← Book details Laylerh Maleek Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 30 OF 144

Sashe 30

Laylerh Maleek Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read

Abbou Jaheed wanda dama tuntuni zuwan Maleek É—in yake jira ne ya É—ago kansa, tare da É—anyin gyaran murya, cikin yanayin dattako irin nasa yace.
"Alhamdulillah ban taraku anan dan na sanar daku wani abu na daban ba, saidan sanin cewa dukanku kuna da haƙƙi akan maganar da zanyi." Ɗan numfasawa Abbou Jaheed ɗin yayi tare dayin gyaran murya, kana yace.
"Na tsaida lokacin auren Laylerh da Najeeb nan da makonni uku masu zuwa. ina fatan kuma dukanku zakuyi farinciki da hakan."

Tamkar Sukan kifiya akan ƙahon zuciyarsa haka yaji sauƙan kalaman Abbou Jaheed ɗin acikin kunnuwansa.
Idanunsa ya rumtse domin ko kaÉ—an bayason sake jin wani batu daya danganci auren Laylerh'n, wanda yayi imani hakan zai iya fasa masa zuciya.

(Wayyo Bacci😪😓😭😴)

*3/December/2020. time 9:50 pm*
1/19/21, 8:12 PM - Ummi Tandama: *LAYLERH MALEEK*

*Writting By*
fatymasardauna

*(This book is mainly for those that pay, if you know you did'nt pay please don't read it. Here is the account number for people that are willing to pay-0002214625 Abubakar Muhammed Sardauna Jaiz Bank. Whatsapp Number 07017879464)*

                   *Chapter 16*

Zaune suke ita da Teemah aƙasan wata bishiyar flower, wanda kuma da yawan lokuta sukan zauna awajen ne,  idan suka fito break.
Sassanyar iskan bishiyan dake hura duk ilahirin jikinta ne yasa ta lumshe idanunta,  tare da sakin ajiyar zuciya me ƙarfi, wani irin daddaɗan yanayi ta samun kanta aciki, wanda kuma hakanne ya taimaka wajen gusar mata da kaso 40 acikin 100 na damuwar dake kwance acikin ranta.  
kallonta ta mayar ga Teemah dake ta  aikin latsa wayarta, time to time take sakin murmushi, wanda hakan ke bayyana cewar tana jin dadin abun da takeyi acikin wayar tata, zubawa Teemah'n idanu tayi, yayinda lokaci ɗaya kuma maganar auren ta da Najeeb ya dawo cikin tunaninta, wanda hakan yasa ta lumshe kyawawan idanunta, take kuwa wani irin faɗuwar gaba da tsoro suka sauƙar mata, in one second duk wani yanayin nishaɗin da takejin kanta aciki ya kau,  wanda hakan yasa  damuwa ta maye gurbin farincikin dake kan fuskarta.       
Teemah kuwa da take buga game din zombie high way awayanta  ba tare da ta ɗago kai ta kalli Laylerh'n  ba tace.   "Babe  kinsan yanda game ɗinnan keda daɗi kuwa?."        
Laylerh da tun ɗazu idanunta ke alumshe, yayinda ta faɗa wata duniya ta daban, hakan yasa sam bata ji abun da Teemah'n ta faɗa ba, hasalima gaba ɗaya hankali da nutsuwarta ba'ajikinta suke ba.   
Jin shiru Laylerh'n bata amsa  bane yasa  Teemah ta cire kai daga kallon  wayarta ta, tare da ɗagowa ta kai dubanta  zuwa ga inda Laylerh'n ke zaune.         
Ganin Laylerh'n tayi shiru ne yasa ta ƙira sunanta, cikin yanayin mamakin sauyawan mood ɗinta lokaci ɗaya.      

Laylerh kuwa kasancewar har  zuwa yanzu bata cikin nutsuwarta, hakan yasa still bataji ƙiran sunan ta da Teemah'n tayi ba.         
Idanu Teemah ta zuba mata, domin bata taɓa ganin Laylerh'n acikin matsananciyar damuwa irin wannan ba, gane cewa da gaske Laylerh'n ta tafi duniyar tunani ne yasa Teemah ɗan buga kafaɗarta, cikin kulawa tace.  "Wai meye haka Laylerh?.". 

Jin Teemah ta taɓata ne yasa ta buɗe idanunta wanda sukayi jajur dasu.               

"Tunanin me kikeyi?."
Teemah ta tambaya tana me tsareta da idanu.         
Ƙasa tayi da kanta haɗe da fesar da wani irin numfashi me zafi, tabbas tasan cewa agaba ɗaya rayuwarta bata da wata ƙawa ko ƴar uwa sama da Teemah, duk da kasancewar tasan ƙwaƙwalwa da kaifin hankalinsu iri ɗaya ne da na Teemah'n, amma tanaji ajikinta cewa Teemah zata iya warware mata wani  abu daga cikin matsalarta, hakanne kuwa yasa taji zuciyarta ta aminta da ta faɗawa Teemah'n damuwarta.         
Ganin yanda idanun Laylerh'n suka ciko da ƙwalla ne yasa Teemah cewa. 
"Ganin hawaye a idanunki, da kuma shirun da kikayi, hakan alamace dake nuna cewar lallai akwai damuwa atattare dake,  meyake damunki Laylerh,  ko Abbou Jaheed ne zai koma Polland?."         

