Sashe 86
Laylerh Maleek Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Jin abunda Abbou Jaheed d’in ya fad’ane kuma yasa, Fou’ad d’ago kai ahankali ya maida dubansa ga Abbou Jaheed d’in, wanda take ya karanci zallan damuwa akan fuskarsa, tabbas yasan abunda Abbou Jaheed d’in keyi k’arfin haline kawae, saboda kallo d’aya zakayi masa kafahimci cewa yana cikin damuwar rashin ganin d’ansa.
Ajiyar zuciya ya sauk’e kana jikinsa amatuk’ar sanyaye, cikin ladabi da kuma sanyin murya ta yanda ya tabbatar cewa Abbou Jaheed d’in zai fahimcesa yace.
“Kayi hak’uri da abunda zan fad’a Abbou domin nasan ba lallaine yayi maka dad’i ba, saidai kuma ya zama
dole na fad’a maka cewar kwata kwata Maleek bayason auren nan, domin saboda hakanne ma yaje ya b’oye kansa awani waje, wajen da babu wanda yasani acikin mu, hak’ik’a inajin tsoron abunda zaije ya dawo bayan an d’aura aurennan, saboda akullum Maleek yana ikirarin cewa shi bazai tab’a zama da wata mace ba, burinshi akoda yaushe shine yayi rayuwarsa shi kad’ai, please Abbou Dan Allah Ajanye maganar auren nan.�
Murmushi me d’auke da dattako Abbou Jaheed yayi, tare da d’ago kansa ya kalli Fou’ad d’in.
Tabbas shi kansa ya jima da fara irin wannan tunanin, amma kuma saidai yasan ko kad’an babu alfano acikin tunanin nasa, barin cikakken Namiji me lafiya kamar Maleek babu aure sam ba daidai bane, saboda arayuwar ko wani d’a Namiji me lafiya yana buk’atar Mace, domin Mace itace duk wani ginshik’in jin dad’i, saida Mace arayuwar ko wani Namiji zai kasance acikin farinciki, tabbas Mace itace komai na rayuwar d’a Namiji, domin saida mace ne kowani Namiji zaisan wanene shi.
Ajiyar zuciya Abbou Jaheed d’in ya sauk’e, tare dayin gyaran murya, cikin tausasa kalamansa yanda yake da yak’inin cewa Fou’ad d’in zai gamsu yace.
“Bawai ina son tursasawa Maleek koyi masa auren dole bane, ina duba abunda ya dace ne, hak’ik’a burin kowani uba shine yaga ya aurar da y’ay’ansa bawai y’ay’ansa mata ba kawae harda maza, domin barin cikakken Namiji baligi agida wanda ya haura shekaru 30 ba daidai bane, matuk’ar yana da lafiya kuma yana da halin yin aure to yayi kawai, saidai kuma idan yana da hujjar cewa bazae tab’a kusantar zina ba, wannan zai iya zama yayi rayuwarsa shi kad’ai, tabbas ada bandamu akan Maleek yayi aure ko a’a ba, domin duk da cewa zuciya bata da k’ashi, amma Ina da yak’ini akansa, tabbas Ina da yak’inin cewa ban haifi fasik’i ba, hak’ik’a najima da bawa Maleek zab’i akan ya nemo matar da yakeson aura, amma yayi watsi da magana ta, haka na hak’ura na k’yalesa, nabarsa ne kuma saboda inaso naga iyaka gudun ruwansa, saboda tabbaci da nake dashi akansa, saidai kuma lokaci d’aya ya ruguza duk wata yarda ta da nake dashi akansa, nagansa da idanuna ya dawo gida acikin maye, cikin k’azamammen yanayin da duk wani Uba na duniya bazai so yaga d’ansa aciki ba, tabbas nasan Ilan maye, yakansa mutum ya aikata komai, ciki kuma harda zina, to Fou’ad ka gayamin tayaya zanbar tilon d’ana Maleek ya kasance acikin irin wannan halin? wannan dalilin shiyasa na yanke hukuncin d’aura masa aure ko da yana so ko bayaso, bankuma yi hakan don banason sa ba, saidan Ina guje masa fad’awa halaka da kuma tsinuwar Allah..�
Sosae jikin Fou’ad yayi sanyi asakamakon jin kalamai da kuma hujjar Abbou Jaheed nason yiwa Maleek aure, hak’ik’a ada yana ganin kamar cewa Abbou Jaheed d’in nason tauye Maleek ne, amma ayanzu tabbas ya fahimci komai, domin shi kansa yana da yak’inin cewa matuk’ar Maleek d’in ya fara shaye shaye to watarana maye zata iya sawa ya aikata ba daidaiba, domin sarai yasan abokinnasa yana da k’arfin sha’awa.
