Sashe 107
Naanah Part 1 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Kallon sa ta yi sai kuma ta mai da Idanunta kan Noor ta ce“Ba zaki faɗa min ba? A ina ki ka samu tuwo?”
“Abincin da zaki kai wa Hajiya Babba ne na ɗibar mata tana jin yunwa, mene?”
Wani irin abu ne ya zo ya tsaya mata a ƙirji, Ta saki rigar Noor tana jin zufa na yanko mata, Abdusammad da ke lura da ita ya ce“Ko akwai wata matsala ne?”
Girgiza masa kai Zahra ta yi tana ƙoƙarin magana Noor ta saki wani irin ihu tana wurgi da plate ɗin hannun ta. Da sauri ya taso ganin yanda take ƙandare jiki tana dafe da cikinta, Zahra ta yi saurin durƙusawa gabanta ta riƙeta tana jijjigata, Yana zuwa ya sanya hannunsa ya ɗauketa ya zauna akan kujerar ya riƙe fuskarta ya ce
“Ke Noor! Noor mene ne?”
Ɗan ƙaramin hannunta ta saka ta riƙe nasa muryarta na rawa ta ce
“Ab...Abbi... Abbiena..”
Wani irin faɗuwar gaba yaji ya ziyarce shi, Ya riƙeta sosai a jikinsa ya ce“Mene ne?”
Kasa magana ta yi sai kuka da take a hankali, Ya kalli Zahra wadda ke kuka ita ma ya ce“Kawon ruwa” Toh kawai ta ce sannan ta nufi kitchen da gudu, Abdusammad ya tallafi fuskarta a hannunsa yana kallon ta ya ce
“Nooriena, Me ya faru?”
Ta kasa magana sai hannunsa data ɗora kan cikinta ta runtse ido, Kallon cikin ya yi sai kuma ya taba wuyanta yaji wani irin zafi, Gaba ɗaya sai ya rikice, dan bai san abin da ya sameta ba. Ya girgiza kansa ya ce
“Cikin ki ne yake miki ciwo?”
Gyaɗa masa kai ta yi tana ƙoƙarin magana sai ga dafara ta fara fitowa daga Bakinta. Abdusammad ya miƙe tsaye da ita a hannunsa cikin wani irin yanayi mai kama da tashin hankali ya ce
“Noorie stay still, Bari na kai ki asibiti.”
“Abbiena...!”
Yaji ta kira sunansa idanunta na neman rufewa, Hannunsa ya sanya ya bubbuga fuskarta ya ce“Na'am Noor!” Bata ce komai ba ta buɗe Idanunta wanda hawaye ke zubowa ta gefensu ta kalle shi, Sai kuma ta sake rufewa. Ji ya yi ta kwanto a jikinsa, Jikinta ya saki gaba ɗaya, Da wani irin tashin hankali ya ɗagota ya tallafeta a hannunsa yana girgizata ya ce
“ke! Ke Noor! Noor!”
Shiru babu amsa, Ya sauketa a wajen ya shiga taɓa jikinta, Babu alamar tana numfashi. Zahra ta dawo parlourn hannunta riƙe da cup da ruwa, Ta yi saurin sakin su a ƙasa ganin yanda yake kiran sunan Noor ɗin bata amsawa. Durƙushewa ta yi a gabansu ta fara ƙoƙarin tashin ta tana kuka, Abdusammad ya yi jim sai kuma ya ɗauketa ya fice daga parlourn da sauri. Da gudu Zahra ta biyo bayansu, Ta tarar har ya shiga back seat tabi bayansu da sauri.
****
Amma ta toshe hancinta saboda ƙaurin da taji, Ta ƙarasa gaban gas ɗin dakyar ta buɗe tukunyar. Gaba ɗaya shinkafar ta yi baƙi ta babbake, Sai ƙauri ke tashi, ta kashe gas ɗin sannan ta juya ta fice daga kitchen ɗin rai ɓace tana kiran sunan Nana..
A parlour ta sameta tana baccinta hankali kwance, Amma ta kai mata duka tana kiran sunanta a fusace. Buɗe idanu Nana ta yi ta dinga kallon Amma sai kuma ta tashi zaune tana mitsitsika idanu, Amma da ranta yake a ɓace ta ce
“wani sabon iskancin ne ya sanya ki ka bar min abinci ya babbake? Meke damunki Nana?”
Saurin rufe bakinta ta yi da hannunta sai kuma ta tashi tsaye tana ɗaukan hular ta ta ce“Wallahi bacci ne ya ɗaukeni Amma..” ta nufi kitchen ɗin da sauri, Tana shiga ta samu Amma ta kashe gas ɗin, Ta buɗe tunkuyar sai kuma ta yi saurin rufe bakinta tari na tawo mata. Rufewa ta yi ta juya ta fice daga ɗakin, A tsaye ta samu Amma inda ta bar ta, Ta dinga kallon ta ganin irin yanda ta haɗe rai, Jiki a sanyaye ta ce
“Ki yi haƙuri Amma, wallahi....”
