Sashe 108
Naanah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Abba ya gama gane ba fahimta yake ba, Dan haka ya shafa kansa ya ce
“To shikenan sai a dawo da ita. Muje yanzu kaji"
Bai ce komai ba yabi bayan Abba dan tuni Aliyu ya fice da ita. A compound ɗin Hajiya Babba suka yi parking, Abba ya fito yana kallon Abdusammad wanda ko motsi bai yi ba, Zagayowa ya yi ya kama hannunsa ya fito daga motar ya ce
“Abdussamad muje”
Gyaɗa masa kai kawai ya yi sannan suka nufi cikin gidan Hajiya Babba, Shimfiɗe ya samu Noor akan carpet an rufeta da farin kyalle har kanta, Ya yi saurin sakin hannun Abba ya ƙarasa ya yaye kyallen cikin ɓacin rai ya ce
“Bana son irin haka! Kada wanda ya sake rufe min ƴa, akan me?!”
Shiru duk suka yi, Hajiya Babba da ke zaune ta dinga kallon sa, Tausayi ya bata ta san irin son da yake yi wa Noor ɗin, Ta san irin shaƙuwar da ke tsakaninsa da ita. Dan haka ta san dole zai shiga hali na ɗimuwa. Abba ne ya yi ƙarfin halin zuwa gabansa ya dafa shi, Abdusammad ya ɗago idanunsa ya kalleshi sai kuma ya tashi tsaye ya ce
“Abba ka ce su daina rufe min ita, akan me? Me ta yi musu? Yarinyar nan karama ce sai ta kasa numfashi?”
Girgiza kai Abba ya yi yana jin wani irin zafi a ransa, Ya dafa shi hawaye na ƙoƙarin fitowa daga cikin idanunsa ya ce
“Abdul ka yi haƙuri kaji! Allah shi ne ke bada haihuwa, Shi ne ke bamu ɗa, kuma shi ne ke karɓa a duk sanda ya so, Duk mai rai mamaci ne, dole sai kowa ya mutu. Dan haka ka ɗauki haƙuri, Allah ya yi mai ƙaramin kwana ce, Allah ya yi ba zaka girma da ita ba, Ka yi haƙuri!”
Janye hannun Abba ya yi daga jikinsa ya ce“Bangane ba Abba, meya sameta to?”
“Ta mutu!”
Abba ya faɗa kai tsaye, Wani irin abu ne ya zo ya tokare masa a ƙirji, Ya ja wani irin dogon numfashi sai kuma ya dafe kansa saboda sara masan da ya yi. Abba ya riƙe shi ya ce
“Ka nutsu dan Allah.”
Jinjina kansa ya yi ya juya yana ƙoƙarin komawa inda take, Sai dai kafin ya ƙarasa yaji kamar an daki ƙirjinsa sai gashi a ƙasa a sume.
08106608363
Nanameera.*Page 64.*
A hankali ya shiga buɗe idanunsa wanda suka yi masa nauyi, Motsin da taji ya sanyata riƙe shi muryarta a sanyaye ta ce
“Uncle.”
Kallon ta ya yi amma bai ce komai ba, Nana ta shiga goge hawayenta tana kallon sa. Buɗe kofar ɗakin aka yi, Abba ya shigo yana kallon su ya ce
“Nana ya tashi ne?”
A sanyaye ta gyaɗa kanta tana janye hannunta daga nasa, Abba ya ƙaraso wajen ya zauna gefen gadon yana kallon sa ya ce
“Abdul ya jikin?”
Lumshe idanu Abdusammad ya yi kafin ya ce
“Abba da gaske Noor ta mutu?”
Wani irin abu ne ya tsayawa Abba arai, Ya jinjina masa kai a sanyaye. Bai ce komai ba ya sake rufe idanunsa, Abba ya kalli Nana wadda ke kuka a hankali ya ce
“Tashi ki je ina zuwa.”
Toh kawai ta ce sannan ta mike ta fice daga ɗakin, Abba ya gyara zamansa yana kallon sa sosai a nutse ya ce
“Ka yi haƙuri Abdusammad, na sani babu daɗi, kowa ma yaji babu daɗi. Amma dan Allah dan Annabi ka yi haƙuri, kayi mata addu'a, Allah yasa mai ceto ce.”
A hankali ya tashi zaune, Abba ya dinga kallon sa jin bai ce komai ba. Can ya sauke numfashi ya ce
“Ba komai Abba, Na sani Allah ya jiƙanta.”
Sosai Abba yaji sanyi a ransa, dan ya san tun da ya ce haka to ya bar zancen. A sanyaye ya sauka daga kan gadon ya nufi toilet, Abba ya tashi ya fice daga ɗakin shima.
