Sashe 61
Naanah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Dakyar ta buɗe kumburarrun Idanunta, ta ɗan zame duvet ɗin daga kanta tana kallonsa, idanunta daya sauka kan Abdusammad ne ya sanya ta fara ƙoƙarin tashi, zama Aliyu ya yi gefenta ya ɗagota ya jinginata da jikinsa, Abdusammad ya taɓe baki yana kallonta ya ce
“Ina Nana take?!”
“Nana kuma? Ya za'a yi ta san inda Nana take Buddy?”
Aliyu ya tambaye shi da mamaki. A tsawace Abdusammad ya ce
“Nace ina Nana take!”
08106608363
Nanameera.*🌹 NAANAH 🌹*
Arewabooks@Nanameera08
Wattpad@Nanameera08
Page 37.
Sunkuyar da kanta ta yi hawaye na biyo kuncinta, Ya gyaɗa kansa sai kuma ya ƙara taku ɗaya zuwa gabansu yana ware idanunsa sosai akanta ya ce
“don't ever let me ask you again! Ina Nana take?”
Ganin yanda ta firgice yasa Aliyu dafata ya ɗago yana kallonsa ya ce
“Haba Buddy she's not feeling well ka barta mana dan Allah” a fusace shima ya ce
“to ni ina ruwana? Mene ne nawa da rashin lafiyarta?”
Aliyu shiru ya yi yana kallonsa ganin yanda ya haɗe rai. Ya maida idanunsa kan Maimoon cikin sanyin murya ya ce“pls idan kin san inda take talk to him” sake fashewa ta yi da kuka tana maƙalewa jikin Aliyu ta ce
“wallahi uncle ban sani ba, ban san inda take ba!”
Wani irin kallon kin zama mahaukaciya Abdusammad ya dinga mata, can kuma ya gyaɗa kansa ya ce“okay!”
Daga haka ya juya ya fice daga ɗakin rai ɓace.
Aliyu ya bishi da kallo sai kuma ya maida idanunsa kan Maimoon, Ya shafa kanta a hankali ya ce“sorry ki daina kukan, ya tafi ai” gyaɗa kanta kawai ta yi ya taimaka mata ta kwanta dan har sannan zazzaɓi ne rau a jikinta.
Abdusammad na fita apartment ɗinsa ya nufa, ya samu Zahra zaune a parlon ta zuba uban tagumi kamar koda yaushe. Kallo ɗaya ya yi mata sai kuma ya haye sama dan ransa a ɓace yake, ta bishi da idanu kawai dan tasan kota kulashi ba amsawa zai yi ba. Tana nan zaune har after 15mins sai kuma ta tashi tabi bayansa, zaune ta sameshi gefen gado ya jingina da fuskar gadon idanunsa a rufe. Ta yi shiru tana kallonsa kafin taja jikinta ta ƙarasa inda yake a sanyaye, ta zauna gefen gadon ba tare da tace komai ba. Sun ɗauki lokaci mai tsayi a haka kafin ta ƙara matsawa kusa dashi, a hankali ta ɗora kanta akan faffaɗan ƙirjinsa. Ko motsi bai yi ba, ballantana ta saka ran zai kulata, dan ta tabbata ba bacci yake ba. A hankali ta zura hannayenta duk biyun a bayansa ta riƙe shi ƙam sai kuma ta fashe da kuka kamar ƙaramar yarinya. Duk yanda ya so yin shiru kasawa ya yi dan sam baya son jin kukan mace, ya ware idanunsa akanta kafin a hankali ya ɗagota yana kallonta da birkitattun idanunsa ya ce
“mene ne?”
Cikin kuka ta ce
“Doctor bana jin daɗi ne kawai. Dan Allah mu koma US”
Numfasawa ya yi kafin ya ce“in sha Allah zamu koma but not now”
“amma meyasa?”