Dakatar da ita Amma ta yi ta hanyar ɗaga mata hannu, Rai ɓace ta fara cewa
“Wato ke ba zaki taɓa hankali ba? Ba zaki nutsu ba? Mene ne amfanin auren da ki ka yi? Haka ki ke a gidan mijin ma kina bari ana zagina. Ace common white rice ba zaki iya dafawa a nutse ba? Uban ki ki ke yi?”
Girgiza kai Nana ta yi jiki a sanyaye ta ce
“Dan Allah Amma ki yi haƙuri, baccin ne ya ɗaukeni ban sani ba.”
“Ai dole bacci ya ɗauke ki! Dole mana! Tun da baki san abin da ki ke ba. To na rantse duk ranar da ki ka sake yimin irin wannan abun sai ran ki ya yi mummunan ɓaci, Kuma ki sani daga yau har ranar da zaki bar garin nan ke ce zaki dinga girka abinci, Ke zaki dinga aiki, duk wani abu da ki ka san ana yi a gida kece zaki dinga yin sa. Idan kin so ki ci gaba da ba dai-dai ba!”
Amma ta ƙare maganar tana harararta, Sai kuma taja tsaki ta bar wajen, Ita dai Nana bata iya ko motsi ba, Dan ta san halin faɗan Ammar. Sai da taga ta shige daƙinta sannan ta ƙarasa kan kujera ta zauna, Ko minti biyu kuma bata yi ba ta kwanta wani baccin ya sake ɗauketa..
****
Tun da aka shiga da ita yake kai komo a wajen, Zahra kuwa sai kuka take ta ɗora hannunta aka. Kusan 30mins kafin Sultan ya buɗe ƙofar ɗakin ya fito, Da Sauri Abdusammad ya ƙarasa gabansa muryarsa a dake ya ce
“Ya jikin nata? What happened to her?”
Kallon sa Sultan ya dinga yi, ya kasa cewa komai. Abdusammad ya ɗan kanƙance idanunsa kafin ya ce
“Sultan mene haka? Do i look like ur mate?”
Girgiza masa kai ya yi, Abdusammad ya kalle shi sai kuma ya sanya hannu ya hankaɗeshi daga wajen ya buɗe ƙofar ɗakin ya shige. Zahra na ganin haka tabi bayansa da sauri, Sultan ya sauke wani zazzafan numfashi hawaye na biyo idanun sa.
Kwance Abdusammad ya sameta, Sai dai ya kasa gane dalilin daya sanya suka rufeta har fuska, Ya ƙarasa gaban gadon ya zauna ya buɗeta. Fuskarta fresh kamar wadda ke murmushi, asalin kamarta dashi ya sake bayyana, Ya kai hannunsa ya taɓa ta a sanyaye ya ce
“sorry ƴar gidan Abbie, zaki samu sauƙi.”
Zahra dake tsaye ɗan nesa dashi ta kalleta jin abin da ya ce. Ta sauke ajiyar zuciya tana dafe ƙirjinta, Sultan ne ya shigo ya tsaya a ɗaya side ɗin gadon yana kallon su, Ganin yanda yake ta nanata zata samu sauƙi. Sun daɗe a haka kafin Abdusammad ya mai da bargon ya rufeta amma ban da fuskarta, Ya tashi tsaye yana kallon Sultan ya ce
“Me ya sameta?”
Kallon sa kawai Sultan ya yi idanunsa cike taf da hawaye. Abdusammad ya girgiza kansa rai ɓace ya ce
“Sultan yaushe ne na fara wasa da kai?”
Jiki a sanyaye ya girgiza kansa yana ƙoƙarin ɓoye damuwarsa ya ce
“Yi haƙuri Yaya. But we lost her!”
Tamkar mafarki, ko kuma almara haka Abdusammad yaji kalaman Sultan na ƙarshe. Ya ɗan ware idanun sa yana son fahimtar abin da ya ce, Sultan ya sake Girgiza kansa wannan karon hawaye na zubowa kan fuskarsa ya ce
“Yaya a ina Noor ta samu guba? Wane ya bawa Noor abinci? A ina ta samu guba!"
