← Book details Laylerh Maleek Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 87 OF 144

Sashe 87

Laylerh Maleek Part 1 Complete Hausa Novel · about 3 min read

Acan gida kuwa Oum Ayush dake zaune tana kallo, Jin alamar shigowan sak’o cikin wayarta ne yasa ta d’aukan wayar ta duba, saidai kuma ganin abunda ke rubuce ajikin sak’on ba k’aramin d’aga mata hankali yayi ba, take cikin matsanancin damuwan da ta samu kanta aciki tayi dialing numbern Abbou Khareem d’in, cikin sa’a kuwa tana k’ira ya d’aga, Jin yanda hankalinta ya tashi sosae ne kuma yasashi soma k’ok’arin kwantar mata da hankali, ta hanyar fad’a mata cewar Maleek d’in bai wani ji ciwo sosai ba.
Nantake kuwa tace masa gatanan zuwa.
“Kitaho da Laylerh.� Abunda ya fad’a kenan ak’arshe ya kashe wayar.
Cikin gaggawa kuwa Oum Ayush ta d’auko mayafinta, tare da makullin motar ta, koda ta fito daga sashin nasu kai tsaye sashin su Laylerh’n ta nufa.
Kusan sau biyu tayi knocking k’ofar falon amma shiru ba’a amsa mata ba, kasancewar damuwa ne kwance aranta, hakan yasa batare da wani tunani ba ta tura k’ofar falon ta shiga, ganin da tayi kuma babu kowa acikin falonne yasa ta shiga k’walawa Laylerh’n k’ira.

Laylerh kuwa da har yanzun ke kwance anan kan carpet d’in da tayi sallah, kamar daga sama taji muryan Oum Ayush na kwad’a mata k’ira, hakan yasa cikin sauri ta mik’e tsaye, tare da bud’e k’ofar d’akin ta fice.
Ganinta sanye da Hijab ne yasa Oum Ayush kamo hannunta, cikin muryarta da tayi sanyi sosae tace.
“Zo muje ki rakani wani waje Laylerh.�
Batare kuma da ta jira me Laylerh’n zata ceba ta kamo hannunta suka nufi hanyar fita daga falon.
Fuskar Laylerh’n d’auke da mamaki had’i da rud’u tace.
“Oum Ayush Ina zamuje?, bani da takalmi kibari na d’auko takalmi na.�
Jin abunda tace ne yasa Oum Ayush tsayawa, tare da cewa.
“Kiyi sauri ki d’auko takalmin naki.�
Ganin damuwa kwance akan fuskar Oum Ayush d’inne yasa Laylerh juyawa cikin sabon faduwar gaban da ta samu kanta aciki ta koma cikin d’aki, wani black half cover shoe me tsananin kyau tasa ak’afanta, cikin sauri ta fito.
Sake kamo hannunta Oum Ayush tayi suka fice daga cikin falon.
Ita dai kam kamar rak’umi da akala haka take bin bayan Oum Ayush d’in.
Har saida suka iso jikin mota kafun Oum Ayus d’in ta sake mata hannu.
Nanfa Oum Ayush ta shiga wajen driver itakuwa ta shiga gefen me zaman banza.
Da wani irin speed Oum Ayush ta ja motar yayinda maigadi ya wangale musu gate suka hau saman shumfud’add’en titin dake malale a k’ofar gidan.
Tunda suka shiga motar Laylerh ke kallon Oum Ayush da gaba d’aya yanayinta ya nuna cewa tana cikin damuwa.
Asanyaye kana cikin voice d’inta dake cracking tace.
“Oum tun safe k’irjina bugawa yake, gaba na yana ta fad’uwa, tsoro nakeji matsananci, Dan Allah Oum kifad’amin meke faruwa? Kuma Ina zamuje haka?.�
Shiru Oum Ayush tayi ta kasa amsawa Laylerh’n tambayoyinta, daidai lokacin kuwa suka kawo cikin asibitin.
Ganinsu acikin asibiti ne kuma yasa Laylerh zaro manya manyan idanunta, cikin matsanancin tsoro tace.
“Wayene bashi da lafiya Oum, Dan Allah Karki cemin Yah M.Jay ne, karki cemin mafarkina na jiya ne yakeson zama gaskiya, pleaseee.....�
da katawa da tafiyan Oum Ayush tayi tare da juyowa ta fuskanci Laylerh’n, cikin muryarta da yayi sanyi sosae tace.
“Shi ne Laylerh Maleek ne yayi accident!�
Wani irin bugawa zuciyar Laylerh tayi wanda yayi sanadiyar durk’ushe wanta awajen, tare da zub’e guiwowinta ak’asa.

8February/2021

*7:30 pm*
2/13/21, 7:53 AM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK*

*Writting By*
fatymasardauna

*Chapter 50*
Chapter 87 · 0% Book details