Sashe 89
Naanah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Zahra tabi bayansa tana zura hannayenta cikin aljihun rigar sanyin dake jikinta.
****
Yola, Nigeria.
Amma ta dinga kallon takardar da mamaki kafin ta ce“Allah mai iko, kaji rabo?” Abba ya ɗan yi murmushi dan har cikin zuciyarsa yaji daɗin kafin ya ce“Allah mai yanda yaso. To Alhamdulillahi Allah ya raba lafiya.”
“Idan ka fita ka sanar da Safwan ɗin.”
Abba ya yi maganar yana kallon Sultan dake tsaye gefe ɗaya ya harɗe hannayensa a ƙirji, Shiru ya yi kamar ba zai amsa ba sai kuma ya ce“Ni da ba shiga harkarsa nake ba Abba.”
“A saboda me? To ko baka shiga harkarsa wannan saƙo ne na baka ka faɗa masa Haule tana dauke da cikinsa. Saboda haƙƙinsa ne a sanar dashi, koda ya saketa kuwa.” Jiki a sanyaye Sultan ya ce
“Tom Abba, in sha Allah zan faɗa masa. Allah ya raba da lafiya” Abba ya amsa da amin sannan ya kalli Amma dake tsaye hannunta rike da takardar har sannan ya ce
“Ki je ki sanar da Fatima, Idan na fita zan faɗawa Yaya. Sai a san yanda za'a yi a faɗawa Hajiya Babba”
Amma da lokaci ɗaya taji jikinta ya yi sanyi saboda Hajiya Babba da aka ambata ta ce“tom in sha Allah zan je.”
“Yanzu ki fara zuwa ki dubata, Bari muje.”
Okay kawai ta ce sannan ta nufi hanyar bedroom ɗin Nanar, Sultan ya sauke numfashi sannan ya juya ya
Fice daga parlon Abba na biye dashi.
****
Kaddu ta yi tagumi tana kallon Anty Khadijah dake ta zazzaga masifa tunda ta shigo. Ta yi shiru tana saurarenta har sai da taga ta tsagaitan dan kanta sannan ta ce
“Ke matsalata dake rashin sanin abin da zaki yi. To sai me dan yace yana sonki? Yana son ki aurar ki ya yi? Ko zai miki dole ne? Ni ban ga abin tashin hankali anan ba wallahi tallahi. Ba dai sai kin sake zuwa wajen nasa sannan har zai faɗi wannan maganar ba? Ai ba shi kaɗai ne malami ba, Gasu nan malamai da bokaye kamar jamfa a Jos, mene ne naki na tada jijiyoyin wuya dan Allah?”
Girgiza kai Anty Khadijah ta yi kafin ta ce“Ba zaki gane ba Kaddu. Ya raina min hankali ne fa, Idan ba rainin hankali ba ina shi ina ni Khadijah? Ina yake da abin da zai aureni? Wannan abun shi ne yake ƙonamin rai wallahi.”
Kaddu ta ja tsaki sannan ta ce“Kin ji ko? To mene na ɓata ranki anan. Kawai ki bar shi mana. Ki kwantar da hankalinki zamu samo wani nan ba da jimawa ba, Yo ko maza sun ƙare me zaki yi da wannan gajan? Ai ke daga nan sai new York in sha Allahu.”
Murmushi Anty Khadijah ta yi ta nemi waje ta zauna kafin ta ce“Har naji sanyi a raina ƙawata.” Kaddu ta kashe mata ido daya sannan ta ce“Yauwa ni bana son naga kina saka kan ki cikin damuwa.” Anty Khadijah ta dauki ruwan da aka ajiye mata tun ɗazu ta balle murfin ta hau sha.
****
New York.
Basu suka dawo gidan ba sai wajen ƙarfe 7:00 na dare. Abdusammad ya sauke Noor dake hannunsa sannan ya ce“maza ki je ki shirya, Zan je nayi sallah.” To kawai ta ce tana riƙe da ledar dake hannunta, Ya ɗan kalli Zahra wadda ranta ke haɗe har sannan sai kuma ya juya ya fice daga parlon.
