Sashe 85
Laylerh Maleek Part 1 Complete Hausa Novel · about 7 min read
Yanayin yanda k’aran fad’uwar motoci biyun suka cika gaba d’aya wajenne yayi sanadiyar dawowan hankalin mutane garesu, ganin irin mummunan accident d’in da akayi ne kuma yasa, hankalin jama’an dake wajen yayi mummunan tashi, domin tuni har d’aya daga cikin motocin tafara hayak’i.
Hakan yasa cikin gaggawa da kuma son ceto rayuka, Jama’a suka nufi wajen da motocin suke da gudu.
Lokaci d’aya wasu daga cikin mutanen suka soma k’ok’arin ciro Maleek da kuma d’ayan mitumin daya kasance shine matuk’in d’aya motar, yayinda wasu kuwa suka shiga k’iran emergency dan basu taimakon gaggawa.
Kasancewar motocin duk sun kwanta ne yasa da k’yar mutanen suka iya ciro ko wannensu daga cikin motarsa, saidai kuma abunda ya k’ara d’agawa jama’ar dake wajen hankali shine, babu mutum d’aya acikinsu dake numfashi, sannan gaba d’ayansu duk jini ya wanke musu fuska.
Salati da sallallami kawae jama’ar wajen keyi, domin ganin da sukayi ya nuna musu cewa, dukansu basa numfashi, da alaman ma cewa babu rai ajikinsu.
Nanfa wasu daga cikin mutanen dake tsaye awajen suka shiga duba motocin acewarsu ko zasu samu wayoyinsu da kuma ID card dan sanin ko sud’in su waye, ta yanda za’a samu asauk’ak’e asanar da y’an uwansu.
Cikin sa’a kuwa suka tsinci wayar Maleek da kuma ID card d’insa, abun mamakin kuwa wayarsa ko fashewa d’aya batayi ba, tana nan normal, hakama na d’ayan me motar saidai nashi screen d’in wayar ta d’an fashe kad’an.
Isowan Emergency wajen cikin gaggawa ne yasa mutanen suka taimaka musu wajen saka su Maleek d’in acikin mota, duka wayoyi da kuma ID card d’in da suka samu suka mik’awa ma’aikatan lafiyan.
Nanfa cikin gaggawa motar Emergency d’in ta kama hanya zuwa babban asibitin nan me suna Nizamiyye Hospital.
Yanayin yanda motar Emergency’n ke matsanancin gudu ne kuma yasa cikin y’an k’alilan d’in mintuna suka samu isowa cikin harabar babban asibitin.
Da wani irin sauri Doctor’s suka zo da irin gadon nan da ake d’aukan marassa lafiya acikinsa.
Anan kan gadon aka d’auki kowannensu cike dason basu taimakon gaggawa kaitsaye aka wuce dasu Intensive Care Unit wato (ICU) dan basu taimakon gaggawa kasancewar duk acikinsu babu wanda yake numfashi.
Likitotine wanda ak’alla zasu kai guda 6 suka duk’ufa akan Maleek wanda kansa keta faman zubda jini, tabbas babu numfashi ajikinsa, amma kuma wani babban abun mamakin shine zuciyarsa na bugawa, al’amarin daya d’aure musu kai kenan, sanin kuma da sukayi cewar Idan har basu dage wajen yin k’ok’arin dawo da numfashinsa ba to tabbas bugun zuciyartasa ma zai iya tsayawa, hakan kuma zai iya jawo sanadiyar rasa rayuwarsa gaba d’aya, nan fa cikin azama suka shiga k’ok’arin tsaida jinin dake zuba akansa, kasancewar ya bugu sosae akannasa shiyasa yake ta zubarda jini ba k’akk’autawa, Uwa uba kuma duk glasses d’in motar ya caccake masa jiki.
Sab’anin abokin accident d’in nasa da buguwa kawae ya samu, akai da kuma k’afarsa, saidai kuma buguwar k’afartasa yafi na ko ina muni, dan k’afartasa taji ciwo sosae, saidai shi bashi da wata matsala bayan wannan, Inda kuma cikin sauk’i likitotin dake kansa suka samu daman ceto numfashinsa, ganin kuma da sukayi cewar akoda yaushe zai iya dawowa cikin hayyacinsa ne, yasa suka kaishi wani d’aki na daban.
