgita, karo na farko kenan da taga Rashin tsoro acikin idon Tamira.
Nuna ta ta yi da yatsan hannunta”ko da can baya da na ke girmamaki ba dan ina jin tsoron ki bane sai don Ƙudirin da na ke dashi na son Rushe Baƙin tarihin da kuka kafa, Ajali ne ke kiran ki shiyasa har ki ka yi gigin shigowa cikin ɗakina, A yau inaso in nuna maki ƙarfin ikon da na ke shi wanda na samu awurin rainon yaran da nake yi, Zafreen Yau zaki yaba ma aya zaƙinta, Ko da zan rasa raina ne saina fara ganin bayanki wulaƙantacciya kawai”a fusace ta ambaci hakan idonta akan fuskar zafreen ga dukkan alamu mamaki da al’jabi ne ya hana ta mayarwa Tamira martanin maganarta. bata ta6a tsammanin tsohuwa Tamira zata Iya yada mata magana ba tare da jin shakkarta ba.
“Tsautsayi da ƙaddara ne suka jefo waɗannan Watsastsun ƙafafuwan naki cikin ɗaki na, Kin ga babu mai kallon mu bare aji sautin mu, Yau zan huce haushina akan ki....” Tunkan ta ƙarasa maganarta, tsohuwa Zafreen ta 6ace ma ganinta, Hankalin tsohuwa Tamira Ba ƙaramin tashi yai ba, babban abunda ta ke ji ma tsoro kada ace ta bar ɗakin, In kuwa haka ta faru zasu fuskanci azabtarwa domin kuwa za ta je ne ta fallasa su.
Jin motsin mutun abayanta yasa ta yi saurin Juyawa, Har saida gabanta Ya ɗan faɗi ganin tsohuwa Zafreen ta bayyana cikin shigar jajayen kayanta hannunta ruƙe da sandarta, ashe 6acewar da ta yi don ta ɗauko sandar hannunta ne ta kuma mayar da suturarta.
“Na yi tsammanin kin ji tsoro kin gudu ne”; acewar tsohuwa Tamira
Mahaukaciyar dariya zafreen Ta saki tare da cewa”Babu tsoro a cikin zuciyar tsohuwa Zafreen! Tamira kin shiga Uku! Kin tsokanowa kanki Bala’e da masifar da ba za ki Iya jurarsu ba, Zan kashe ki har lahira bayan na gama da ke zan ƙarasa kashe waɗanda basu mutu ba a cikin Yaran can naki, Zan sha Jinin su In ci tsokar naman su”
Tana kai ƙarshen maganar ta, ta yi kukan kura tare da Afkawa tsohuwa Tamira, gaba da gabanta Aljani Ya taka wuta, Domin kuwa Zafreen tafi Tamira ƙarfin sihiri, Faɗane ya kaure a tsakanin su kamar dawakai, ba ka iya jin komai sai sautin buge bugen su da gurnaninsu uwa namun dawa, Ƙura ta karaɗe cikin ɗa ki, Kusan atare su ka canza suffofin su, Tsohuwa Zafreen ta rikiɗa ta koma Damusa, Tamira ta koma kura, Ko a namun dawa Damusa ba abokiyar karawar Kura bace, Faɗan nasu Ya canza salo, kamar a filin daga su ka cigaba da kaima junan su Hari duk suka raunata kawunan su.
*ANGEL*
Tsawon lokaci tana a sume saman Gadon da aka kwantar da ita, fatar jikinta jawur da Jinin da su ka yi mata wanka dashi duk ya daskare mata, zai yi wuya yabar Jikinta, saukar ruwan sanyin da ta ji ajikinta ne ya farkar da ita a firguce ta farka, sai dai ta kasa buɗe idanuwanta saboda nauyin dasu ka yi mata, hatta bakinta Yaƙi buɗuwa la66anta sun kumbura suntum wani irin zogin azaba su ke yi mata.
Ba zato ba tsammani kunnuwanta su ka jiyo mata muryar SALSABEEL.