“Bari naje na kai wa Anty Nana nata.”
Noor ta yi maganar tana ɗaukan ɗaya daga cikin ledojin da guard ɗin ya ajiye a parlourn, wata irin tsawa Zahra ta daka mata ta ce
“Kin bar nan ko sai ci ubanki!”
Bata saba da irin haka ba dan haka ta fashe da kuka ta yar da ledar hannunta, Zahra ta yi tsaki ta wuce sama ta bar ta a wajen. Har ya dawo daga sallah bata daina kukan ba, Ya ƙarasowa wajen yana kallon ta da mamaki ya ce
“Noorie me aka miki?”
Cikin kuka ta ce“Ummi ta min tsawa Abbie, Kaina zafi yake min.” Ta ƙare maganar tana sake rushewa da wani sabon kukan, Sosai ransa ya ɓaci dan ko da wasa baya son yaga an ɓatawa yaro rai. Ya durƙusa daidai tsayinta yana goge mata hawayen kafin ya ce
“Shikenan ya isa daina kukan kinji, Ke da zaki ci gaba da zuwa school gobe?”
Tuni ta manta da batun tsawar ta washe baki tana dariya ta ce“Abbie ina son naga Afeefa.”
Murmushi ya yi ya ja kumatunta ya ce“Okay zaki ganta ai, Maza je ki ɗaki.” Sakin hannunsa ta yi ta nufi saman da gudu, Ya bita da kallo kafin ya miƙe tsaye. Kallon apartment ɗin Zahran ya yi, Kamar ya shige sai kuma ya nufi sama. Zaune ya sameta gefen gado tana danna wayarta ya ƙarasa ciki ya tsaya a jikin madubi hannayensa harɗe a ƙirjinsa ya ce
“Akan me zaki dinga yiwa yarinya ƙarama tsawa? Me ta yi miki?.”
Ɗago kanta ta yi da kalleshi sai kuma ta sake sunkuyar da kai tana ci gaba da danna wayarta. Ba ƙaramin mamaki ta bashi ba, dan Zahra bata saba haka ba, Ya yi shiru yana kallon ta kafin ya sake cewa
“Zahra dake nake magana fa...”
Miƙewa tsaye ta yi a fusace tana kallon sa ta ce“To bani da ikon yi mata tsawa ne? Ko ka manta nima ƴata ce? Laifin ta min shiyasa nayi mata!” ta ƙare maganar a mugun fusace. Shiru ya yi yana kallon ta, ganin haka ya sanya ta ɗauki wayarta ta fice daga ɗakin kamar zata tashi sama. Ya daɗe tsaye a wajen yana mamakin abin da ta yi, Can kuma ya sauke numfashi ya juya ya bar ɗakin shima.
Wajejen ƙarfe 8:00 na dare ya fito sanye da ƙananun kaya, Kai tsaye kuma apartment ɗin Nana ya nufa. Kwance ya hangeta tsakiyar gado sai juyi take gaba ɗaya ta yamutse bedsheet ɗin, Ya ƙarasa ciki yana kallonta ya ce
“Nana mene haka?”
Jin bata bashi amsa ba ya sanya shi hawa kan gadon, hannunsa ɗaya ya sanya ya jawota. Kamar jira take ta saki wani marayan kuka tana riƙe shi, Da mamaki yake kallon ta, Ya janyota jikinsa gaba ɗaya yana kallon fuskarta ya ce
“Nana mene ne? Meke damunki?”
Ya yi tambayar yana taɓa jikinta, Zafi yaji sosai dan haka ya sake cewa“Baki da lafiya? Mene yake miki ciwo.?”
Cikin shassheƙar kuka ta ce“Uncle ka kaini wajen Abbana, ni gida zani.”
“To zan kai ki, Yanzu faɗa min meke damunki?”
Rufe idanunta ta yi hawaye na zubowa ta cikinsu ta ce“cikina ne yake min ciwo.”
