← Book details Laylerh Maleek Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 15 OF 144

Sashe 15

Laylerh Maleek Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Kusan atare suka shigo cikin gidan su dukansu, Najeeb wanda shiya fara ganin Maleek ɗin, murmushi ne ya faɗaɗa akan fuskarsa, cikin sakewa ya miƙawa Maleek hannu alaman su gaisa, akaron farko kenan tun wayewar gari zuwa yanzu da ya ɗan saki murmushi akan fuskarsa, wanda shima iya kansa kan laɓɓan bakinsa, hannu ya miƙawa Najeeb ɗin suka gaisa.
Alhaji Ahmad Rufa'e ne ya fafaÉ—a fari'arsa tare da É—an bubbuga kafaÉ—an Maleek É—in cikin kulawa yace. "Wellcome back son, i hope kadawo nan Nigeria da zama?."
ÆŠan murmushi yayi wanda ya bayyana tsantsar kyaunsa, cikin husky voice É—insa yace.
"Haka nake tunani."
Murmushi dukansu sukayi, cikin jin dadi Abbu da Alhaji Ahmad Rufa'e sukace.
"Allah yasa."
Abbu ne ya dubi Maleek É—in cikin kulawa yace.
"M.J ga Najeeb ina fatan zamanka a America baisa kamantashi ba."

ÆŠan kallon Najeeb É—in yayi, wanda shima kallonsa yake, batare da ya ce komai ba ya jinjina kai, alaman bai mantashi ba. ÆŠauke kansa yayi gefe tare daÉ—an lumshe idanunsa, wanda hakan ya zame masa sabo kuma É—abi'a.
Najeeb kuwa ƙurawa M.J ɗin idanu yayi, hakanan yaji wani abu aransa game da Maleek ɗin, saidai atake yakau da tunanin dake ransa.

Kusan atare duk suka shiga cikin falon, Momy dake zaune tana ganinsu ta saki murmushi, cikin kulawa da son karrama baƙin nasu tace. "Sannunku da dawowa, kusan mintuna 15 kenan da dinner ke jiranku a dinning."
Murmushi Abbu yayi, tare da kai dubansa ga Maleek wanda ke ƙoƙarin nufar sashinsa.
"Maleek."
Abbu yaƙira sunansa.
Tsayawa da tafiyan yayi tare da É—an juyowa ya kalli Abbu'n nashi. Shima Abbun kallonsa yayi.
Tabbas shi mutum ne me saurin fahimta, sometimes ma yafi fahimtar magana ta ido, fiye da yanda mutum zai furta, wannan yasa ko awajen horar da É—alibai yakan sa su koyan yanda zasuyi magana da idanunsu, haka kuma idan aka musu magana da ido zasu fahimta, yakan gane abun dake zuciyar mutum daga yanayin kallon da mutum É—in keyi masa, gane abun da Abbu ke nufi ne ya sashi fasa shiga side din nasa.
Ƙarasawa dining area din sukayi, wanda tuni anriga da an ƙara yawan kujerun waje, sabanin da da kujeru 4 ne awajen.
Zama sukayi dukansu, yayinda Momy ta shiga ƙoƙarin seving ɗinsu. Abbu ne ya ɗago kai tare da duban Momy cikin kulawa yace.
"Kisa aƙiramin Laylerh?."

Wani baƙin cikine ya tokare maƙoshin ta, sam batason kulawan da Abbu ke bawa Laylerh,Batare da ranta yaso ba ta ƙira ɗaya daga cikin masu aikin gidan, tace da ita taje ta ƙira Laylerh.
Cikin sauri kuwa haka me aikin nasu ta tafi dan cika umarnin Momy'n.