Baki ya bud’e da niyar cewa wani abu amma kuma saidai k’iran da ya shigo wayar Abbou Jaheed ne yasashi tsuke bakinsa.
Abbou Jaheed kuwa akaron farko kenan da yaji k’iran waya ya tsinkar masa da zuciya.
Asanyaye ya kai hannu ya d’aga wayar, duk da cewar bakuwar number ya gani amma hakan bai hanashi d’agawa ba tare da kara wayar akan kunnensa, sallaman da akayi masa ya amsa, saidai kuma jin abunda wanda ke kan wayar ke fad’ane yasashi jin wani irin matsanancin fad’uwar gaba da kuma tashin hankali me tsanani wanda har saida ya kaisa ga mik’ewa tsaye, cikin kid’ima da kuma rud’ewa ya ambaci kalmar “Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un!!!�
Batare kuma daya daidaita nutsuwarsa ba yasaki wayar tasa ta fad’i k’asa.
Hakan da yayin kuwa shiya saka hankalin su Abbou Khareem da kuma Fou’ad yayi wani irin masifaffen tashi, cikin yanayin mamaki da kuma rud’ewa suka shiga tambayarsa ko lafiya.
Kasa amsa musu yayi sai sa hannu da yayi ya dafe daedae saitin zuciyarsa, da kuma k’irjinsa dake bugawa sosae, ganin hakane yasa Fou’ad nufar wajen fridge ya d’auko goran ruwa me sanyi, mik’awa Abbou Jaheed d’in goran ruwan yayi, cikin yanayin damuwa yace.
“Abbou lafiya meyake faruwa ne?.�
Wani irin numfashi Abbou Jaheed da gaba d’aya hankalinsa baya jikinsa yayi, cikin muryarsa da ta sark’e yace.
“Maleek ne yayi accident, Khareem Maleek d’ana yayi accident, baisan inda kansa yake ba, Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un, Ya Allah Kasa kada na zamo silar rasa rayuwar.......�
Cikin tashin hankali Abbou Khareem yasa hannunsa ya toshewa Yayan nasa baki, kansa ya d’an girgiza cike dason samarwa d’an uwannasa nutsuwa yace.
“Kada kace haka Yayah Allah Yana tare damu, yafi kowa sanin niya da kuma nufin dake cikin zuciyarka, awani asibiti Maleek d’in yake, mu hanzarta zuwa dansanin halin da yake ciki.�
“Nizamiyye hospital!� Abbou Jaheed d’in ya fad’a da muryarsa wanda take fitar da zallan tashin hankalin da yake ciki.
Yayinda Fou’ad kuwa tsabar shocking d’in da ya samu kansa aciki, kasa furta komai yayi, sai jikinsa dake ta faman karkarwa.
Hannun Abbou Jaheed d’in Abbou Khareem ya kamo cikin dauriya yace.
“Muje muje lokaci na k’urewa.�
Haka suka fice daga cikin falon dukansu babu wanda yake da gamsashshiyar nutsuwa atattare dashi, ko awajen tuk’in mota ma Fou’ad ne ya iya dauriyan tuk’asu, saidai kuma irin gudun da yake tsulawa yasa duk wanda ya ga motar tasu saidai ya kauce ya basu hanya.
Yanayin yanda Fou’ad d’in ke gudu kaman zai tashi sama ne yasa cikin mintuna kad’an suka iso farfajiyar asibitin.