Ta tambaya da damuwa sosai akan fuskarta. Sai da ya janyeta daga jikinsa ya miƙe tsaye yana gyara rigar jikinsa ya ce“cause i have alot to do” daga haka ya nufi toilet. Da idanu kawai Zahra ta bi shi sai kuma ta dauke kanta, ta zame jikinta ta kwanta akan gadon ta lumshe idanu..
Kusan 3 weeks kenan, abubuwa sun fara shigewa, sai dai wanda aka yiwa shi ne mai manta ba, duk matan sun tare gidan mazajensu har da Siyama wadda take ta faman gigi. Amma har sannan ta kasa daina zancen Nana, kullum bata da magana sai tata, koda yaushe cikin son ganinta take. Sai dai koda wasa bata isa tayi maganarta gaban Abba ba indai ba tana son ɓacin ransa bane, ko sunan Nana baya son yaji an ambata. Duk da ƙasan zuciyarsa bai manta da ita amma sam yaƙi bari mutane su gane hakan. A ɓangaren Maimoon kam kusan kullum cikin kuka take, dan har cikin zuciyarta bata san inda Nanan take ba, sam tunaninta bai bata ta tambayeta inda zata je a ranar. Gashi ta kasa samunta a waya, hasalima kullum ta kira wayar a kashe suke ce mata, wannan yasa har sannan ta kasa sakar jikinta duk yanda Aliyu ke nuna mata so da ƙauna.
****
Wasu ƙattin maza ne tsaye su huɗu, sun yi masa ƙawanya kowannesu hannunsa riƙe da bindiga sai zazzare idanu suke yi. Kasancewar fuskarsa a rufe take da wani abu mai kamada buhu ya sanya bai san su wane ba, dan ko numfashi baya samun damar yi. After 5mins aka buɗe ƙofar, nan take duk suka juyo suna kallonsa, cike da girmamawa kuma suka durƙusa a tare suka gaishe shi. Ya gyaɗa musu kai sannan ya ƙarasa gabansa ya janye buhun. Wani irin jan numfashi Junaid ya yi, ya sauke shi a wahalce fuskarsa ta yi jajur dan ba ƙaramin duka yasha ba, gaba ɗaya sun sauya masa kammani. Bai ƙarasa dawowa daidai ba yaji ɗaya daga cikinsu ya cafki maƙogaronsa cikin ƙaraji ya ce
“Hey ina yarinyar take?”
Kasa magana ya yi dan bai bashi damar haka ba, ganin yana neman rasa rayuwarsa ya sanya ya ce
“Stop!”
Cak ya tsaya ya kuma zare hannunsa, ya umarce su da su yi baya, kamar jira suke kuwa suka koma bayan. Ya dafashi yana zare face mask ɗinsa da ɗayan hannun, nan take kyakkyawar fuskarsa ta bayyana, gyara tsaiwarsa ya yi kafin a sanyaye ya ce
“Ina Nana take?”
Ganin yanda ya yi magana a dake ya sanya Junaid haɗiyar yawu, Ya girgiza kansa yana kallonsa cikin tashin hankali ya ce
“Nana kuma? Me ya samu Nana? Dan Allah kada ka cemin wani abun ya sameta”
Wani irin duka ya kai masa da ƙasan bindiga nan take haƙoransa uku na gaba suka zube, Ya dafe bakin yana jin wata irin azaba na kawo masa ziyara. Bai bari ya wartsake ba ya shaƙe wuyansa wannan karon cikin ɓacin rai ya ce
“Ina take? Ina ka kai ta?”
Girgiza kai Junaid kawai yake, dan sam bai san abin da yake magana akai ba. Ya dinga wani irin numfashi dakyar kamar zai mutu, sakinsa ya yi yana ɗauke kai ya ce
“kar ka bari na sake tambayarka tana ina?”
Junaid da azaba ke neman hallaka shi ya fashe da kuka jini na zubowa daga bakinsa ya ce
“Wallahi ban san me ku ke magana akai ba, Mene ne ya samu Nana? Dan Allah kada ku cemin wani abun ya sameta”
Ɗauke kai Abdusammad ya yi yana murmushi ganin yanda yake neman raina masa hankali. Junaid ya bishi da idanu yana fatan ya sanar dashi abin da ke faruwa.