“Meyasa ki ka yi gaggawa? Kin manta me na faɗa ma ki? Sai da nace ku yi takatsantsan idan ba haka ba za ku ja ma kan ku ne damu kan mu....” Sam ta ƙasa motsa bakinta, Idanuwanta kaɗai ta iya samun damar buɗe su akan jikin shi, Yana atsaye Cikin shigar Giant ko’ina na jikin shi arufe kamar yarda ta ganshi a shekaran Jiya. Ta yi mamaki sosai saboda a tattaunar da su ka yi da ita ya faɗa mata cewa ba zata sa ke ganin shi ba, sai ga shi Ya dawo yau, hakan ya tabbatar mata da cewa suna acikin haɗari gaba ɗayan su, taja masu bala’e.
Rushewa ta yi da matsancin kuka raunin da ke abakinta yaci gaba da fitar da jini
Tsananin tausayin ta ne Ya kama shi, ganin yadda suka raunata Jikinta sun gur6ata mata tsaftatacciyar fatarta, tsabar takaici da danasanin gaggawar da ta yi ne yasa ta yin kukan, tana so ta yi ma shi magana sai dai ta kasa saboda sautin muryar ta yaƙi fita ko da tana yin kukan babu sauti.
A fujajan ta koma cikin ɗakin tana neman abunda zata ƙwala mata, Duk ta bi ta haukace sai waige waige ta ke yi fuskarta sharkaf da hawaye, har zata juya ta wutsiyar idonta ta hango Rigar wuƙa da ke a so ke a tsakanin littattafan cikin Book shelves ɗin ɗakin.
Tsohuwar ajiye ce wuƙar da tsohuwa Tamira ta ba Danish Kyautarta a lokacin da ya buƙaci yana son datse sumar kan shi, ashe ya maida mata ita shiyasa ko lokacin da Angel ta yi mashi magiya akan ya bata wuƙar Yaƙi bata saboda bata atare da shi, da gudu Batul ta nufi book shelves din ta zura hannu ta ɗauko rigar wukar ta zaro ta Jikinta har salƙi ya ke yi saboda tsabar kaifinta, wuƙar sihiri ce mai haɗarin gaske, Cikin zafin nama ta watsa aguje bata nufi ko’ina ba sai kan Tsohuwa Zafreen a lokacin ta gama da su Rubina juyowar da za ta yi ke da wuya Batul ta daddage ta Luma mata wuƙar Cikin idonta, kafin ta yi wani yunƙurin yin amfani da sihirinta Batul ta ja wuƙar Tun daga kan idonta har zuwa saman wuyanta ta tsartsarga mata Jikinta, Wani irin ƙarfine yazo mata, Dama jinin ta akan akaifa ya ke, Zuciyar ta bushe, Gaba ɗaya tsohuwa zafreen ta gigice saboda azabar zafin da taji na shigar wuƙar, Ta yi ƙoƙarin Buge Batul sai dai Allah bai bata Ikon Yin hakan ba, ba ƙaramin Illah Batul ta yi mata ba, Sai dai duk da haka wani abun mamaki babu ɗigon Jini da ya fito daga idonta, duk inda Batul ta fasa mata da wuƙar kamar ana ɗinke fatar wurin haka ta dinga haɗewa tamkar ba’a ta6a tsaga ta ba.
So ta ke ta lalubo sandar hannunta saboda ƙarfin sihirinta yana a jikin sandar, Idan har babu ita Sauran sihirin da ke a jikinta ba lallai Ya iya yi mata tasiri ba, Daƙyar ta samu ta yi wurgi da Batul gefe ɗaya gaba ɗaya ta kife ƙasa kanta ya daku, wuƙar hannunta ta kufce mata, yunƙurawa zafreen ta yi tare da miƙewa tsaye Jikinta na kakarwa ta soma tafiya tana tunkararta, so ta ke kawai ta kashe ta har Lahira, Cikin fitar hayyaci Batul ta miƙe zaune daga kwancen da ta ke a ƙasa, Ja da baya ta dinga Yi har sai da ta ƙurewa bango.
