← Book details Naanah Part 1 Complete Hausa Novel Local reading mode
READING PART 106 OF 125

Sashe 106

Naanah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read

Jiki a sanyaye ta miƙe ya yi gaba yana riƙe da hannunta, Gaba ɗaya kunyar Abdusammad ɗin ta rufeta. Shi kuwa ɗauke kansa ya yi yana taɓe baki. Bayan sun bar wajen ya mai da idanunsa kan Nana wadda ke danna wayarta, kamar ba zai magana ba sai kuma ya sanya hannu ya karbi wayar yana kalla, Game take as usual, Ya ɗan yi murmushi ya ce

“Ke ba zaki taɓa girma ba ko?”

Turo baki ta yi ta kawo hannu zata amshi wayar, Ya ɗauke yana tsuke fuska ya ce“Ina wasa da ke?”

“Uncle ka bani wayataaa.!”

Ta yi maganar kamar zata yi kuka, Bai ce komai ba ya zura a aljihunsa yana ɗauke kansa, Ta dinga kallon sa sai kuma ta fara hawaye tana cewa

“Ka bani dan Allah.”

Ba zaka taɓa cewa dashi take ba dan ko kallon ta bai yi ba, Ganin tana shirin ɓare baki ya sanya shi kallon ta fuskarsa a tamke babu alamar wasa ya ce

“Kina min kuka ina buge ki anan, Ɗauka abincin ki.”

Ya yi maganar yana nuna mata plate ɗin data ajiye a ƙasa. Kasa cewa komai ta yi, ganin yanda ya yi da fuska, Ya dauko plate ɗin abincin ya ɗiba a spoon yana kallonta ya ce

“Haaa..”

Kallon sa ta tsaya yi, Ya ajiye spoon ɗin ya rankwasheta a goshi, Dafe goshinta ta yi tana marairaice fuska kamar zata yi kuka. Ya sake diban abincin ya kai mata baki, Babu yanda ta iya haka ta buɗe bakin, Ya dinga feeding ɗinta har ta kusa cinyewa. Bayan ta gama ya ɗora mata plate ɗin akan cinyarta sannan ya ce

“Oyah tashi anan. Sai da safe”

“Sai da safe kuma? Yanzu fa rana ce”

“To ko zaki bi ni ne?”

Ya yi maganar yana miƙewa tsaye, Gyaɗa masa kai ta yi duk da bata san inda za shin ba. Bai ce komai ya juya ya fice daga ɗakin, Ta ajiye plate ɗin a wajen ta biyo bayansa tana gyara zaman mayafin kanta. A compound ɗin ta same shi yana shirin buɗe motar sa, Ta ƙaraso wajen da sauri tana cewa

“To ba zaka tsaya ni ba?”

“Za dai ki bi ni ki ka ce?”

Ya yi tambayar yana ƙoƙarin shiga motar, Gyaɗa masa kai ta yi. Ya jinjina kansa ya ce“Zagayo to” Da sauri ta koma ɗaya side ɗin ta buɗe ta shiga tana murmushi. Shi dai bai ce mata komai ba ya yi motar key suka bar compound ɗin. Tun Nana na kallon titi tana murmushi har sai da ta fara kallon sa da mamaki, ganin tafiya kawai suke yasa ta ce

“Uncle.”

Sam bai ji ta ba, Saboda yanda ta yi maganar a can ƙasa shi kuma yana bin karatun Alkur'anin da ya kunna. Ta sanya hannunta ta taɓa shi ta ce“Unclee...!” Sai a sannan ya ɗan kalleta, Ya rage volume ɗin karatun ya ce

“Mene ne?”

“Ina zamu je?”

Ta ce kamar zata yi kuka, Ɗan murmushi ya yi ya ce“Sai da ke zan yi.” Dariya ta yi ta ce

“Sai dani kuma? Ni ɗin?”