Ban da kuka babu abin da Zahra ke yi tun bayan da aka sanar da ita mutuwar Noor ɗin, Ta zama tamkar wata zararriya, Ta rasa inda zata kama. Tunanin ta ɗaya, maganin da ke cikin abincin ne ya kashe Noor ɗin? To akan me? Dama maganin mutuwa ne?. Tana nan zaune aka buɗe ƙofar ɗakin, A hankali ta ɗaga idanunta tana kallon sa. Tsaye yake ya harɗe hannayensa a ƙirji, Idanunsa sun ɗan janye sun yi jajur dasu. Sai da gabanta ya faɗi saboda irin kallon da taga yana yi mata, Ya sauke nunfashi ba tare da ya ce komai ba. Itama kasa magana ta yi sai hawaye dake zubowa kan fuskarta, Sun daɗe a haka sai kawai taga ya juya ya fice daga ɗakin without saying anything. Zahra ta dinga kallon wajen daya bari cike da mamakin abin da ya hana shi maganar, Yana fita ɗakinsa ya nufa, Ya zauna gefen gado ya yi shiru yana tunani, Can kuma ya tashi ya shige toilet.
****
Washegari da safe wajejen ƙarfe 8:00 aka kai Noor, Tun da suka dawo bai ce da kowa komai ba ya nufi cikin gidansa. Yinin ranar babu wanda ya gan shi, A ɓangaren Zahra kuwa suna zaune a parlourn ta ita da Anty Khadijah, Amal, Safeena da kuma Siyama. Ta yi kuka har ta gaji, Ta suma yafi sau biyar, Daga ƙarshe ta haƙuri ta yi shiru sai kukan zuci. Haka ma Nana ta yi kuka har ta gaji, Duk yanda Amma ta yi da ita ƙin cin abinci ta yi, Sai kuka sai tunani. Bayan kwana uku kowa ya watse, Sai wanda abun ya shafa. Ranar Litinin around 9:00am Aliyu da Sultan suka shigo parlour, Yana zaune gefen Abba ya yi shiru idanunsa a lumshe. Hajiya Babba na zaune akan kujera tana kallon su, Bayan sun zauna suka gaisar da kowa sannan wajen ya yi shiru. Papa ne ya fara cewa
“Sultan muna jin ka"
Sauke zazzafan numfashi Sultan ya yi kafin ya ce
“Papa na rasa abin cewa, Wane ya sanya guba a cikin abinci?”
Shiru duk suka yi, Can dai Abba ya ce
“Sultan kun duba sosai kuwa? Guba kuma? Me ta ci? Wane ya bata abincin?”
“Ni ne na bata!”
Kamar daga sama suka ji muryar tasa, Kallon sa duk suka yi, amma ga mamakin su sai suka ga basu yake kallo ba, Hasalima idanun sa a lumshe suke. Abba ne ya ce
“To a ina aka samu guba Abdusammad?”
Sai a sannan ya buɗe idanun sa, Sosai suka yi jaa, Hawaye ya kwanta a cikinsu. Ya sauke numfashi sannan ya ce“Nima ban sani ba Abba. Pls excuse me!”
Ya yi maganar yana miƙewa tsaye, Bai tsaya jiran abin da zasu ce ba ya fice daga parlourn da sauri. Shiru duk suka yi suna mamakin abin da ya faɗa ɗin, Papa ya sauke numfashi yana girgiza kansa ya ce
“Allah ya kyauta.”
“To a ina aka samu guba a cikin abincin? Ni ban gane ba”
Aliyu ya yi maganar a dame, Ajiyar zuciya Papa ya sauke sannan ya ce
“Kawai abar maganar tun da baya so a yi.”
“But Papa...”
Ɗaga masa hannu Papa ya yi, Ya miƙe tsaye yana gyara zaman rigarsa ya ce“Ya isa haka nace!”
Ya yiwa Hajiya Babba sallama sannan ya fice daga parlourn, Ita ma tashi ta yi ta nufi sama ba tare da ta ce komai ba. Abba ya kalli Aliyu wanda ya yi shiru ya ce
“Ka bar maganar ka ji, Zan yi masa magana”
Gyaɗa masa kai ya yi a hankali, Abba ya tashi ya fice daga parlourn shima. Taɓe baki Sultan ya yi ya ce“Ai shikenan, amma wallahi Yaya guba ce a ciki, Kuma a abin da ta ci ne.”
Da mamaki Aliyu ya ce“To akan mene yasa baya son a yi maganar?”
Girgiza kai Sultan ya yi ya ce“Nima ban sani ba Yaya, But definitely there is something fishy.”