Wani irin ihu Zahra ta saki sai gata a ƙasa Sumammiya, Abdusammad da ya kasa koda motsi daga inda yake ya sunkuyar da kansa sai sauke ajiyar zuciya yake akai akai. Da sauri Sultan ya nufi inda Zahra take yana kallon ta, Sai kuma ya fice daga ɗakin da sauri, Not too long suka dawo tare da wasu nurses mata guda uku, Akan wheelchair suka ɗorata suka fita daga ɗakin. Har sannan Abdusammad bai motsa daga inda yake ba, Gumi ne kawai ke tsatsafo masa duk da acn dake wajen, Zuciyarsa ta kasa yarda da abin da Sultan yake, Tunanin sa ya tsaya cak, ƙwaƙwalwarsa ta toshe. Yana nan tsaye har after 15mins Sultan ya dawo, Ya dinga kallon sa cike da tausayawa, Ya san ba lallai a fahimci halin da yake ciki ba, domin kuka ko magana baya ɗaya daga cikin abin da yake yi yayin da baƙin ciki ya yi masa yawa. Sultan ya sauke numfashi ya ƙarasa inda Noor take ya rufe mata fuskarta, Yana ƙoƙarin ɗagowa yaji Abdusammad ya riƙe hannunsa gam, Cikin wata irin kakkausar murya ya ce
“Don't ever try that!”
Sultan bai ce komai ba ya janye jikinsa ya bar ɗakin, Abdusammad ya zauna gefen gadon ya ɗaukota ya ɗora a jikinsa, Ya sanya hannunsa ya tallafi fuskarta muryarsa a sanyaye ya fara cewa
“Noorie! Noorien Abbie, Kina jina ko? Kina ji ko? Ai ƙarya suke yi na sani, babu abin da ya same ki, kina nan tare da Abbie, Ba zaki bar ni ba na sani. I know!”
Bata bashi amsa ba, Domin bata jin abin da yake cewa, ruhin ta ya yi ƙaura daga gangar jikinta, Jin bata ce komai ba ya sanya shi girgiza kansa yana ɗan murmushi ya ce
“Fushi ki ke yi da Abbie? Ki yi haƙuri kin ji. Next time zan kawo ki asibiti da wuri, But...!”
Sai ya sami kansa da yin shiru, Ya zubawa kyakkyawar fuskarta ido yana kallon ta, ba zaka taɓa cewa bata raye ba, Kamar bacci take..irin baccin data saba yi da yamma ta tashi bayan magriba, Wani lokacin kuma idan ta yi baccin shikenan sai gobe. Yana nan zaune sama da mintina ashirin bai sani ba, Shi kansa bai san a wane hali yake ba. Idanunsa dai har sannan na kan fuskarta, Buɗe kofar ɗakin aka yi, Ya daga idanunsa yana kallon su. Abba ne ya shigo sai Aliyu a bayansa, Ya yi saurin cewa
“Yauwa Abba zo kaji wai Noor ce taci guba? A ina Noor ta samu guba?”
Girgiza kai Abba ya yi ya janye Noor daga hannunsa ya miƙawa Aliyu, Abdusammad zai yi magana Abba ya kama hannunsa a sanyaye ya ce
“Muje gida tukun”
“But Abba ai bata ji sauki ba, Ya za'a yi mu tafi gida da ita a haka? At least ta samu lafiya”
“Abincin da zaki kai wa Hajiya Babba ne na ɗibar mata tana jin yunwa, mene?”
Wani irin abu ne ya zo ya tsaya mata a ƙirji, Ta saki rigar Noor tana jin zufa na yanko mata, Abdusammad da ke lura da ita ya ce“Ko akwai wata matsala ne?”
Girgiza masa kai Zahra ta yi tana ƙoƙarin magana Noor ta saki wani irin ihu tana wurgi da plate ɗin hannun ta. Da sauri ya taso ganin yanda take ƙandare jiki tana dafe da cikinta, Zahra ta yi saurin durƙusawa gabanta ta riƙeta tana jijjigata, Yana zuwa ya sanya hannunsa ya ɗauketa ya zauna akan kujerar ya riƙe fuskarta ya ce
“Ke Noor! Noor mene ne?”
Ɗan ƙaramin hannunta ta saka ta riƙe nasa muryarta na rawa ta ce
“Ab...Abbi... Abbiena..”
Wani irin faɗuwar gaba yaji ya ziyarce shi, Ya riƙeta sosai a jikinsa ya ce“Mene ne?”
Kasa magana ta yi sai kuka da take a hankali, Ya kalli Zahra wadda ke kuka ita ma ya ce“Kawon ruwa” Toh kawai ta ce sannan ta nufi kitchen da gudu, Abdusammad ya tallafi fuskarta a hannunsa yana kallon ta ya ce
“Nooriena, Me ya faru?”
Ta kasa magana sai hannunsa data ɗora kan cikinta ta runtse ido, Kallon cikin ya yi sai kuma ya taba wuyanta yaji wani irin zafi, Gaba ɗaya sai ya rikice, dan bai san abin da ya sameta ba. Ya girgiza kansa ya ce
“Cikin ki ne yake miki ciwo?”