Gyaɗa mata kai kawai ya yi sannan ya ƙara volume ɗin karatunsa, Ita ma bata sake cewa komai ba ta mai da kanta jikin mirror tana kalle-kalle. A bakin wani ƙaton mansion ya ɗan yi parking, Nana ta dinga kallon gidan dan bata taɓa ganinsa ba. Horn ya danna aka zo aka buɗe gate ɗin, Ya tura hancin motar ciki. A tsakiyar compound ɗin gidan ya yi parking sannan ya kashe motar ya sakko, Nana ta buɗe side dinta ta fito tana karewa babban compound ɗin kallo. Iyakar haɗuwa wajen ya haɗu, Ya ja hannunta suka nufi main entrance ɗin gidan, Wani katon parlour ne wanda aka ƙawatashi da kujeru na alfarma, Sai tv babba sai curtains masu kyau da tsada, Bai zauna a parlourn ba ya ja hannunta suka nufi sama. Ita dai Nana sai bin sa take da kallo duk inda ya yi, Wani ɗaki ya buɗe ya shiga yana rike da hannunta, Babban bedroom ne mai ɗauke da furnitures da kuma kujera, ya saki hannun ta yana ƙoƙarin kwance agogon hannun sa..

“Bari na kwance ma”

Yaji saukar muryarta tana ƙoƙarin taɓa hannunsa. Bai ce komai ba ya dinga kallon ta har ta kwance agogon ya juya ya bar wajen ita kuma ta nufi gefen gado ta zauna tana riƙe da agogon. Tana nan zaune har kusan 20mins kafin ya fito daga toilet yana sanye da bathrobe, Nana ta dinga kallon sa dan bata yi tunanin wanka ya yi ba. Press ya buɗe ya ɗauki wasu kaya masu sauƙin nauyi ya saka sannan ya dawo gefen gadon yana kallon ta ya ce

“Ba zaki yi wanka ba?”

Girgiza masa kai ta yi kafin ta ce“Nayi ai.” Bai ce komai ba ya hau tsakiyar gadon ya kwanta, Ta daɗe zaune a wajen kafin taji ya ce

“Baki jin bacci?”

Kallon sa ta yi sai kuma ta girgiza masa kai duk da baccin data fara ji. Ya ɗan yi murmushi sannan ya jawo hannunta, A gefen sa ya kwantar da ita ya zame mayafin kanta gashinta mai kyau wanda ya sha gyara ya bayyana, A hankali ya kai hannunsa ya fara shafa gashin, Nana ta sauke ajiyar zuciya tana lumshe idanun ta. After some minutes ta fara ƙoƙarin tashi zaune jin abin da yake yi ta ce

“Uncle mu tafi gida!”

Hannu ɗaya ya sanya ya dawo da ita ya kwantar yana murmushi ya ce

“Ba rakoni ki ka yi ba?”

Girgiza kanta ta yi jin yana ƙoƙarin jan rigar jikinta ta ce“a'a ni gida zan je! Wallahi gida zan je uncle...”

Bai tsaya saurarenta ba ya haɗe bakinsu ya fara sauke mata wasu irin kisses masu tsayawa a rai, Nana ta dinga ƙoƙarin kwace kanta amma hakan ya gagara dan ƙarfi ya sakar mata. Tun tana dauriya da shi har sai da ta fara kuka, amma sam bai san tana yi ba ya ci gaba da abin da ya yi niyya.. Sai da dan kansa ya haƙura ya koma gefe yana sauke numfashi.

****
Basu suka dawo gidan ba sai wajen karfe 6:00 na yamma, Yana gama parking ta buɗe motar ta fita babu ko sallama, Murmushi kawai ya yi yana girgiza kansa sannan ya yi gaba, Bayan ya fito daga motar yana ƙoƙarin shiga gidan Noor ta tawo da gudu ta rungumeshi tana dariya. Sunkuyawa ya yi ya ɗauketa yana murmushi ya ce

“Noor ina ki ka je?”

“Naje wajen Anty Juwaira ne Abbie.”

Jinjina kansa kawai ya yi sannan ya buɗe kofar suka shiga, Babu kowa a parlourn sai tashin ƙamshi da yake. Ya kalleta ya ce“Muje ciki ko?” gyada masa kai ta yi suka nufi upstairs tare, Zahra dake kitchen tana girki sam bata ji shigowar su ba. Ta ƙarasa kwasar kayan abincin ta fita dasu ta ajiye a parlourn, Da sauri kuma ta koma kitchen ɗin, ledar maganin data zuba ta ɗauka ta yar a shara sannan ta gyare ko ina ta fito. Zaune ta same shi a parlour yana danna wayarsa, ta dinga kallon sa da mamaki can kuma ta ce

“Doctor dama ka dawo?”