Girgiza kansa ya yi ya ce“Sannu to, kwanta ina zuwa.” Ya kwantar da ita sannan ya miƙe ya fice daga ɗakin, Tashi ta yi da kyar ta sakko daga kan gadon, Ta yi durƙusa a wajen ta ɗora kanta a gefen gadon kamar me kneel down. Har ya dawo tana haka, Ya ajiye drip ɗin hannunsa da allurar ya tsaya yana kallon ta, can kuma ya ce
“Ke cikinki ke ciwo ko mararki?”
Kamar daga sama taji tambayar tasa, Ta ɗago idanunta da kyar tana kallon sa. Ƙarasowa wajen ya yi ya zauna gefen gadon ya ɗagota ya zaunar da ita a jikinsa ya ce
“Mararki ne ke ciwo ko cikin ki?”
“Marata...”
Ta ce cikin shessheƙar kuka. Dungure mata kai ya yi kafin ya ce“shi ne zaki ce min cikin ki? Me ki ke ɓoyewa?” Ita dai bata iya magana ba saboda ciwon da yaci ƙarfinta. Ya kwantar da ita akan gadon sannan ya tashi ya fice, After 5mins ya dawo hannunsa riƙe da mug da wata injection, Ya ajiye allurar kan waɗancan sannan ya zauna kusa da ita, Ɗagota ya yi da hannu ɗaya ya jinginata da jikinsa ya ce
“Oya drink it.”
“Ni ba zan iya sha ba.”
Ta yi maganar tana yarfe hannu, Haɗe rai ya yi ya ce“zan makeki, drink it my friend!” kuka ta fara yi a hankali, Ya kai mata mug ɗin bakinta, Dakyar ta buɗe bakin ta fara sha a hankali. Ko rabin shayin bata sha ba ta ɗauke kanta, Ya sake miƙo mata fuskarsa a haɗe ya ce
“Yaushe na fara wasa da ke?”
Toshe bakinta ta yi tana girgiza masa kai, Ya janye hannun daga kan bakinta kamar jira take ta fara wanke shin da amai. Shiru ya yi yana kallon ta ganin yanda take kwarara aman har da na abincin da taci ɗazu, gaba ɗaya ta ɓata masa jikinsa, ta ɗora kanta akan ƙirjinsa tana sauke numfashi idanunta a lumshe. Hannunsa ya sanya ya dafa kanta a sanyaye ya ce
“Sannu.”
Bata ce komai ba, Ya tashi da ita a jikinsa ya nufi toilet, Zaunar da ita ya yi sannan ya fara ƙoƙarin zare mata kayan jikinta. Ta yi saurin riƙe hannunsa tana kuka a hankali, Haɗe rai ya yi ya doke hannunta sannan ya ƙarasa zare mata rigar dake jikinta. Wata irin ajiyar zuciya suka sauke a tare, Ya yi saurin ɗauke kansa daga kan ƙirjinta wanda lokaci ɗaya yaji yana neman tada masa da hankali, sam bai yi tunanin yarinyar ta kai haka ba. Ya kawar da tunanin daga ransa ya miƙar da ita tsaye, Da kansa ya yi mata wankan sannan ya saka mata bathrobe, Ta sake kwantowa jikinsa tana maƙalƙalesa. Ɗaukanta ya yi ya fice daga banɗakin, Ya zaunar da ita kan doguwar Kujerar dake gefen gadon sannan ya yaye bedsheet ɗin ya naɗeshi ya kai toilet ya saka cikin washing machine. Bayan ya fito ya dauƙo sabon bedsheet ya shimfiɗa akan gadon sannan ya ɗaukota ya kwantar da ita akai, Ta dunƙule jikinta waje ɗaya saboda sanyin da take ji, Press ɗinta ya buɗe ya dauko mata wata yar ƙaramar riga mara nauyi, Ya haɗo mata da pant da kuma pad. Ajiyewa ya yi a gefen gadon ya fara ƙoƙarin jawota, saurin riƙe hannunsa ta yi kamar zata yi kuka ta ce
“Zan yi da kaina uncle.”