Cikin wani irin zafin nama ya dawo gabansa ya ɗora hancin bindigar hannunsa a tsakiyar kansa yana kallonsa rai ɓace ya ce
“ina Nana take?”
Girgiza kai kawai Junaid yake, jikinsa sai rawa yake. Ya sake matse kunamar bindigar ya ce
“ka faɗa min ko na harbeka, kuma idan na kasheka na kashe banza!”
Bakinsa na rawa ya ce
“Waam... wallahi, wallahi ban sani ba, ban san Nana ta bar gidan nan ba”
Shiru ya yi yana kallonsa da ɗan mamaki, dan ya lura babu ƙarya a maganarsa ya ɗauke bindigar ya miƙewa ɗaya daga cikinsu sannan ya zaro hotunan da suke aljihunsa, buɗesu ya yi ya kara masa a fuska yanda zai gani ya ce
“ba kai bane wannan?”
Da mamaki Junaid ke kallonsa sai kuma ya kai hannu zai kwace hoton yana faɗin “ina ka samu wadannan hotunan?”wani banzan kallo Abdusammad ya watsa masa sannan ya mayar da hotunan envelope ɗin ya ce“ina Nana take?”
Junaid ya sake girgiza kansa a karo na barkatai kafin ya ce“wallahi ban sani ba! Ban san ma bata gida ba, yaushe ta bar gida?”
Kujera yaja ya zauna yana kallonsa sosai fuskarsa a haɗe babu alamar wasa ya ce“tell me ina ka haɗu da ita? And kada ka ɓoye min koda abu guda ɗaya ne” Junaid ya dinga kallonsa sai kuma ya sunkuyar da kansa, Da hannu ya yi musu alama dasu dawo suka dawo kansa suka tsaya kowanne yana riƙe da bindigarsa har sannan. A hankali ya daga idanunsa yana kallonsa sai kuma ya sake saukewa, kusan 2mins kafin ya buɗe baki ya fara bashi labarin duk abin da ya faru daga farko har zuwa ƙarshe.
Ban da kallonsa babu abin da Abdusammad ke yi, Junaid da ke kuka kamar ransa zai fita ya sake cewa“wallahi ban yi da niyyar cutar da Nana ba, sam bana nufinta da mugun abu”
Numfasawa Abdusammad ya yi yana saurarensa har sannan, gaba ɗaya kansa ya kulle, ya lura babu ƙarya a cikin zantukan Junaid. Ya tashi tsaye yana kallonsa ya ce
“baka nufinta da sharri amma ka iya ɗaukanta hotuna har kake mata barazana? Sannan baka nufinta da sharri har ka iya cutar da ita duk da cewa ita da zuciya ɗaya taje wajenka? Haka ne baka nufinta da sharri?”
Girgiza kai Junaid ya yi yana jin wanda irin ɗaci a ransa ya ce“wallahi bana nufin Nana da sharri, na san ban kyauta ba, kuma ban yi dai-dai ba. Amma nima zugar aboki ce ta yi tasiri akaina, sai bayan dana aikata abun sannan nafara danasani. Wallahi ban taɓa tunanin fitar da hotunan Nana ba, hasalima bayan wanda na tura mata bani da wasu, dan na goge ba zan juri kalla ba. Kawai na so yin amfani da hakan ne wajen sakata ta yi duk mai yiwuwa kar ta ga an rabamu.”
Ya sauke numfashi hawaye na gangarowa kan fuskarsa ya ci gaba da faɗin “sai dai hakan bai yi wani amfani ba. Na rasata, gefe guda kuma na haifar mata da baƙin ciki wanda zata dade tana tunawa, a yanzu banida wani buri daya shige naga Nana domin na nemi yafiyarta duk da na san ban cancanci hakan ba. Ta ɗaukeni masoyi na gaskiya ni kuma na cutar da ita, Dan Allah ina zan ga Nanaa?...”