Tuni tsohuwa zafreen ta cimmata, tafin ƙafarta ta ɗaura saman Yatsun hannun Batul ta murjesu, tsabar raɗaɗin da Batul ta ji ne yasa ta fashe da matsanancin ku ka na fitar hayyaci, wata irin zufa ta soma tsasstafo mata
“Kafin ki kashe Ni, Ni zan fara kashe ki, Dabba kawai, Kin yi kuskure da ki ka soka mini wuƙa A cikin idona, Angaya maki cewa Ni Mutunce da zan mutu farat ɗaya? Tana huci ta yi tambayar, janye tafin ƙafarta tayi daga kan yatsun hannun Batul ta ɗaura ƙafar saman jikinta da ƙarfi ta danna shi tare da murza ƙafar, Jini ne ya soma gangarowa ta cikin bakin batul Nan ta ke Numfashinta ya soma kokawar ɗaukewa.....
Ba zato ba tsammani tsohuwa Zafreen Taji an buge mata kanta da ƙarfi gaba ɗaya ta kife ƙasa, ta baya aka shammace ta, A hanzar ce ta ɗago don ta ga wanene, a matuƙar ruɗe ta ke kallon fuskarta, Ba kowa bace face TSOHUWA TAMIRA.
“Ban yi mamakin ganin ki ba Dama na jima da zargin cewa ba ki atare damu Tamira!” zafreen ce tayi maganar muryarta akausashe, saboda tsabar 6acin rai facial musles din tsohuwa tamira har kerma su ke yi, Hankalinta yai matuƙar tashi ganin yadda zafreen ta lalata rayuwar Yaran da ta raina gaba ɗaya ta gama da rayuwarsu, ta yi danasanin zuwan da ta yi amakare da duk hakan bata faru ba, idanuwanta sun yi jawur dasu tamkar garwashin wuta, wani irin hu ci ta ke futarwa
Yunƙurawa tsohuwa zafreen ta yi tare da miƙewa tsaye, Ido cikin ido su ke kallon juna babu sassauci akan fuskokin kowannan su.
“Ni dama ba ki ta6a burgeni ba, Muguwa azzaluma baƙar kafura, Ban ta6a ganin dabba Jahila daƙiƙiya irin ki ba, Wai ke baki da hankali ne? Ke fa mutunce waɗannan yaran da kika lalata rayuwar su mutanene fa ba dabbo bi ba, Laifin me su ka yi maki da har su ka cancanci wannan hukuncin daga gare ki”? Rai amutuƙar 6ace ta jefa mata tambayar.
Ɗaure fuska tsohuwa zafreen Ta yi, idanuwanta sun kaɗa jawur dasu, Babu ko alamun imani akan fuskarta
Tana magana tana huci kamar mayun waciyar zakanya” Ni kike gayawa magana? Ka da ki manta ke bakowa bace a gidan kurkukun nan face ƙasƙantacciya mai rainon Yara, dole Ki yi mini biyayya saboda ni ke agaba da ke, Nafi ƙarfin ki Tamira nesa ba kusa ba, Idan har kina son ki tsira da ranki to ki gaggauta barin wajen nan tunkafin In yi maki mummunar Ill......”Bata kai ga ƙarasa maganar ba, tsohuwa Tamira ta daka mata tsawa har saida ta furgita, karo na farko kenan da taga Rashin tsoro acikin idon Tamira.
Nuna ta ta yi da yatsan hannunta”ko da can baya da na ke girmamaki ba dan ina jin tsoron ki bane sai don Ƙudirin da na ke dashi na son Rushe Baƙin tarihin da kuka kafa, Ajali ne ke kiran ki shiyasa har ki ka yi gigin shigowa cikin ɗakina, A yau inaso in nuna maki ƙarfin ikon da na ke shi wanda na samu awurin rainon yaran da nake yi, Zafreen Yau zaki yaba ma aya zaƙinta, Ko da zan rasa raina ne saina fara ganin bayanki wulaƙantacciya kawai”a fusace ta ambaci hakan idonta akan fuskar zafreen ga dukkan alamu mamaki da al’jabi ne ya hana ta mayarwa Tamira martanin maganarta. bata ta6a tsammanin tsohuwa Tamira zata Iya yada mata magana ba tare da jin shakkarta ba.