Laylerh da har yanzu ke zaune akan sallaya ta lumshe idanunta tare da dafe saman mararta dake murɗawa, jin ana knocking ƙofar ɗakin nata ne yasa ta bude idanunta, tare da juyawa ta zubawa ƙofar idanu, still knocking ƙofar da aka cigaba da yine, yasa ta miƙewa tsaye, duk da cewar tanajin ciwo amararta amma haka ta cije. Ƙarasawa jikin ƙofar ɗakin tayi tare da buɗewa.
"Kizo in ji Hajiya." Me aikin tafaÉ—a tana me kafe Laylerh'n da idanu.
Kai Laylerh ta jinjina alaman. "To." sanin halin Momy yasa batare da ta koma cikin ɗakin nata ba ta fito, yayinda ta ware ɗan kwalin dake kanta taɗan yafa zuwa wuyanta, duk dama dai vail ɗin dashi gwamma babu dan yana showing sosae. Tana ƙarasowa cikin falon, takai dubanta kan dining area'n, take kuwa idanunta suka sauƙa akan faffaɗan bayansa, kasancewar zaman da yayi ya bawa cikin falon baya ne, wani irin fitinannen sanyi ne taji na shiga jikinta, tare da ratsa tafin ƙafanta, yayinda hancinta ya shiga zuƙo mata daddaɗan ƙamshin turarensa.
Ƙasa tayi da kanta tare da ƙarasowa dining area ɗin.
Najeeb da tun shigowanta cikin falon ya zuba mata idanunsa, har zuwa yanzu kuwa bai É—auke kallonsa daga gareta ba, baisan me yasa ba hakanan yake samun kansa dason kallonta, wani abu na musamman yakeji adangane da ita.
Cikin sanyi taja kujera ta zauna, ɗan ɗago da kanta tayi, bisa tsautsayi idanunta suka faɗa cikin na Najeeb dake jifanta da kallo me ɗauke da ma'anoni daban daban, sauƙe idanunta ƙasa tayi, tare da sauƙesu akan yatsun hannun Maleek dake ɗaure bisa saman table ɗin cin abincin.
Ƙurawa kyawawan fararen yatsun nasa idanu tayi wanda suke ɗauke da shining nails, yatsarsa ta tsakiya ta ƙurawa ido wanda ke sanye da wani haɗaɗɗen shining ring, ajikin ring ɗin an rubuta A.M da manyan baƙi.
Kallon ring ɗin dake hannunta tayi da kyau, sam basu da maraba da wanda ke hannunsa saidai ita harufan da aka rubuta akan nata L.M ne nashi kuma A.M, ɗan jim tayi tare da murza zoben nata, duk da ita kanta batasan da ya akayi zoben ya shiga hannunta ba amma tanason zoben sosai, dan bata taɓa mantawa watarana tun tana ƙarama, ta kwanta bacci koda ta tashi sai gani tayi an sanya mata zobe aɗaya daga cikin yatsun hannunta, tun daga wannan lokacin kuwa bata taɓa cire zoben daga hannunta ba.
So take taÉ—an saci kallonsa amma nauyin hakan takeji.
Ganin duk sun fara cin abincinne yasa ta É—auki plate tayi seving kanta.

Duk yanda taso cin abincin nata ta kasa, domin hakanan takejin kallon da Najeeb keyi mata duk ya takurata, gefe guda kuma ga ciwon marar ta da ya tsananta, rumtse idanunta tayi tare da É—an karyar da wuyanta gefe, ciwo mararta keyi sosae.

Najeeb ne ya tsaida cin abincin da yakeyi tare da zuba mata ido, dan ya karanci cewa akwai abun dake damunta.
"Laylerh!." Yaƙira sunanta cikin wata silent voice.

Laylerh da ayanzu ciwon nata yakaita maƙura har ta kai ga idanunta sun kaɗa sunyi ja, ahankali ta ɗago da kanta ta kallesa.
Idanunsa yaÉ—an zaro waje ganin yanda idanunta suka sauya launi ne yasa cikin kulawa yace.
"Are you okay?."
Samun kanta tayi da kasa tanka masa, lokaci É—aya wasu hawaye suka kwaranyo daga cikin idanunta.

Wanda Sauƙan hawayen nata yayi daidai da ɗago kai da Maleek yayi, wanda tun zuwanta bai ɗago kansa daga abun da yakeyi ba.
Ganin hawaye a idanunta ne ya sashi janye idanunsa daga kanta, asanyaye ya É—an lumshe idanunsa.