Idanunta ta lumshe tare da girgida kai alaman "Aa."     

Ajiyar zuciya Teemah ta sauƙe, cikin halin nuna kulawa tace. 
"Okay tell me whats wrong? ba kuma naso ki ɓoyemin komai dan Allah!."     
Jin abun da Teemah'n  ta faɗane yasa idanunta sake cikowa da ƙwalla, kanta dake ƙasa ta ɗago tare da duban Teemah wanda ta tsura mata ido.    Ganin ruwan hawayen dake cikin  idanun Laylerh'n sun ƙaru ne, yasa Teemah zaro idanu, cikin yanayin mamaki tace.
"Laylerh kuka kuma? Please  ki faɗamin meke damunki da har ya saki kuka!."           
Ayanda takejin zuciyarta, yasa  batajin zata iya ɓoyewa Teemah komai,  kuma ya zama dole ta faɗawa Teemah'n  koda hakan zaisa taji sanyi acikin ranta, ƙoƙarin shanye hawayen nata tayi, cikin sanyi da kuma muryar dake bayyana rauninta tace. 
"Teemah Aure Abbou Jaheed zai yimin, zai aurar dani ga wani daban, wanda bansan cewa yana sona ko baya sona ba, tsoro nakeji Teemah bansan ya ake zaman aure ba, bansan ta ina zan fara ba, zuciya ta da ƙirjina bugawa suke, inajin gaba ɗaya duniyar bata min daɗi, haka nakejin tamkar zan rasa wani abu ne da yafi komai mahimmanci arayuwata!." 
Ta faɗi maganar hawayen dake cikin idanunta suna me sauƙa akan fuskarta.  
Idanu Teemah ta ɗan zaro cikin yanayin mamaki tace.  
"Aure kuma Laylerh? wai kina nufin Abbou Jaheed da kansa yace zai aurar dake? waye zai aura miki to?."    Teemah tayi mata duka waƴannan tambayoyin alokaci ɗaya, domin ba kaɗan ba maganar auren Laylerh'n  ya shigeta.         
Guntun hawayen da suka ɗan gangaro daga cikin idanunta ta share, araunane tace. 
"Ki taɓa saitin zuciyata kiji Teemah, gaba ɗaya fargaba ne ya cika cikinta,  sannan inajin wani abu me zafi na sukana."     
Tsagaitawa da maganan tayi tare da kamo hannun Teemah ta ɗaura adaidai saitin zuciyarta, cikin wani irin yanayi tace. 
"Tabbas inada buƙatar sanin haƙiƙanin abun da nakeji acikin zuciyata Teemah, ki taɓa zuciyata da kyau kiji, sam bata da nutsuwa, haka zalika tunani da komai na akansa ne, yanzu na, anjima na, da ma ko yaushe na,  inajinsa yana gudana ajikina tamkar yanda  jini ke gudana, haƙiƙa nayi imani cewa matuƙar na cigaba da rayuwa ahaka wannan yanayin zai illatamin zuciya da kuma gangar jiki, please Teemah ki faɗamin  me yasa nakejinsa ako yaushe? ko acikin baccina shi nake gani, ko wani bugun zuciyata da tunani haɗe da komai nasa yake tafiya, shin me hakan yake nufi ki faɗamin dan Allah tun kafun narasa hankali na!."         
Idanu Teemah ta zuba mata akaron farko kenan da taji ajikinta cewa, ƙawartata  ta samu zaucewar ƙwaƙwalwa. 
Riƙo hannun Laylerh'n tayi da kyau cikin rashin fahimtar inda kalaman Laylerh'n suka dosa tace.   "Ki dawo cikin hayyacinki Laylerh, kada ki bari ki zautar da kanki akan abun da gaskiyarsa yake abayyane, bansan akan wa kike magana ba, ki faiyyace min komai ta yanda zan fahimta, sannan kidaina waƴannan kalaman masu wuyar fahimta please!."             
Jin abun da Teemah'n ta faɗa yasa ta lumshe idanunta, tare da ɗan soma girgiza kai, akaron farko kenan da ta riga ta fahimci cewa Teemah, bazata iya warware mata tsalarta ba, haka zalika kuma ba zata taɓa fahimtar abun dake cikin rai da zuciyarta ba, "Why ƙaddara zata zo mata da nauyi me girma irin haka?, nauyin da har takai ga tanajinsa kaman zai fasa mata ƙwaƙwalwa."
Lallai bata da mafita wanda kuma hakan yasa taji duk gaba ɗaya zaman makarantar ya isheta,  miƙewa tsaye tayi, tare da sa hannu ta dafe kanta da lokaci ɗaya taji yana sara mata. 
Kallonta Teemah tayi tare da cewa.  "Ina kuma zakije?."   
"Class!." ta bata amsa asanyaye batare kuma da ta jirayi komai ba ta fara tafiya.  
ÆŠan jim Teemah tayi na wasu lokuta tare da binta da idanu, itakam sam bata fahimci komai akan lamarin Laylerh'n ba, hasali ma gani tayi kaman Aljanu ne ke damunta.
Ganin cewar da gaske tafiya class Laylerh'n zatayi ta barta yasa cikin hanzari ta rufa mata baya.                    
Chapter 30 · 0% Book details