Gyaɗa mata kai ya yi ya ce“Eh na dawo, Ai naga kamar kina aiki ne” Murmushi ta yi ta ce“Ai na gama ma, Daman abincin Hajiya Babba ne.”

“Kin yi abincin ne?”

Gyaɗa masa kai ta yi tana murmushi, Ya ɗan jinjina kansa fuskarsa a sake ya ce“Su Hajiya masu surukai. To maza ki kai mata”

“Zan fara wanka ne”

Toh kawai ya ce, Ya nufi sama da sauri. Ko minti biyar bata yi da hawa ba Noor ta sakko tana riƙe da teddy ƙato a hannunta, Ta ƙaraso wajensa tana dariya ta ce“Abbie!” Murmushi ya yi ya ja kumatunta ya ce

“Nooriya!”

“Abbie yunwa nake ji!”

Ta yi maganar tana yatsine fuska, Girgiza kansa ya yi ya ce“Da gaske? Ko zaki ci tuwo to?" gyaɗa masa kai ta yi, Ya kalleta sai kuma ya kalli inda Zahra ta ajiye warmern ya ce

“To bari na baki.”

Daga haka ya tashi ya ƙarasa gaban warmern, A kitchen ya saka ta ɗauko plate ya buɗe warmern farko, Tuwon shinkafa ne wanda ya yi kyau an zuba shi a ledoji, Ya ɗauki ɗaya ƙarami ya raba biyu ya saka mata rabi dan ya san ba cin abinci take ba, Sannan ya buɗe ɗayan ya ga miyar egusi ce lafiyayya, Da ɗan yawa ya zuba mata miyar ya miƙa mata, Karɓa ta yi sannan ta yi masa kiss a kumatu ta ce

”Thank you Abbie.”

Murmushi kawai ya yi sannan ya tashi ya koma kan kujera ya zauna, Itama ta koma can kujerar da ke kusa da tv ta zauna ta fara cin tuwon tana lumshe ido.

08106608363
Nanameera.
*Page 63*.

Amma ta dinga kallon ta babu yabo babu fallasa ta ce“Shi ne ki ka yi wannan daɗewar?” Sunkuyar da kanta ta yi a sanyaye ta ce“Eh fa Amma. Kuma ai har da uncle ma yana can” Taɓe baki ta yi ta tashi tana kallon ta ta ce“Tashi ki dafa min shinkafa”Toh kawai ta ce sannan ta miƙe ta nufi kitchen duk da yanda take jin jikinta babu gwari. Ruwan shinkafar kawai ta ɗora ta fito ta dawo parlour ta zauna tana jiran ya tafasa, Haule dake zaune kan kujera ta kalleta ta ce“Nana ɗazu Atta ta ce na kira ki” Kallon ta Nana ta yi tana riƙe da wayarta ta ce“To ni ba zan je ba wallahi, haka kawai ta dinga zagina.” Ita dai Haule bata sake cewa komai ba ta ci gaba da kallon ta, After some minutes ta tashi ta koma kitchen ɗin dan duba abin da take.

****
Zahra ta sakko tana kallon Noor dake cin tuwon a hankali dan daman ita ba gwanar cin abinci ba ce, Da mugun mamaki ta ƙaraso wajen, Ta ɗago kanta hankali a ɗan tashe ta ce

“Ke! Wane ya baki wannan abincin?”

Noor ta kalleta ganin yanda take zare ido ya sanyata sunkuyar da kanta, Ta daka mata tsawa ta ce

“Ba magana nake miki ba?”

Sai a sannan Abdusammad ya kallesu dalilin tsawar da yaji, Ya buɗe baki cike da mamakin ganin yanda ta cakume yarinyar ya ce

“Zahra lafiya dai?”
Chapter 106 · 0% Book details