****
Yola, Nigeria.
Amma ta dinga kallon takardar da mamaki kafin ta ce“Allah mai iko, kaji rabo?” Abba ya ɗan yi murmushi dan har cikin zuciyarsa yaji daɗin kafin ya ce“Allah mai yanda yaso. To Alhamdulillahi Allah ya raba lafiya.”
“Idan ka fita ka sanar da Safwan ɗin.”
Abba ya yi maganar yana kallon Sultan dake tsaye gefe ɗaya ya harɗe hannayensa a ƙirji, Shiru ya yi kamar ba zai amsa ba sai kuma ya ce“Ni da ba shiga harkarsa nake ba Abba.”
“A saboda me? To ko baka shiga harkarsa wannan saƙo ne na baka ka faɗa masa Haule tana dauke da cikinsa. Saboda haƙƙinsa ne a sanar dashi, koda ya saketa kuwa.” Jiki a sanyaye Sultan ya ce
“Tom Abba, in sha Allah zan faɗa masa. Allah ya raba da lafiya” Abba ya amsa da amin sannan ya kalli Amma dake tsaye hannunta rike da takardar har sannan ya ce
“Ki je ki sanar da Fatima, Idan na fita zan faɗawa Yaya. Sai a san yanda za'a yi a faɗawa Hajiya Babba”
Amma da lokaci ɗaya taji jikinta ya yi sanyi saboda Hajiya Babba da aka ambata ta ce“tom in sha Allah zan je.”
“Yanzu ki fara zuwa ki dubata, Bari muje.”
Okay kawai ta ce sannan ta nufi hanyar bedroom ɗin Nanar, Sultan ya sauke numfashi sannan ya juya ya
Fice daga parlon Abba na biye dashi.
****
Kaddu ta yi tagumi tana kallon Anty Khadijah dake ta zazzaga masifa tunda ta shigo. Ta yi shiru tana saurarenta har sai da taga ta tsagaitan dan kanta sannan ta ce
“Ke matsalata dake rashin sanin abin da zaki yi. To sai me dan yace yana sonki? Yana son ki aurar ki ya yi? Ko zai miki dole ne? Ni ban ga abin tashin hankali anan ba wallahi tallahi. Ba dai sai kin sake zuwa wajen nasa sannan har zai faɗi wannan maganar ba? Ai ba shi kaɗai ne malami ba, Gasu nan malamai da bokaye kamar jamfa a Jos, mene ne naki na tada jijiyoyin wuya dan Allah?”
Girgiza kai Anty Khadijah ta yi kafin ta ce“Ba zaki gane ba Kaddu. Ya raina min hankali ne fa, Idan ba rainin hankali ba ina shi ina ni Khadijah? Ina yake da abin da zai aureni? Wannan abun shi ne yake ƙonamin rai wallahi.”
Kaddu ta ja tsaki sannan ta ce“Kin ji ko? To mene na ɓata ranki anan. Kawai ki bar shi mana. Ki kwantar da hankalinki zamu samo wani nan ba da jimawa ba, Yo ko maza sun ƙare me zaki yi da wannan gajan? Ai ke daga nan sai new York in sha Allahu.”
Murmushi Anty Khadijah ta yi ta nemi waje ta zauna kafin ta ce“Har naji sanyi a raina ƙawata.” Kaddu ta kashe mata ido daya sannan ta ce“Yauwa ni bana son naga kina saka kan ki cikin damuwa.” Anty Khadijah ta dauki ruwan da aka ajiye mata tun ɗazu ta balle murfin ta hau sha.
****
New York.
Basu suka dawo gidan ba sai wajen ƙarfe 7:00 na dare. Abdusammad ya sauke Noor dake hannunsa sannan ya ce“maza ki je ki shirya, Zan je nayi sallah.” To kawai ta ce tana riƙe da ledar dake hannunta, Ya ɗan kalli Zahra wadda ranta ke haɗe har sannan sai kuma ya juya ya fice daga parlon.