Ko tsayawa gama daidai ta parking baiyi haka suka fito cikin tashin hankali sukayi cikin asibitin, murafen motar ma a bud’e suka barsu.
Abbou Khareem ne ya d’auki wayar Abbou Jaheed d’in ya k’ira numbern da aka k’irasu dashi d’azun dan sanin inda aka ajiye Maleek d’in.
Da yake kuma numbern na d’aya daga cikin doctors d’in asibitin da suka karb’i Maleek d’inne, yasa cikin sauk’i Doctorn ya musu kwatancen office d’insa, suna zuwa kuwa suka samu duka doctors d’in atare awaje d’aya.
Ganin irin tashin hankali da kuma damuwan dake d’auke akan fuskokinsu ne yasa Doctors d’in soma k’ok’arin kwantar musu da hankali.
Ta hanyar ce musu Maleek d’in yana nan lafiya.
“Kufad’amin idan wani abu ya samu d’ana, yana Ina ku kaini naga Maleek, shi kad’aine d’an dana Haifa aduniya Dan Allah ku fad’amin cewa Maleek yana darai bai mutu ba!!!� Abbou Jaheed ya fad’i hakan cikin tashin hankalin da yakejin kansa aciki.
Murmushi Dr.Mouhammad yayi, wanda shine babban likitan dake kan case d’in Maleek d’in, cikin son kwantarwa da Abbou Jaheed d’in hankali yace.
“Alhaji Jaheed Gwani ka kwantar da hankalinka domin d’anka bai mutu ba, domin tabbatar da hakan kuwa kana iya Bina muje kaga d’anka.�
Ae ma kafun Dr Mouhammad ya rufe bakinsa, tuni Abbou Jaheed yace.
“Muje Doctor muje nagansa.�
Shigewa gaba Dr Mouhammad yayi, yayinda su Abbou Jaheed suka rufa masa baya.
Kaitsaye d’akin da Maleek d’in ke kwance suka nufa, bud’e musu k’ofar d’akin Dr. Mouhammad yayi tare dayi musu alama akan su shiga, riga rigen shiga kuwa sukayi, yayinda kuma suna shiga suka sauk’e idanunsu akan Maleek d’in dake kwance flat akan gado, kansa nad’e da bandage.
Cikin sauri Abbou Jaheed ya k’arasa kusa da gadon, tare dasa hannayensa duka biyu ya rungume Maleek d’in, lokaci guda yaji wasu irin hawaye sun cika idanunsa, matsanancin tausayin d’annasa ne ya kamasa, hakan yasa ya d’aura kansa akirjin Maleek d’in daidai inda zuciyarsa take, wani irin ajiar zuciya me k’arfi ya sauk’e alokacin da kunnuwansa suka jiye masa sautin bugun zuciyar Maleek d’in, cikin zuciyarsa yace.
“Alhamdulillah!�
K’arasowa wajen Maleek d’in su Abbou Khareem da Fou’ad sukayi, cike da tausayin Maleek d’in suka shafa kansa dake lik’e da bandage.
Gaba d’ayansu tausayi suka bawa Dr.Mouhammad hakan yasa shi d’anyin gyaran murya cikin kulawa yace.
“Ayanzu Maleek hutu yake da buk’ata, bazan hanaku zama awajensa ba, amma saidai ku kiyaye yin surutu, sannan zai iya bud’e idanunsa any time, zuwa anjima kad’an akwai alluran da zanzo na sake yi masa, so dan Allah Ku kula sosae.�
“Insha Allah Zamu kula doctor.�
Cewar Fou’ad dake k’ok’arin maida k’wallan dake cikin idanunsa.
Kai Dr.Mouhammad ya jinjina, anutse yasa kai ya fice daga cikin d’akin, zuciyarsa cike da alhinin ta yanda zai fara fad’awa Alhaji Jaheed abunda ya samu d’ansa sanadiyar accident d’in da yayi.