Shiru Aliyu ya yi can kuma ya gyaɗa kansa ya ce“Dole na nemo mene ne. I'm coming” Ya ƙare maganar yana tashi tsaye, Sultan bai ce komai ba har ya fice daga parlon, Shima ya tashi yabi bayansa.
****
Nana na zaune kan gado ta yi shiru tana tunani, Amma ta buɗe ɗakin ta shigo tana kallon ta.
“Naana.”
Amma ta kira sunanta, A hankali ta buɗe idanunta, a sanyaye ta ce“Na'am Amma!.”
“Ki tashi ki yi breakfast.”
“Na ƙoshi”
Ta ce a hankali, Da mamaki Amma ke kallon ta, Can kuma ta ce“Da ki ka ci me?”
Bata ce komai ba sai yamutse fuska take, Amma ta harareta ta ce
“Malama tashi na ce!”
Madadin ta tashin sai kawai ta fara kuka, Amma ta yi tsaye tana kallon ta. Can kuma ta ƙarasa gaban gadon ta zauna ta jawota, Faɗawa jikinta tayi tana sakin wani marayan kuka, Amma ta dinga shafa kanta without saying anything, Cikin kuka Nana ta ce
“Amma shikenan Noor ta mutu ta bar mu? Shikenan Amma, ba zan sake ganinta ba? Amma ya zan yi?”
Girgiza kai Amma ta yi, Ita ma jikinta a sanyaye ta ce“ki yi hakuri Nana, Allahn daya bamu ita shi ne ya ɗauketa, Babu yanda zamu yi sai dai mu yi haƙuri kin ji. Ki daina kuka”
Bata ce komai ba ta ci gaba da kukanta tana jikin Amma, After some minutes Amma ta ɗagota ta ce
“Tashi muje ki ci abinci.”
Bata yi musu ba ta tashi daga jikinta, Amma ta sauka daga kan gadon tana riƙe da hannunta suka fice daga ɗakin.
****
Ya jima zaune gefen gadon yana jujjuya pen ɗin hannunsa, Can dai ya sauke numfashi ya tashi ya ɗauki car key ɗinsa ya fice daga ɗakin. Zahra na zaune akan sofa a ƙasa ta zuba uban tagumi, Ya ƙaraso parlourn yana kallon ta ya ce
“Zahra ko zaki rakani?”
“To shikenan sai a dawo da ita. Muje yanzu kaji"
Bai ce komai ba yabi bayan Abba dan tuni Aliyu ya fice da ita. A compound ɗin Hajiya Babba suka yi parking, Abba ya fito yana kallon Abdusammad wanda ko motsi bai yi ba, Zagayowa ya yi ya kama hannunsa ya fito daga motar ya ce
“Abdussamad muje”
Gyaɗa masa kai kawai ya yi sannan suka nufi cikin gidan Hajiya Babba, Shimfiɗe ya samu Noor akan carpet an rufeta da farin kyalle har kanta, Ya yi saurin sakin hannun Abba ya ƙarasa ya yaye kyallen cikin ɓacin rai ya ce
“Bana son irin haka! Kada wanda ya sake rufe min ƴa, akan me?!”
Shiru duk suka yi, Hajiya Babba da ke zaune ta dinga kallon sa, Tausayi ya bata ta san irin son da yake yi wa Noor ɗin, Ta san irin shaƙuwar da ke tsakaninsa da ita. Dan haka ta san dole zai shiga hali na ɗimuwa. Abba ne ya yi ƙarfin halin zuwa gabansa ya dafa shi, Abdusammad ya ɗago idanunsa ya kalleshi sai kuma ya tashi tsaye ya ce
“Abba ka ce su daina rufe min ita, akan me? Me ta yi musu? Yarinyar nan karama ce sai ta kasa numfashi?”
Girgiza kai Abba ya yi yana jin wani irin zafi a ransa, Ya dafa shi hawaye na ƙoƙarin fitowa daga cikin idanunsa ya ce
“Abdul ka yi haƙuri kaji! Allah shi ne ke bada haihuwa, Shi ne ke bamu ɗa, kuma shi ne ke karɓa a duk sanda ya so, Duk mai rai mamaci ne, dole sai kowa ya mutu. Dan haka ka ɗauki haƙuri, Allah ya yi mai ƙaramin kwana ce, Allah ya yi ba zaka girma da ita ba, Ka yi haƙuri!”
Janye hannun Abba ya yi daga jikinsa ya ce“Bangane ba Abba, meya sameta to?”
“Ta mutu!”