Yayinda doctors d’in dake aiki akan Maleek kuwa suka ci gaba da gudanar da aikinsu, domin har yanzu sun kasa samo numfashin Maleek d’in.
Laylerh
Ahankali ta bud’e murfin k’ofar bathroom d’in ta fito, yayinda fuskarta da kuma hannaye da k’afafunta ke d’auke da danshin ruwa, wanda hakan nuna cewar alwala ta d’auro acikin toilet d’in.
Cikin yanayin sanyin jikin da takejin kanta aciki ta k’arasa gaban drawer’nta, ta ciro wani d’an madaidaicin Hijab d’inta ta saka, juyawa tayi tare da jingina bayanta da jikin drawer’n ahankali ta lumshe idanunta, wanda tun d’azu takejin k’walla nason taruwa acikinsu wanda kuma sam batasan dalilin hakan ba, gaba d’aya tun tashinta abacci takejin mood d’inta ya sauya batare kuma da tasan dalilin hakan ba, fad’uwar gaba take taji, da wani irin tsoro wanda batasan daga inane yake b’ullowa ba, babban abunda ke k’ara da gula mata lissafi kuwa shine tunanin Maleek dake fad’o mata akai akai, wanda kuma hakanne ke haifar mata da k’arin bugun zuciya.
“Yah Allah Kasa komai yazomin cikin sauk’i, Allah Kaga zuciyata ayanzu gab take da bugawa, ina rok’oka kada ka tabbatar da mummunan mafarkin da nayi akan Yah M.Jay, Ya Allah Kaduba maraicin mu!!!�
Tafad’i hakan cikin muryarta da tayi rauni sosai, tare dasa d’an yatsanta ta share hawayen dake k’ok’arin sauk’a daga cikin idanunta.
Hak’ik’a ayanzu nutsuwar zuciya da kuma farinciki takeso, domin su kad’aice zasu kore mata tsanancin tsoron da takeji.
Asanyaye cikin bawa kanta k’warin guiwa ta k’arasa gaban d’an madaidaicin carpet d’in dake shumfud’e a gefen gadonta, wanda kuma an shumfud’a carpet d’inne musamman dan akeyin Sallah akansa.
Daidaita tsayuwarta akan carpet d’in tayi, tare fuskantar gabas ta tada sallah’n azahar wanda tuni masallacin dake gefen gidannasu har sun shiga salla’n.
Kasancewar ayanzun kusan k’arfe 1 da wasu y’an mintuna ake nema.
Koda ta idar da sallan kuwa anan kan sallayan ta kwanta, duk da cewar tanajin yunwa na k’wak’ulan cikinta amma batajin zata iya saka ko wani irin abinci acikinta.
After 1hour.
Kusan atare gaba d’aya likitotin da har yanzu ke tsaye akan Maleek d’in suka d’ago kansu suka kalli juna, yayinda kowannensu yanayin fuskarsa ke d’auke da matsanancin damuwa, tabbas sunsha wahala matuk’a wajen ganin Maleek d’in ya tsira da numfashi, sunkuma yi sa’a domin Allah Ya dafa musu wajen ganin sun dawo masa da numfashinsa, duk da cewar bai farfad’o ya dawo hayyacinsa ba, amma tabbas suna saka ran farfad’owarsa akoda yaushe, ganin da sukayi kuma ya bugu sosai akansa da kuma sauran sassan jikinsa ne yasa suka d’anyi masa gwaje gwaje dan tabbatar da lafiyar jiki da kuma na kansa, sunji dad’i k’warai da sukaga cewar buguwan da yayi akannasa bai tab’a masa kansa ba, saidai wani babban matsala da suka gani daga wani waje na dabanne yasa su shiga alhini tare dajin matsanancin tausayin Maleek d’in ya cika musu zuciya.
D’aya daga cikin doctors d’inne yayi masa duk wasu alluran da suka dace, sannan sukayi treating duk wani ciwo dake jikinsa, duk dama ciwukan nasa y’an k’ananan yankane daya samu ta sanadin glasses d’in da suka d’an cakesa.
Nanfa biyu daga cikin doctors d’in suka tura gadon da yake cikin wani special room, inda babu yawan hayaniya sosai.
After 2hours
Acan gida kuwa Abbou Jaheed ne zaune acikin katafaren falonsa wanda yaji komai da komai na more rayuwa, domin kuwa falo ne wanda ya amsa sunan falo, irin na manya manyan masu kud’i da kuma matsayi.