Fitan Dr. Mouhammad ne yasa su Abbou Jaheed d’in neman waje suka zauna, nan fa Abbou Khareem ya zaro wayarsa dake cikin aljihunsa, ya turawa Oum Ayush sak’on cewa Maleek d’in yayi accident, bayan ya tura mata sak’onne kuma ya turawa Momy da kuma Najeeb suma, daga haka baisake turawa kowa ba ya ajiye wayartasa.
Ajiyar zuciya ya sauk’e kana jikinsa amatuk’ar sanyaye, cikin ladabi da kuma sanyin murya ta yanda ya tabbatar cewa Abbou Jaheed d’in zai fahimcesa yace.
“Kayi hak’uri da abunda zan fad’a Abbou domin nasan ba lallaine yayi maka dad’i ba, saidai kuma ya zama
dole na fad’a maka cewar kwata kwata Maleek bayason auren nan, domin saboda hakanne ma yaje ya b’oye kansa awani waje, wajen da babu wanda yasani acikin mu, hak’ik’a inajin tsoron abunda zaije ya dawo bayan an d’aura aurennan, saboda akullum Maleek yana ikirarin cewa shi bazai tab’a zama da wata mace ba, burinshi akoda yaushe shine yayi rayuwarsa shi kad’ai, please Abbou Dan Allah Ajanye maganar auren nan.�
Murmushi me d’auke da dattako Abbou Jaheed yayi, tare da d’ago kansa ya kalli Fou’ad d’in.
Tabbas shi kansa ya jima da fara irin wannan tunanin, amma kuma saidai yasan ko kad’an babu alfano acikin tunanin nasa, barin cikakken Namiji me lafiya kamar Maleek babu aure sam ba daidai bane, saboda arayuwar ko wani d’a Namiji me lafiya yana buk’atar Mace, domin Mace itace duk wani ginshik’in jin dad’i, saida Mace arayuwar ko wani Namiji zai kasance acikin farinciki, tabbas Mace itace komai na rayuwar d’a Namiji, domin saida mace ne kowani Namiji zaisan wanene shi.
Ajiyar zuciya Abbou Jaheed d’in ya sauk’e, tare dayin gyaran murya, cikin tausasa kalamansa yanda yake da yak’inin cewa Fou’ad d’in zai gamsu yace.
“Bawai ina son tursasawa Maleek koyi masa auren dole bane, ina duba abunda ya dace ne, hak’ik’a burin kowani uba shine yaga ya aurar da y’ay’ansa bawai y’ay’ansa mata ba kawae harda maza, domin barin cikakken Namiji baligi agida wanda ya haura shekaru 30 ba daidai bane, matuk’ar yana da lafiya kuma yana da halin yin aure to yayi kawai, saidai kuma idan yana da hujjar cewa bazae tab’a kusantar zina ba, wannan zai iya zama yayi rayuwarsa shi kad’ai, tabbas ada bandamu akan Maleek yayi aure ko a’a ba, domin duk da cewa zuciya bata da k’ashi, amma Ina da yak’ini akansa, tabbas Ina da yak’inin cewa ban haifi fasik’i ba, hak’ik’a najima da bawa Maleek zab’i akan ya nemo matar da yakeson aura, amma yayi watsi da magana ta, haka na hak’ura na k’yalesa, nabarsa ne kuma saboda inaso naga iyaka gudun ruwansa, saboda tabbaci da nake dashi akansa, saidai kuma lokaci d’aya ya ruguza duk wata yarda ta da nake dashi akansa, nagansa da idanuna ya dawo gida acikin maye, cikin k’azamammen yanayin da duk wani Uba na duniya bazai so yaga d’ansa aciki ba, tabbas nasan Ilan maye, yakansa mutum ya aikata komai, ciki kuma harda zina, to Fou’ad ka gayamin tayaya zanbar tilon d’ana Maleek ya kasance acikin irin wannan halin? wannan dalilin shiyasa na yanke hukuncin d’aura masa aure ko da yana so ko bayaso, bankuma yi hakan don banason sa ba, saidan Ina guje masa fad’awa halaka da kuma tsinuwar Allah..�
Sosae jikin Fou’ad yayi sanyi asakamakon jin kalamai da kuma hujjar Abbou Jaheed nason yiwa Maleek aure, hak’ik’a ada yana ganin kamar cewa Abbou Jaheed d’in nason tauye Maleek ne, amma ayanzu tabbas ya fahimci komai, domin shi kansa yana da yak’inin cewa matuk’ar Maleek d’in ya fara shaye shaye to watarana maye zata iya sawa ya aikata ba daidaiba, domin sarai yasan abokinnasa yana da k’arfin sha’awa.