Ya ƙare maganar yana sakin wani raunataccen kuka. Shiru Abdusammad ya yi can kuma ya furzar da iska daga bakinsa ya ce“kana son ka ce min baka san inda take ba?”
“Ina Nana take?!”
“Nana kuma? Ya za'a yi ta san inda Nana take Buddy?”
Aliyu ya tambaye shi da mamaki. A tsawace Abdusammad ya ce
“Nace ina Nana take!”
08106608363
Nanameera.*🌹 NAANAH 🌹*
Arewabooks@Nanameera08
Wattpad@Nanameera08
Page 37.
Sunkuyar da kanta ta yi hawaye na biyo kuncinta, Ya gyaɗa kansa sai kuma ya ƙara taku ɗaya zuwa gabansu yana ware idanunsa sosai akanta ya ce
“don't ever let me ask you again! Ina Nana take?”
Ganin yanda ta firgice yasa Aliyu dafata ya ɗago yana kallonsa ya ce
“Haba Buddy she's not feeling well ka barta mana dan Allah” a fusace shima ya ce
“to ni ina ruwana? Mene ne nawa da rashin lafiyarta?”
Aliyu shiru ya yi yana kallonsa ganin yanda ya haɗe rai. Ya maida idanunsa kan Maimoon cikin sanyin murya ya ce“pls idan kin san inda take talk to him” sake fashewa ta yi da kuka tana maƙalewa jikin Aliyu ta ce
“wallahi uncle ban sani ba, ban san inda take ba!”
Wani irin kallon kin zama mahaukaciya Abdusammad ya dinga mata, can kuma ya gyaɗa kansa ya ce“okay!”
Daga haka ya juya ya fice daga ɗakin rai ɓace.
Aliyu ya bishi da kallo sai kuma ya maida idanunsa kan Maimoon, Ya shafa kanta a hankali ya ce“sorry ki daina kukan, ya tafi ai” gyaɗa kanta kawai ta yi ya taimaka mata ta kwanta dan har sannan zazzaɓi ne rau a jikinta.
Abdusammad na fita apartment ɗinsa ya nufa, ya samu Zahra zaune a parlon ta zuba uban tagumi kamar koda yaushe. Kallo ɗaya ya yi mata sai kuma ya haye sama dan ransa a ɓace yake, ta bishi da idanu kawai dan tasan kota kulashi ba amsawa zai yi ba. Tana nan zaune har after 15mins sai kuma ta tashi tabi bayansa, zaune ta sameshi gefen gado ya jingina da fuskar gadon idanunsa a rufe. Ta yi shiru tana kallonsa kafin taja jikinta ta ƙarasa inda yake a sanyaye, ta zauna gefen gadon ba tare da tace komai ba. Sun ɗauki lokaci mai tsayi a haka kafin ta ƙara matsawa kusa dashi, a hankali ta ɗora kanta akan faffaɗan ƙirjinsa. Ko motsi bai yi ba, ballantana ta saka ran zai kulata, dan ta tabbata ba bacci yake ba. A hankali ta zura hannayenta duk biyun a bayansa ta riƙe shi ƙam sai kuma ta fashe da kuka kamar ƙaramar yarinya. Duk yanda ya so yin shiru kasawa ya yi dan sam baya son jin kukan mace, ya ware idanunsa akanta kafin a hankali ya ɗagota yana kallonta da birkitattun idanunsa ya ce
“mene ne?”
Cikin kuka ta ce
“Doctor bana jin daɗi ne kawai. Dan Allah mu koma US”
Numfasawa ya yi kafin ya ce“in sha Allah zamu koma but not now”
“amma meyasa?”
Ta tambaya da damuwa sosai akan fuskarta. Sai da ya janyeta daga jikinsa ya miƙe tsaye yana gyara rigar jikinsa ya ce“cause i have alot to do” daga haka ya nufi toilet. Da idanu kawai Zahra ta bi shi sai kuma ta dauke kanta, ta zame jikinta ta kwanta akan gadon ta lumshe idanu..