Abba ya faɗa kai tsaye, Wani irin abu ne ya zo ya tokare masa a ƙirji, Ya ja wani irin dogon numfashi sai kuma ya dafe kansa saboda sara masan da ya yi. Abba ya riƙe shi ya ce
“Ka nutsu dan Allah.”
Jinjina kansa ya yi ya juya yana ƙoƙarin komawa inda take, Sai dai kafin ya ƙarasa yaji kamar an daki ƙirjinsa sai gashi a ƙasa a sume.
08106608363
Nanameera.*Page 64.*
A hankali ya shiga buɗe idanunsa wanda suka yi masa nauyi, Motsin da taji ya sanyata riƙe shi muryarta a sanyaye ta ce
“Uncle.”
Kallon ta ya yi amma bai ce komai ba, Nana ta shiga goge hawayenta tana kallon sa. Buɗe kofar ɗakin aka yi, Abba ya shigo yana kallon su ya ce
“Nana ya tashi ne?”
A sanyaye ta gyaɗa kanta tana janye hannunta daga nasa, Abba ya ƙaraso wajen ya zauna gefen gadon yana kallon sa ya ce
“Abdul ya jikin?”
Lumshe idanu Abdusammad ya yi kafin ya ce
“Abba da gaske Noor ta mutu?”
Wani irin abu ne ya tsayawa Abba arai, Ya jinjina masa kai a sanyaye. Bai ce komai ba ya sake rufe idanunsa, Abba ya kalli Nana wadda ke kuka a hankali ya ce
“Tashi ki je ina zuwa.”
Toh kawai ta ce sannan ta mike ta fice daga ɗakin, Abba ya gyara zamansa yana kallon sa sosai a nutse ya ce
“Ka yi haƙuri Abdusammad, na sani babu daɗi, kowa ma yaji babu daɗi. Amma dan Allah dan Annabi ka yi haƙuri, kayi mata addu'a, Allah yasa mai ceto ce.”
A hankali ya tashi zaune, Abba ya dinga kallon sa jin bai ce komai ba. Can ya sauke numfashi ya ce
“Ba komai Abba, Na sani Allah ya jiƙanta.”
Sosai Abba yaji sanyi a ransa, dan ya san tun da ya ce haka to ya bar zancen. A sanyaye ya sauka daga kan gadon ya nufi toilet, Abba ya tashi ya fice daga ɗakin shima.
Ban da kuka babu abin da Zahra ke yi tun bayan da aka sanar da ita mutuwar Noor ɗin, Ta zama tamkar wata zararriya, Ta rasa inda zata kama. Tunanin ta ɗaya, maganin da ke cikin abincin ne ya kashe Noor ɗin? To akan me? Dama maganin mutuwa ne?. Tana nan zaune aka buɗe ƙofar ɗakin, A hankali ta ɗaga idanunta tana kallon sa. Tsaye yake ya harɗe hannayensa a ƙirji, Idanunsa sun ɗan janye sun yi jajur dasu. Sai da gabanta ya faɗi saboda irin kallon da taga yana yi mata, Ya sauke nunfashi ba tare da ya ce komai ba. Itama kasa magana ta yi sai hawaye dake zubowa kan fuskarta, Sun daɗe a haka sai kawai taga ya juya ya fice daga ɗakin without saying anything. Zahra ta dinga kallon wajen daya bari cike da mamakin abin da ya hana shi maganar, Yana fita ɗakinsa ya nufa, Ya zauna gefen gado ya yi shiru yana tunani, Can kuma ya tashi ya shige toilet.
****
Washegari da safe wajejen ƙarfe 8:00 aka kai Noor, Tun da suka dawo bai ce da kowa komai ba ya nufi cikin gidansa. Yinin ranar babu wanda ya gan shi, A ɓangaren Zahra kuwa suna zaune a parlourn ta ita da Anty Khadijah, Amal, Safeena da kuma Siyama. Ta yi kuka har ta gaji, Ta suma yafi sau biyar, Daga ƙarshe ta haƙuri ta yi shiru sai kukan zuci. Haka ma Nana ta yi kuka har ta gaji, Duk yanda Amma ta yi da ita ƙin cin abinci ta yi, Sai kuka sai tunani. Bayan kwana uku kowa ya watse, Sai wanda abun ya shafa. Ranar Litinin around 9:00am Aliyu da Sultan suka shigo parlour, Yana zaune gefen Abba ya yi shiru idanunsa a lumshe. Hajiya Babba na zaune akan kujera tana kallon su, Bayan sun zauna suka gaisar da kowa sannan wajen ya yi shiru. Papa ne ya fara cewa
“Sultan muna jin ka"
Sauke zazzafan numfashi Sultan ya yi kafin ya ce
“Papa na rasa abin cewa, Wane ya sanya guba a cikin abinci?”