Baki ya bud’e da niyar cewa wani abu amma kuma saidai k’iran da ya shigo wayar Abbou Jaheed ne yasashi tsuke bakinsa.
Abbou Jaheed kuwa akaron farko kenan da yaji k’iran waya ya tsinkar masa da zuciya.
Asanyaye ya kai hannu ya d’aga wayar, duk da cewar bakuwar number ya gani amma hakan bai hanashi d’agawa ba tare da kara wayar akan kunnensa, sallaman da akayi masa ya amsa, saidai kuma jin abunda wanda ke kan wayar ke fad’ane yasashi jin wani irin matsanancin fad’uwar gaba da kuma tashin hankali me tsanani wanda har saida ya kaisa ga mik’ewa tsaye, cikin kid’ima da kuma rud’ewa ya ambaci kalmar “Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un!!!�
Batare kuma daya daidaita nutsuwarsa ba yasaki wayar tasa ta fad’i k’asa.
Hakan da yayin kuwa shiya saka hankalin su Abbou Khareem da kuma Fou’ad yayi wani irin masifaffen tashi, cikin yanayin mamaki da kuma rud’ewa suka shiga tambayarsa ko lafiya.
Kasa amsa musu yayi sai sa hannu da yayi ya dafe daedae saitin zuciyarsa, da kuma k’irjinsa dake bugawa sosae, ganin hakane yasa Fou’ad nufar wajen fridge ya d’auko goran ruwa me sanyi, mik’awa Abbou Jaheed d’in goran ruwan yayi, cikin yanayin damuwa yace.
“Abbou lafiya meyake faruwa ne?.�
Wani irin numfashi Abbou Jaheed da gaba d’aya hankalinsa baya jikinsa yayi, cikin muryarsa da ta sark’e yace.
“Maleek ne yayi accident, Khareem Maleek d’ana yayi accident, baisan inda kansa yake ba, Innalillahi Wa’inna Ilaihirraju’un, Ya Allah Kasa kada na zamo silar rasa rayuwar.......�
Cikin tashin hankali Abbou Khareem yasa hannunsa ya toshewa Yayan nasa baki, kansa ya d’an girgiza cike dason samarwa d’an uwannasa nutsuwa yace.
“Kada kace haka Yayah Allah Yana tare damu, yafi kowa sanin niya da kuma nufin dake cikin zuciyarka, awani asibiti Maleek d’in yake, mu hanzarta zuwa dansanin halin da yake ciki.�
“Nizamiyye hospital!� Abbou Jaheed d’in ya fad’a da muryarsa wanda take fitar da zallan tashin hankalin da yake ciki.
Yayinda Fou’ad kuwa tsabar shocking d’in da ya samu kansa aciki, kasa furta komai yayi, sai jikinsa dake ta faman karkarwa.
Hannun Abbou Jaheed d’in Abbou Khareem ya kamo cikin dauriya yace.
“Muje muje lokaci na k’urewa.�
Haka suka fice daga cikin falon dukansu babu wanda yake da gamsashshiyar nutsuwa atattare dashi, ko awajen tuk’in mota ma Fou’ad ne ya iya dauriyan tuk’asu, saidai kuma irin gudun da yake tsulawa yasa duk wanda ya ga motar tasu saidai ya kauce ya basu hanya.
Yanayin yanda Fou’ad d’in ke gudu kaman zai tashi sama ne yasa cikin mintuna kad’an suka iso farfajiyar asibitin.
Ko tsayawa gama daidai ta parking baiyi haka suka fito cikin tashin hankali sukayi cikin asibitin, murafen motar ma a bud’e suka barsu.