Kusan 3 weeks kenan, abubuwa sun fara shigewa, sai dai wanda aka yiwa shi ne mai manta ba, duk matan sun tare gidan mazajensu har da Siyama wadda take ta faman gigi. Amma har sannan ta kasa daina zancen Nana, kullum bata da magana sai tata, koda yaushe cikin son ganinta take. Sai dai koda wasa bata isa tayi maganarta gaban Abba ba indai ba tana son ɓacin ransa bane, ko sunan Nana baya son yaji an ambata. Duk da ƙasan zuciyarsa bai manta da ita amma sam yaƙi bari mutane su gane hakan. A ɓangaren Maimoon kam kusan kullum cikin kuka take, dan har cikin zuciyarta bata san inda Nanan take ba, sam tunaninta bai bata ta tambayeta inda zata je a ranar. Gashi ta kasa samunta a waya, hasalima kullum ta kira wayar a kashe suke ce mata, wannan yasa har sannan ta kasa sakar jikinta duk yanda Aliyu ke nuna mata so da ƙauna.
****
Wasu ƙattin maza ne tsaye su huɗu, sun yi masa ƙawanya kowannesu hannunsa riƙe da bindiga sai zazzare idanu suke yi. Kasancewar fuskarsa a rufe take da wani abu mai kamada buhu ya sanya bai san su wane ba, dan ko numfashi baya samun damar yi. After 5mins aka buɗe ƙofar, nan take duk suka juyo suna kallonsa, cike da girmamawa kuma suka durƙusa a tare suka gaishe shi. Ya gyaɗa musu kai sannan ya ƙarasa gabansa ya janye buhun. Wani irin jan numfashi Junaid ya yi, ya sauke shi a wahalce fuskarsa ta yi jajur dan ba ƙaramin duka yasha ba, gaba ɗaya sun sauya masa kammani. Bai ƙarasa dawowa daidai ba yaji ɗaya daga cikinsu ya cafki maƙogaronsa cikin ƙaraji ya ce
“Hey ina yarinyar take?”
Kasa magana ya yi dan bai bashi damar haka ba, ganin yana neman rasa rayuwarsa ya sanya ya ce
“Stop!”
Cak ya tsaya ya kuma zare hannunsa, ya umarce su da su yi baya, kamar jira suke kuwa suka koma bayan. Ya dafashi yana zare face mask ɗinsa da ɗayan hannun, nan take kyakkyawar fuskarsa ta bayyana, gyara tsaiwarsa ya yi kafin a sanyaye ya ce
“Ina Nana take?”
Ganin yanda ya yi magana a dake ya sanya Junaid haɗiyar yawu, Ya girgiza kansa yana kallonsa cikin tashin hankali ya ce
“Nana kuma? Me ya samu Nana? Dan Allah kada ka cemin wani abun ya sameta”
Wani irin duka ya kai masa da ƙasan bindiga nan take haƙoransa uku na gaba suka zube, Ya dafe bakin yana jin wata irin azaba na kawo masa ziyara. Bai bari ya wartsake ba ya shaƙe wuyansa wannan karon cikin ɓacin rai ya ce
“Ina take? Ina ka kai ta?”
Girgiza kai Junaid kawai yake, dan sam bai san abin da yake magana akai ba. Ya dinga wani irin numfashi dakyar kamar zai mutu, sakinsa ya yi yana ɗauke kai ya ce
“kar ka bari na sake tambayarka tana ina?”
Junaid da azaba ke neman hallaka shi ya fashe da kuka jini na zubowa daga bakinsa ya ce
“Wallahi ban san me ku ke magana akai ba, Mene ne ya samu Nana? Dan Allah kada ku cemin wani abun ya sameta”
Ɗauke kai Abdusammad ya yi yana murmushi ganin yanda yake neman raina masa hankali. Junaid ya bishi da idanu yana fatan ya sanar dashi abin da ke faruwa.