*( Menene fata da burin dake cikin zuciyar Laylerh da Maleek? Idan ƙundin Ƙaddaransu ahaɗe take dana juna, me kuke tunanin zai faru anan gaba idan Najeeb ya shigo cikin rayuwar Laylerh? Tabbas akwai wata soyayya me tsananin zafi da taɓa zuciya agaba, kada ku manta tun afarko na faɗa muku cewa wannan salon na dabanne, haka zalika LAYLERH MALEEK daban yake da sauran labarai da kuka sani, kar ku manta yanzu akafara wasan. sannan kuyi haƙuri jia kunjini shiru nayi typing ne ya goge shiyasa, kuma typing akwai wahala sosai😪)*

*Vote nd Comment*

*fatymasardauna*
1/19/21, 8:10 PM - Ummi Tandama: 🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇🍇

       *LAYLERH MALEEK*

     *Writting By*
Phatymasardauna

                    *Wattpad*
             @fatymasardauna

#hausanovels

                   *Chapter 8*

Idanu Najeeb ya zuba mata ganin yanda take ta mutsu mutsu, ga kuma hawaye still na sauƙa akan fuskarta, ganin yanda take taune lips ɗinta ne yasa shi jin wani iri ajikinsa, asanyaye ya sake ƙiran sunanta, akaro na biyuk enan.                   
Kasa amsa masa tayi saima rumtse idanunta da tayi, tare da cizan laɓɓanta, asanyaye ta sa hannu ta share hawayen dake kwance akan fuskarta, jin bazata iya jurewa bane yasa ta ɗaura kanta akan table ɗin cin abincin, sosai marar nata ke ci gaba da  murɗawa, ahankali ta soma sakin sheshsheƙan kuka, tare da dafe saman marar nata da hannunta.         
Tashin sautin sheshsheƙan kukanta ne yasa hankalin su Abbu Jaheed dawowa kanta, cikin kulawa haɗe da nuna tsantsar damuwa Abbu Jaheed yace. 
"Subahanallah Laylerh lafiya meke damunki?."
Yayi maganar cikin yanayi na ɗan ruɗewa.                  
Jin muryar Abbu ne yasa kukan nata ƙaruwa, cikin  sheshsheƙan kuka tace.  "Abbu mara na zai faɗo ƙasa, ciwo nakeji sosai."          
Cikin tausayawa, Abbu da  Alhaji Ahmad suka haɗa baki wajen faɗin.  "Subahanallah!."      
Ɗan jim Abbu Jaheed yayi, take kuma tunanin ƙiran Doctor ya zo masa, waya ya zaro daga cikin aljihunsa, cikin yanayin damuwa yace.
"Bari naƙira Dr.Yazo ya dubaki."         
Baisaurari komae ba yayi dialing number'n Dr.Ishaq.
Bugu biyu kacal Dr. Ishaq  ɗin ya ɗaga, bayan sun gaisane Abbu  yayi masa bayanin abun dake faruwa,  kasancewar sa family doctor ɗinsu, yasa take yace gashinan zuwa.                 Jin hakanne yasa Abbu ya aje wayar, kallon Laylerh'n ya kuma yi wanda har yanzu ke aikin kuka, yayinda ta duƙunƙune jikinta waje ɗaya da dukkan alama ciwon marar ne ke wahalar da ita.       
Cikin tausayinta Abbun yace.    "Sannu ko Laylerh, yanzu Dr. zai zo ya dubaki, am sorry jeki ɗaki ki kwanta kafun Dr. Ishaq ɗin yazo."                 
Jin abun da Abbun ya faɗa ne yasa ta ɗan jan kujeran da take kai baya, cike da son daure ciwon da takeji ta miƙe tsaye,  tashin ta tsaye kuwa yayi daidai da wani irin murɗawa da mararta yayi, wanda hakan yasa ta rumtse idanunta da ƙarfi, tare da sakin wata ƴar ƙara, take jiri ya kwasheta, hakan yasa tatafi luuu zata faɗi, cikin azama Najeeb yasa hannu ya tarota ta faɗa jikinsa. 
Daidai lokacin  kuwa Maleek ya ɗago kansa, wanda tun fara kukan nata ya sadda kansa ƙasa  baisake ɗagowa ba sai yanzun,  ɗago idanunsa da yayi yayi daidai da faɗawarta jikin Najeeb.     Wani irin abune yaji ya caki ƙahon zuciyarsa, wanda zafi da raɗaɗin sa ya ratsa cikin ƙwaƙwalwa da sassan jikinsa, rumtse idanunsa da suka kaɗa sukayi jajur yayi tare da buɗe bakinsa ya fesar da wani zazzafan numfashi.               
Chapter 15 · 0% Book details