“Tsautsayi da ƙaddara ne suka jefo waɗannan Watsastsun ƙafafuwan naki cikin ɗaki na, Kin ga babu mai kallon mu bare aji sautin mu, Yau zan huce haushina akan ki....” Tunkan ta ƙarasa maganarta, tsohuwa Zafreen ta 6ace ma ganinta, Hankalin tsohuwa Tamira Ba ƙaramin tashi yai ba, babban abunda ta ke ji ma tsoro kada ace ta bar ɗakin, In kuwa haka ta faru zasu fuskanci azabtarwa domin kuwa za ta je ne ta fallasa su.
Jin motsin mutun abayanta yasa ta yi saurin Juyawa, Har saida gabanta Ya ɗan faɗi ganin tsohuwa Zafreen ta bayyana cikin shigar jajayen kayanta hannunta ruƙe da sandarta, ashe 6acewar da ta yi don ta ɗauko sandar hannunta ne ta kuma mayar da suturarta.
“Na yi tsammanin kin ji tsoro kin gudu ne”; acewar tsohuwa Tamira
Mahaukaciyar dariya zafreen Ta saki tare da cewa”Babu tsoro a cikin zuciyar tsohuwa Zafreen! Tamira kin shiga Uku! Kin tsokanowa kanki Bala’e da masifar da ba za ki Iya jurarsu ba, Zan kashe ki har lahira bayan na gama da ke zan ƙarasa kashe waɗanda basu mutu ba a cikin Yaran can naki, Zan sha Jinin su In ci tsokar naman su”
Tana kai ƙarshen maganar ta, ta yi kukan kura tare da Afkawa tsohuwa Tamira, gaba da gabanta Aljani Ya taka wuta, Domin kuwa Zafreen tafi Tamira ƙarfin sihiri, Faɗane ya kaure a tsakanin su kamar dawakai, ba ka iya jin komai sai sautin buge bugen su da gurnaninsu uwa namun dawa, Ƙura ta karaɗe cikin ɗa ki, Kusan atare su ka canza suffofin su, Tsohuwa Zafreen ta rikiɗa ta koma Damusa, Tamira ta koma kura, Ko a namun dawa Damusa ba abokiyar karawar Kura bace, Faɗan nasu Ya canza salo, kamar a filin daga su ka cigaba da kaima junan su Hari duk suka raunata kawunan su.
*ANGEL*
Tsawon lokaci tana a sume saman Gadon da aka kwantar da ita, fatar jikinta jawur da Jinin da su ka yi mata wanka dashi duk ya daskare mata, zai yi wuya yabar Jikinta, saukar ruwan sanyin da ta ji ajikinta ne ya farkar da ita a firguce ta farka, sai dai ta kasa buɗe idanuwanta saboda nauyin dasu ka yi mata, hatta bakinta Yaƙi buɗuwa la66anta sun kumbura suntum wani irin zogin azaba su ke yi mata.
Ba zato ba tsammani kunnuwanta su ka jiyo mata muryar SALSABEEL.
“Meyasa ki ka yi gaggawa? Kin manta me na faɗa ma ki? Sai da nace ku yi takatsantsan idan ba haka ba za ku ja ma kan ku ne damu kan mu....” Sam ta ƙasa motsa bakinta, Idanuwanta kaɗai ta iya samun damar buɗe su akan jikin shi, Yana atsaye Cikin shigar Giant ko’ina na jikin shi arufe kamar yarda ta ganshi a shekaran Jiya. Ta yi mamaki sosai saboda a tattaunar da su ka yi da ita ya faɗa mata cewa ba zata sa ke ganin shi ba, sai ga shi Ya dawo yau, hakan ya tabbatar mata da cewa suna acikin haɗari gaba ɗayan su, taja masu bala’e.
Rushewa ta yi da matsancin kuka raunin da ke abakinta yaci gaba da fitar da jini
Tsananin tausayin ta ne Ya kama shi, ganin yadda suka raunata Jikinta sun gur6ata mata tsaftatacciyar fatarta, tsabar takaici da danasanin gaggawar da ta yi ne yasa ta yin kukan, tana so ta yi ma shi magana sai dai ta kasa saboda sautin muryar ta yaƙi fita ko da tana yin kukan babu sauti.