Shiru duk suka yi, Can dai Abba ya ce
“Sultan kun duba sosai kuwa? Guba kuma? Me ta ci? Wane ya bata abincin?”
“Ni ne na bata!”
Kamar daga sama suka ji muryar tasa, Kallon sa duk suka yi, amma ga mamakin su sai suka ga basu yake kallo ba, Hasalima idanun sa a lumshe suke. Abba ne ya ce
“To a ina aka samu guba Abdusammad?”
Sai a sannan ya buɗe idanun sa, Sosai suka yi jaa, Hawaye ya kwanta a cikinsu. Ya sauke numfashi sannan ya ce“Nima ban sani ba Abba. Pls excuse me!”
Ya yi maganar yana miƙewa tsaye, Bai tsaya jiran abin da zasu ce ba ya fice daga parlourn da sauri. Shiru duk suka yi suna mamakin abin da ya faɗa ɗin, Papa ya sauke numfashi yana girgiza kansa ya ce
“Allah ya kyauta.”
“To a ina aka samu guba a cikin abincin? Ni ban gane ba”
Aliyu ya yi maganar a dame, Ajiyar zuciya Papa ya sauke sannan ya ce
“Kawai abar maganar tun da baya so a yi.”
“But Papa...”
Ɗaga masa hannu Papa ya yi, Ya miƙe tsaye yana gyara zaman rigarsa ya ce“Ya isa haka nace!”
Ya yiwa Hajiya Babba sallama sannan ya fice daga parlourn, Ita ma tashi ta yi ta nufi sama ba tare da ta ce komai ba. Abba ya kalli Aliyu wanda ya yi shiru ya ce
“Ka bar maganar ka ji, Zan yi masa magana”
Gyaɗa masa kai ya yi a hankali, Abba ya tashi ya fice daga parlourn shima. Taɓe baki Sultan ya yi ya ce“Ai shikenan, amma wallahi Yaya guba ce a ciki, Kuma a abin da ta ci ne.”
Da mamaki Aliyu ya ce“To akan mene yasa baya son a yi maganar?”
Girgiza kai Sultan ya yi ya ce“Nima ban sani ba Yaya, But definitely there is something fishy.”
Shiru Aliyu ya yi can kuma ya gyaɗa kansa ya ce“Dole na nemo mene ne. I'm coming” Ya ƙare maganar yana tashi tsaye, Sultan bai ce komai ba har ya fice daga parlon, Shima ya tashi yabi bayansa.
****
Nana na zaune kan gado ta yi shiru tana tunani, Amma ta buɗe ɗakin ta shigo tana kallon ta.
“Naana.”
Amma ta kira sunanta, A hankali ta buɗe idanunta, a sanyaye ta ce“Na'am Amma!.”
“Ki tashi ki yi breakfast.”
“Na ƙoshi”
Ta ce a hankali, Da mamaki Amma ke kallon ta, Can kuma ta ce“Da ki ka ci me?”
Bata ce komai ba sai yamutse fuska take, Amma ta harareta ta ce
“Malama tashi na ce!”
Madadin ta tashin sai kawai ta fara kuka, Amma ta yi tsaye tana kallon ta. Can kuma ta ƙarasa gaban gadon ta zauna ta jawota, Faɗawa jikinta tayi tana sakin wani marayan kuka, Amma ta dinga shafa kanta without saying anything, Cikin kuka Nana ta ce
“Amma shikenan Noor ta mutu ta bar mu? Shikenan Amma, ba zan sake ganinta ba? Amma ya zan yi?”
Girgiza kai Amma ta yi, Ita ma jikinta a sanyaye ta ce“ki yi hakuri Nana, Allahn daya bamu ita shi ne ya ɗauketa, Babu yanda zamu yi sai dai mu yi haƙuri kin ji. Ki daina kuka”
Bata ce komai ba ta ci gaba da kukanta tana jikin Amma, After some minutes Amma ta ɗagota ta ce
“Tashi muje ki ci abinci.”
Bata yi musu ba ta tashi daga jikinta, Amma ta sauka daga kan gadon tana riƙe da hannunta suka fice daga ɗakin.
****
Ya jima zaune gefen gadon yana jujjuya pen ɗin hannunsa, Can dai ya sauke numfashi ya tashi ya ɗauki car key ɗinsa ya fice daga ɗakin. Zahra na zaune akan sofa a ƙasa ta zuba uban tagumi, Ya ƙaraso parlourn yana kallon ta ya ce
“Zahra ko zaki rakani?”