Zaune yake akan d’aya daga cikin luntsuma luntsuman kujerun dake cikin falon, agabansa kuwa wani babban stool ne wanda samansa ke d’auke da wasu invitations card’s masu yawan gaske, d’aya bayan d’aya kuwa haka yake d’aukan cards d’in yana dubawa, da dukkan alamu kuma katunan dake gabannasa na d’aurin auren Maleek ne.
Turo k’ofar falon da kuma sallaman da yaji anyi ne yasashi d’ago kansa, abakinsa kuwa yana me amsa sallaman, da Abbou Khareem da kuma Fou’ad ne sukayi ta.
Ganinsu da yayine yasashi d’an sakin murmushi, tare da cewa. “Kuyi hak’uri na d’ago ku akan uzururrukan da kukeyi.�
Murmushi dukansu sukayi tare da k’arasowa cikin falon, wato inda Abbou Jaheed d’in ke zaune.
“Babu komae Yayah Allah Dai yasa muji alkhairi.�
Cewar Abbou Kareem fuskarsa d’auke da yalwatacciyar murmushi.
“Insha Allah Ma alkhairi ne.� Abbou Jaheed ya fad’a yana me d’an gyara zama.
Fou’ad kuwa dake k’ok’arin zama akan had’adden sofan dake malale atsakiyar falon, cikin girmamawa yace.
“Abbou barka da gida.�
“Yauwa barka dae Malam Fou’ad ya aiki, da kuma fama da Jama’a?.�
“Lafiya Alhamdulillah.�
Fou’ad ya amsa yana me d’an shafa kansa.
“To Masha Allah dama haka akeso.�
Abbou Jaheed ya fad’a yana me k’ok’arin har had’a cards d’in dake zube agabansa.
Shiru sukayi na d’an wani lokaci kafun Abbou Jaheed d’in ya zaro wasu daga cikin invitations cards d’in dake gabansa ya mik’awa kowannensu, fuskarsa d’auke da damuwar da sam ya kasa b’oyeta afili da kuma bad’ininsa yace.
“Ga katin auren Maleek nan, d’azu way’anda na bawa kwangilan bugawa suka kawomin, abunda yasa na k’iraku kuma kenan, domin nasan kuma kunada naku jama’an da zaku gayyata, gasunan sai ku d’ebi wanda zai isheku.� Ya k’are maganar yana me tura musu katunan gabansu.
Hakan yasa cikin gaggawa da kuma son ceto rayuka, Jama’a suka nufi wajen da motocin suke da gudu.
Lokaci d’aya wasu daga cikin mutanen suka soma k’ok’arin ciro Maleek da kuma d’ayan mitumin daya kasance shine matuk’in d’aya motar, yayinda wasu kuwa suka shiga k’iran emergency dan basu taimakon gaggawa.
Kasancewar motocin duk sun kwanta ne yasa da k’yar mutanen suka iya ciro ko wannensu daga cikin motarsa, saidai kuma abunda ya k’ara d’agawa jama’ar dake wajen hankali shine, babu mutum d’aya acikinsu dake numfashi, sannan gaba d’ayansu duk jini ya wanke musu fuska.
Salati da sallallami kawae jama’ar wajen keyi, domin ganin da sukayi ya nuna musu cewa, dukansu basa numfashi, da alaman ma cewa babu rai ajikinsu.
Nanfa wasu daga cikin mutanen dake tsaye awajen suka shiga duba motocin acewarsu ko zasu samu wayoyinsu da kuma ID card dan sanin ko sud’in su waye, ta yanda za’a samu asauk’ak’e asanar da y’an uwansu.
Cikin sa’a kuwa suka tsinci wayar Maleek da kuma ID card d’insa, abun mamakin kuwa wayarsa ko fashewa d’aya batayi ba, tana nan normal, hakama na d’ayan me motar saidai nashi screen d’in wayar ta d’an fashe kad’an.
Isowan Emergency wajen cikin gaggawa ne yasa mutanen suka taimaka musu wajen saka su Maleek d’in acikin mota, duka wayoyi da kuma ID card d’in da suka samu suka mik’awa ma’aikatan lafiyan.
Nanfa cikin gaggawa motar Emergency d’in ta kama hanya zuwa babban asibitin nan me suna Nizamiyye Hospital.