“Bari naje na kai wa Anty Nana nata.”
Noor ta yi maganar tana ɗaukan ɗaya daga cikin ledojin da guard ɗin ya ajiye a parlourn, wata irin tsawa Zahra ta daka mata ta ce
“Kin bar nan ko sai ci ubanki!”
Bata saba da irin haka ba dan haka ta fashe da kuka ta yar da ledar hannunta, Zahra ta yi tsaki ta wuce sama ta bar ta a wajen. Har ya dawo daga sallah bata daina kukan ba, Ya ƙarasowa wajen yana kallon ta da mamaki ya ce
“Noorie me aka miki?”
Cikin kuka ta ce“Ummi ta min tsawa Abbie, Kaina zafi yake min.” Ta ƙare maganar tana sake rushewa da wani sabon kukan, Sosai ransa ya ɓaci dan ko da wasa baya son yaga an ɓatawa yaro rai. Ya durƙusa daidai tsayinta yana goge mata hawayen kafin ya ce
“Shikenan ya isa daina kukan kinji, Ke da zaki ci gaba da zuwa school gobe?”
Tuni ta manta da batun tsawar ta washe baki tana dariya ta ce“Abbie ina son naga Afeefa.”
Murmushi ya yi ya ja kumatunta ya ce“Okay zaki ganta ai, Maza je ki ɗaki.” Sakin hannunsa ta yi ta nufi saman da gudu, Ya bita da kallo kafin ya miƙe tsaye. Kallon apartment ɗin Zahran ya yi, Kamar ya shige sai kuma ya nufi sama. Zaune ya sameta gefen gado tana danna wayarta ya ƙarasa ciki ya tsaya a jikin madubi hannayensa harɗe a ƙirjinsa ya ce
“Akan me zaki dinga yiwa yarinya ƙarama tsawa? Me ta yi miki?.”
Ɗago kanta ta yi da kalleshi sai kuma ta sake sunkuyar da kai tana ci gaba da danna wayarta. Ba ƙaramin mamaki ta bashi ba, dan Zahra bata saba haka ba, Ya yi shiru yana kallon ta kafin ya sake cewa
“Zahra dake nake magana fa...”
Miƙewa tsaye ta yi a fusace tana kallon sa ta ce“To bani da ikon yi mata tsawa ne? Ko ka manta nima ƴata ce? Laifin ta min shiyasa nayi mata!” ta ƙare maganar a mugun fusace. Shiru ya yi yana kallon ta, ganin haka ya sanya ta ɗauki wayarta ta fice daga ɗakin kamar zata tashi sama. Ya daɗe tsaye a wajen yana mamakin abin da ta yi, Can kuma ya sauke numfashi ya juya ya bar ɗakin shima.
Wajejen ƙarfe 8:00 na dare ya fito sanye da ƙananun kaya, Kai tsaye kuma apartment ɗin Nana ya nufa. Kwance ya hangeta tsakiyar gado sai juyi take gaba ɗaya ta yamutse bedsheet ɗin, Ya ƙarasa ciki yana kallonta ya ce
“Nana mene haka?”
Jin bata bashi amsa ba ya sanya shi hawa kan gadon, hannunsa ɗaya ya sanya ya jawota. Kamar jira take ta saki wani marayan kuka tana riƙe shi, Da mamaki yake kallon ta, Ya janyota jikinsa gaba ɗaya yana kallon fuskarta ya ce
“Nana mene ne? Meke damunki?”
Ya yi tambayar yana taɓa jikinta, Zafi yaji sosai dan haka ya sake cewa“Baki da lafiya? Mene yake miki ciwo.?”
Cikin shassheƙar kuka ta ce“Uncle ka kaini wajen Abbana, ni gida zani.”
“To zan kai ki, Yanzu faɗa min meke damunki?”
Rufe idanunta ta yi hawaye na zubowa ta cikinsu ta ce“cikina ne yake min ciwo.”