Abbou Khareem ne ya d’auki wayar Abbou Jaheed d’in ya k’ira numbern da aka k’irasu dashi d’azun dan sanin inda aka ajiye Maleek d’in.
Da yake kuma numbern na d’aya daga cikin doctors d’in asibitin da suka karb’i Maleek d’inne, yasa cikin sauk’i Doctorn ya musu kwatancen office d’insa, suna zuwa kuwa suka samu duka doctors d’in atare awaje d’aya.
Ganin irin tashin hankali da kuma damuwan dake d’auke akan fuskokinsu ne yasa Doctors d’in soma k’ok’arin kwantar musu da hankali.
Ta hanyar ce musu Maleek d’in yana nan lafiya.
“Kufad’amin idan wani abu ya samu d’ana, yana Ina ku kaini naga Maleek, shi kad’aine d’an dana Haifa aduniya Dan Allah ku fad’amin cewa Maleek yana darai bai mutu ba!!!� Abbou Jaheed ya fad’i hakan cikin tashin hankalin da yakejin kansa aciki.
Murmushi Dr.Mouhammad yayi, wanda shine babban likitan dake kan case d’in Maleek d’in, cikin son kwantarwa da Abbou Jaheed d’in hankali yace.
“Alhaji Jaheed Gwani ka kwantar da hankalinka domin d’anka bai mutu ba, domin tabbatar da hakan kuwa kana iya Bina muje kaga d’anka.�
Ae ma kafun Dr Mouhammad ya rufe bakinsa, tuni Abbou Jaheed yace.
“Muje Doctor muje nagansa.�
Shigewa gaba Dr Mouhammad yayi, yayinda su Abbou Jaheed suka rufa masa baya.
Kaitsaye d’akin da Maleek d’in ke kwance suka nufa, bud’e musu k’ofar d’akin Dr. Mouhammad yayi tare dayi musu alama akan su shiga, riga rigen shiga kuwa sukayi, yayinda kuma suna shiga suka sauk’e idanunsu akan Maleek d’in dake kwance flat akan gado, kansa nad’e da bandage.
Cikin sauri Abbou Jaheed ya k’arasa kusa da gadon, tare dasa hannayensa duka biyu ya rungume Maleek d’in, lokaci guda yaji wasu irin hawaye sun cika idanunsa, matsanancin tausayin d’annasa ne ya kamasa, hakan yasa ya d’aura kansa akirjin Maleek d’in daidai inda zuciyarsa take, wani irin ajiar zuciya me k’arfi ya sauk’e alokacin da kunnuwansa suka jiye masa sautin bugun zuciyar Maleek d’in, cikin zuciyarsa yace.
“Alhamdulillah!�
K’arasowa wajen Maleek d’in su Abbou Khareem da Fou’ad sukayi, cike da tausayin Maleek d’in suka shafa kansa dake lik’e da bandage.
Gaba d’ayansu tausayi suka bawa Dr.Mouhammad hakan yasa shi d’anyin gyaran murya cikin kulawa yace.
“Ayanzu Maleek hutu yake da buk’ata, bazan hanaku zama awajensa ba, amma saidai ku kiyaye yin surutu, sannan zai iya bud’e idanunsa any time, zuwa anjima kad’an akwai alluran da zanzo na sake yi masa, so dan Allah Ku kula sosae.�
“Insha Allah Zamu kula doctor.�
Cewar Fou’ad dake k’ok’arin maida k’wallan dake cikin idanunsa.
Kai Dr.Mouhammad ya jinjina, anutse yasa kai ya fice daga cikin d’akin, zuciyarsa cike da alhinin ta yanda zai fara fad’awa Alhaji Jaheed abunda ya samu d’ansa sanadiyar accident d’in da yayi.
Fitan Dr. Mouhammad ne yasa su Abbou Jaheed d’in neman waje suka zauna, nan fa Abbou Khareem ya zaro wayarsa dake cikin aljihunsa, ya turawa Oum Ayush sak’on cewa Maleek d’in yayi accident, bayan ya tura mata sak’onne kuma ya turawa Momy da kuma Najeeb suma, daga haka baisake turawa kowa ba ya ajiye wayartasa.