Yanayin yanda motar Emergency’n ke matsanancin gudu ne kuma yasa cikin y’an k’alilan d’in mintuna suka samu isowa cikin harabar babban asibitin.
Da wani irin sauri Doctor’s suka zo da irin gadon nan da ake d’aukan marassa lafiya acikinsa.
Anan kan gadon aka d’auki kowannensu cike dason basu taimakon gaggawa kaitsaye aka wuce dasu Intensive Care Unit wato (ICU) dan basu taimakon gaggawa kasancewar duk acikinsu babu wanda yake numfashi.
Likitotine wanda ak’alla zasu kai guda 6 suka duk’ufa akan Maleek wanda kansa keta faman zubda jini, tabbas babu numfashi ajikinsa, amma kuma wani babban abun mamakin shine zuciyarsa na bugawa, al’amarin daya d’aure musu kai kenan, sanin kuma da sukayi cewar Idan har basu dage wajen yin k’ok’arin dawo da numfashinsa ba to tabbas bugun zuciyartasa ma zai iya tsayawa, hakan kuma zai iya jawo sanadiyar rasa rayuwarsa gaba d’aya, nan fa cikin azama suka shiga k’ok’arin tsaida jinin dake zuba akansa, kasancewar ya bugu sosae akannasa shiyasa yake ta zubarda jini ba k’akk’autawa, Uwa uba kuma duk glasses d’in motar ya caccake masa jiki.
Sab’anin abokin accident d’in nasa da buguwa kawae ya samu, akai da kuma k’afarsa, saidai kuma buguwar k’afartasa yafi na ko ina muni, dan k’afartasa taji ciwo sosae, saidai shi bashi da wata matsala bayan wannan, Inda kuma cikin sauk’i likitotin dake kansa suka samu daman ceto numfashinsa, ganin kuma da sukayi cewar akoda yaushe zai iya dawowa cikin hayyacinsa ne, yasa suka kaishi wani d’aki na daban.
Yayinda doctors d’in dake aiki akan Maleek kuwa suka ci gaba da gudanar da aikinsu, domin har yanzu sun kasa samo numfashin Maleek d’in.
Laylerh
Ahankali ta bud’e murfin k’ofar bathroom d’in ta fito, yayinda fuskarta da kuma hannaye da k’afafunta ke d’auke da danshin ruwa, wanda hakan nuna cewar alwala ta d’auro acikin toilet d’in.
Cikin yanayin sanyin jikin da takejin kanta aciki ta k’arasa gaban drawer’nta, ta ciro wani d’an madaidaicin Hijab d’inta ta saka, juyawa tayi tare da jingina bayanta da jikin drawer’n ahankali ta lumshe idanunta, wanda tun d’azu takejin k’walla nason taruwa acikinsu wanda kuma sam batasan dalilin hakan ba, gaba d’aya tun tashinta abacci takejin mood d’inta ya sauya batare kuma da tasan dalilin hakan ba, fad’uwar gaba take taji, da wani irin tsoro wanda batasan daga inane yake b’ullowa ba, babban abunda ke k’ara da gula mata lissafi kuwa shine tunanin Maleek dake fad’o mata akai akai, wanda kuma hakanne ke haifar mata da k’arin bugun zuciya.
“Yah Allah Kasa komai yazomin cikin sauk’i, Allah Kaga zuciyata ayanzu gab take da bugawa, ina rok’oka kada ka tabbatar da mummunan mafarkin da nayi akan Yah M.Jay, Ya Allah Kaduba maraicin mu!!!�
Tafad’i hakan cikin muryarta da tayi rauni sosai, tare dasa d’an yatsanta ta share hawayen dake k’ok’arin sauk’a daga cikin idanunta.
Hak’ik’a ayanzu nutsuwar zuciya da kuma farinciki takeso, domin su kad’aice zasu kore mata tsanancin tsoron da takeji.
Asanyaye cikin bawa kanta k’warin guiwa ta k’arasa gaban d’an madaidaicin carpet d’in dake shumfud’e a gefen gadonta, wanda kuma an shumfud’a carpet d’inne musamman dan akeyin Sallah akansa.
Daidaita tsayuwarta akan carpet d’in tayi, tare fuskantar gabas ta tada sallah’n azahar wanda tuni masallacin dake gefen gidannasu har sun shiga salla’n.
Kasancewar ayanzun kusan k’arfe 1 da wasu y’an mintuna ake nema.