Girgiza kansa ya yi ya ce“Sannu to, kwanta ina zuwa.” Ya kwantar da ita sannan ya miƙe ya fice daga ɗakin, Tashi ta yi da kyar ta sakko daga kan gadon, Ta yi durƙusa a wajen ta ɗora kanta a gefen gadon kamar me kneel down. Har ya dawo tana haka, Ya ajiye drip ɗin hannunsa da allurar ya tsaya yana kallon ta, can kuma ya ce
“Ke cikinki ke ciwo ko mararki?”
Kamar daga sama taji tambayar tasa, Ta ɗago idanunta da kyar tana kallon sa. Ƙarasowa wajen ya yi ya zauna gefen gadon ya ɗagota ya zaunar da ita a jikinsa ya ce
“Mararki ne ke ciwo ko cikin ki?”
“Marata...”
Ta ce cikin shessheƙar kuka. Dungure mata kai ya yi kafin ya ce“shi ne zaki ce min cikin ki? Me ki ke ɓoyewa?” Ita dai bata iya magana ba saboda ciwon da yaci ƙarfinta. Ya kwantar da ita akan gadon sannan ya tashi ya fice, After 5mins ya dawo hannunsa riƙe da mug da wata injection, Ya ajiye allurar kan waɗancan sannan ya zauna kusa da ita, Ɗagota ya yi da hannu ɗaya ya jinginata da jikinsa ya ce
“Oya drink it.”
“Ni ba zan iya sha ba.”
Ta yi maganar tana yarfe hannu, Haɗe rai ya yi ya ce“zan makeki, drink it my friend!” kuka ta fara yi a hankali, Ya kai mata mug ɗin bakinta, Dakyar ta buɗe bakin ta fara sha a hankali. Ko rabin shayin bata sha ba ta ɗauke kanta, Ya sake miƙo mata fuskarsa a haɗe ya ce
“Yaushe na fara wasa da ke?”
Toshe bakinta ta yi tana girgiza masa kai, Ya janye hannun daga kan bakinta kamar jira take ta fara wanke shin da amai. Shiru ya yi yana kallon ta ganin yanda take kwarara aman har da na abincin da taci ɗazu, gaba ɗaya ta ɓata masa jikinsa, ta ɗora kanta akan ƙirjinsa tana sauke numfashi idanunta a lumshe. Hannunsa ya sanya ya dafa kanta a sanyaye ya ce
“Sannu.”
Bata ce komai ba, Ya tashi da ita a jikinsa ya nufi toilet, Zaunar da ita ya yi sannan ya fara ƙoƙarin zare mata kayan jikinta. Ta yi saurin riƙe hannunsa tana kuka a hankali, Haɗe rai ya yi ya doke hannunta sannan ya ƙarasa zare mata rigar dake jikinta. Wata irin ajiyar zuciya suka sauke a tare, Ya yi saurin ɗauke kansa daga kan ƙirjinta wanda lokaci ɗaya yaji yana neman tada masa da hankali, sam bai yi tunanin yarinyar ta kai haka ba. Ya kawar da tunanin daga ransa ya miƙar da ita tsaye, Da kansa ya yi mata wankan sannan ya saka mata bathrobe, Ta sake kwantowa jikinsa tana maƙalƙalesa. Ɗaukanta ya yi ya fice daga banɗakin, Ya zaunar da ita kan doguwar Kujerar dake gefen gadon sannan ya yaye bedsheet ɗin ya naɗeshi ya kai toilet ya saka cikin washing machine. Bayan ya fito ya dauƙo sabon bedsheet ya shimfiɗa akan gadon sannan ya ɗaukota ya kwantar da ita akai, Ta dunƙule jikinta waje ɗaya saboda sanyin da take ji, Press ɗinta ya buɗe ya dauko mata wata yar ƙaramar riga mara nauyi, Ya haɗo mata da pant da kuma pad. Ajiyewa ya yi a gefen gadon ya fara ƙoƙarin jawota, saurin riƙe hannunsa ta yi kamar zata yi kuka ta ce
“Zan yi da kaina uncle.”