Cikin wani irin zafin nama ya dawo gabansa ya ɗora hancin bindigar hannunsa a tsakiyar kansa yana kallonsa rai ɓace ya ce
“ina Nana take?”
Girgiza kai kawai Junaid yake, jikinsa sai rawa yake. Ya sake matse kunamar bindigar ya ce
“ka faɗa min ko na harbeka, kuma idan na kasheka na kashe banza!”
Bakinsa na rawa ya ce
“Waam... wallahi, wallahi ban sani ba, ban san Nana ta bar gidan nan ba”
Shiru ya yi yana kallonsa da ɗan mamaki, dan ya lura babu ƙarya a maganarsa ya ɗauke bindigar ya miƙewa ɗaya daga cikinsu sannan ya zaro hotunan da suke aljihunsa, buɗesu ya yi ya kara masa a fuska yanda zai gani ya ce
“ba kai bane wannan?”
Da mamaki Junaid ke kallonsa sai kuma ya kai hannu zai kwace hoton yana faɗin “ina ka samu wadannan hotunan?”wani banzan kallo Abdusammad ya watsa masa sannan ya mayar da hotunan envelope ɗin ya ce“ina Nana take?”
Junaid ya sake girgiza kansa a karo na barkatai kafin ya ce“wallahi ban sani ba! Ban san ma bata gida ba, yaushe ta bar gida?”
Kujera yaja ya zauna yana kallonsa sosai fuskarsa a haɗe babu alamar wasa ya ce“tell me ina ka haɗu da ita? And kada ka ɓoye min koda abu guda ɗaya ne” Junaid ya dinga kallonsa sai kuma ya sunkuyar da kansa, Da hannu ya yi musu alama dasu dawo suka dawo kansa suka tsaya kowanne yana riƙe da bindigarsa har sannan. A hankali ya daga idanunsa yana kallonsa sai kuma ya sake saukewa, kusan 2mins kafin ya buɗe baki ya fara bashi labarin duk abin da ya faru daga farko har zuwa ƙarshe.
Ban da kallonsa babu abin da Abdusammad ke yi, Junaid da ke kuka kamar ransa zai fita ya sake cewa“wallahi ban yi da niyyar cutar da Nana ba, sam bana nufinta da mugun abu”
Numfasawa Abdusammad ya yi yana saurarensa har sannan, gaba ɗaya kansa ya kulle, ya lura babu ƙarya a cikin zantukan Junaid. Ya tashi tsaye yana kallonsa ya ce
“baka nufinta da sharri amma ka iya ɗaukanta hotuna har kake mata barazana? Sannan baka nufinta da sharri har ka iya cutar da ita duk da cewa ita da zuciya ɗaya taje wajenka? Haka ne baka nufinta da sharri?”
Girgiza kai Junaid ya yi yana jin wanda irin ɗaci a ransa ya ce“wallahi bana nufin Nana da sharri, na san ban kyauta ba, kuma ban yi dai-dai ba. Amma nima zugar aboki ce ta yi tasiri akaina, sai bayan dana aikata abun sannan nafara danasani. Wallahi ban taɓa tunanin fitar da hotunan Nana ba, hasalima bayan wanda na tura mata bani da wasu, dan na goge ba zan juri kalla ba. Kawai na so yin amfani da hakan ne wajen sakata ta yi duk mai yiwuwa kar ta ga an rabamu.”
Ya sauke numfashi hawaye na gangarowa kan fuskarsa ya ci gaba da faɗin “sai dai hakan bai yi wani amfani ba. Na rasata, gefe guda kuma na haifar mata da baƙin ciki wanda zata dade tana tunawa, a yanzu banida wani buri daya shige naga Nana domin na nemi yafiyarta duk da na san ban cancanci hakan ba. Ta ɗaukeni masoyi na gaskiya ni kuma na cutar da ita, Dan Allah ina zan ga Nanaa?...”
Ya ƙare maganar yana sakin wani raunataccen kuka. Shiru Abdusammad ya yi can kuma ya furzar da iska daga bakinsa ya ce“kana son ka ce min baka san inda take ba?”