Koda ta idar da sallan kuwa anan kan sallayan ta kwanta, duk da cewar tanajin yunwa na k’wak’ulan cikinta amma batajin zata iya saka ko wani irin abinci acikinta.
After 1hour.
Kusan atare gaba d’aya likitotin da har yanzu ke tsaye akan Maleek d’in suka d’ago kansu suka kalli juna, yayinda kowannensu yanayin fuskarsa ke d’auke da matsanancin damuwa, tabbas sunsha wahala matuk’a wajen ganin Maleek d’in ya tsira da numfashi, sunkuma yi sa’a domin Allah Ya dafa musu wajen ganin sun dawo masa da numfashinsa, duk da cewar bai farfad’o ya dawo hayyacinsa ba, amma tabbas suna saka ran farfad’owarsa akoda yaushe, ganin da sukayi kuma ya bugu sosai akansa da kuma sauran sassan jikinsa ne yasa suka d’anyi masa gwaje gwaje dan tabbatar da lafiyar jiki da kuma na kansa, sunji dad’i k’warai da sukaga cewar buguwan da yayi akannasa bai tab’a masa kansa ba, saidai wani babban matsala da suka gani daga wani waje na dabanne yasa su shiga alhini tare dajin matsanancin tausayin Maleek d’in ya cika musu zuciya.
D’aya daga cikin doctors d’inne yayi masa duk wasu alluran da suka dace, sannan sukayi treating duk wani ciwo dake jikinsa, duk dama ciwukan nasa y’an k’ananan yankane daya samu ta sanadin glasses d’in da suka d’an cakesa.
Nanfa biyu daga cikin doctors d’in suka tura gadon da yake cikin wani special room, inda babu yawan hayaniya sosai.
After 2hours
Acan gida kuwa Abbou Jaheed ne zaune acikin katafaren falonsa wanda yaji komai da komai na more rayuwa, domin kuwa falo ne wanda ya amsa sunan falo, irin na manya manyan masu kud’i da kuma matsayi.
Zaune yake akan d’aya daga cikin luntsuma luntsuman kujerun dake cikin falon, agabansa kuwa wani babban stool ne wanda samansa ke d’auke da wasu invitations card’s masu yawan gaske, d’aya bayan d’aya kuwa haka yake d’aukan cards d’in yana dubawa, da dukkan alamu kuma katunan dake gabannasa na d’aurin auren Maleek ne.
Turo k’ofar falon da kuma sallaman da yaji anyi ne yasashi d’ago kansa, abakinsa kuwa yana me amsa sallaman, da Abbou Khareem da kuma Fou’ad ne sukayi ta.
Ganinsu da yayine yasashi d’an sakin murmushi, tare da cewa. “Kuyi hak’uri na d’ago ku akan uzururrukan da kukeyi.�
Murmushi dukansu sukayi tare da k’arasowa cikin falon, wato inda Abbou Jaheed d’in ke zaune.
“Babu komae Yayah Allah Dai yasa muji alkhairi.�
Cewar Abbou Kareem fuskarsa d’auke da yalwatacciyar murmushi.
“Insha Allah Ma alkhairi ne.� Abbou Jaheed ya fad’a yana me d’an gyara zama.
Fou’ad kuwa dake k’ok’arin zama akan had’adden sofan dake malale atsakiyar falon, cikin girmamawa yace.
“Abbou barka da gida.�
“Yauwa barka dae Malam Fou’ad ya aiki, da kuma fama da Jama’a?.�
“Lafiya Alhamdulillah.�
Fou’ad ya amsa yana me d’an shafa kansa.
“To Masha Allah dama haka akeso.�
Abbou Jaheed ya fad’a yana me k’ok’arin har had’a cards d’in dake zube agabansa.
Shiru sukayi na d’an wani lokaci kafun Abbou Jaheed d’in ya zaro wasu daga cikin invitations cards d’in dake gabansa ya mik’awa kowannensu, fuskarsa d’auke da damuwar da sam ya kasa b’oyeta afili da kuma bad’ininsa yace.
“Ga katin auren Maleek nan, d’azu way’anda na bawa kwangilan bugawa suka kawomin, abunda yasa na k’iraku kuma kenan, domin nasan kuma kunada naku jama’an da zaku gayyata, gasunan sai ku d’ebi wanda zai isheku.� Ya k’are maganar yana me tura musu katunan gabansu.