Gyaɗa masa kai ta yi tana ƙoƙarin magana sai ga dafara ta fara fitowa daga Bakinta. Abdusammad ya miƙe tsaye da ita a hannunsa cikin wani irin yanayi mai kama da tashin hankali ya ce
“Noorie stay still, Bari na kai ki asibiti.”
“Abbiena...!”
Yaji ta kira sunansa idanunta na neman rufewa, Hannunsa ya sanya ya bubbuga fuskarta ya ce“Na'am Noor!” Bata ce komai ba ta buɗe Idanunta wanda hawaye ke zubowa ta gefensu ta kalle shi, Sai kuma ta sake rufewa. Ji ya yi ta kwanto a jikinsa, Jikinta ya saki gaba ɗaya, Da wani irin tashin hankali ya ɗagota ya tallafeta a hannunsa yana girgizata ya ce
“ke! Ke Noor! Noor!”
Shiru babu amsa, Ya sauketa a wajen ya shiga taɓa jikinta, Babu alamar tana numfashi. Zahra ta dawo parlourn hannunta riƙe da cup da ruwa, Ta yi saurin sakin su a ƙasa ganin yanda yake kiran sunan Noor ɗin bata amsawa. Durƙushewa ta yi a gabansu ta fara ƙoƙarin tashin ta tana kuka, Abdusammad ya yi jim sai kuma ya ɗauketa ya fice daga parlourn da sauri. Da gudu Zahra ta biyo bayansu, Ta tarar har ya shiga back seat tabi bayansu da sauri.
****
Amma ta toshe hancinta saboda ƙaurin da taji, Ta ƙarasa gaban gas ɗin dakyar ta buɗe tukunyar. Gaba ɗaya shinkafar ta yi baƙi ta babbake, Sai ƙauri ke tashi, ta kashe gas ɗin sannan ta juya ta fice daga kitchen ɗin rai ɓace tana kiran sunan Nana..
A parlour ta sameta tana baccinta hankali kwance, Amma ta kai mata duka tana kiran sunanta a fusace. Buɗe idanu Nana ta yi ta dinga kallon Amma sai kuma ta tashi zaune tana mitsitsika idanu, Amma da ranta yake a ɓace ta ce
“wani sabon iskancin ne ya sanya ki ka bar min abinci ya babbake? Meke damunki Nana?”
Saurin rufe bakinta ta yi da hannunta sai kuma ta tashi tsaye tana ɗaukan hular ta ta ce“Wallahi bacci ne ya ɗaukeni Amma..” ta nufi kitchen ɗin da sauri, Tana shiga ta samu Amma ta kashe gas ɗin, Ta buɗe tunkuyar sai kuma ta yi saurin rufe bakinta tari na tawo mata. Rufewa ta yi ta juya ta fice daga ɗakin, A tsaye ta samu Amma inda ta bar ta, Ta dinga kallon ta ganin irin yanda ta haɗe rai, Jiki a sanyaye ta ce
“Ki yi haƙuri Amma, wallahi....”
Dakatar da ita Amma ta yi ta hanyar ɗaga mata hannu, Rai ɓace ta fara cewa
“Wato ke ba zaki taɓa hankali ba? Ba zaki nutsu ba? Mene ne amfanin auren da ki ka yi? Haka ki ke a gidan mijin ma kina bari ana zagina. Ace common white rice ba zaki iya dafawa a nutse ba? Uban ki ki ke yi?”
Girgiza kai Nana ta yi jiki a sanyaye ta ce
“Dan Allah Amma ki yi haƙuri, baccin ne ya ɗaukeni ban sani ba.”
“Ai dole bacci ya ɗauke ki! Dole mana! Tun da baki san abin da ki ke ba. To na rantse duk ranar da ki ka sake yimin irin wannan abun sai ran ki ya yi mummunan ɓaci, Kuma ki sani daga yau har ranar da zaki bar garin nan ke ce zaki dinga girka abinci, Ke zaki dinga aiki, duk wani abu da ki ka san ana yi a gida kece zaki dinga yin sa. Idan kin so ki ci gaba da ba dai-dai ba!”
Amma ta ƙare maganar tana harararta, Sai kuma taja tsaki ta bar wajen, Ita dai Nana bata iya ko motsi ba, Dan ta san halin faɗan Ammar. Sai da taga ta shige daƙinta sannan ta ƙarasa kan kujera ta zauna, Ko minti biyu kuma bata yi ba ta kwanta wani baccin ya sake ɗauketa..
****
Tun da aka shiga da ita yake kai komo a wajen, Zahra kuwa sai kuka take ta ɗora hannunta aka. Kusan 30mins kafin Sultan ya buɗe ƙofar ɗakin ya fito, Da Sauri Abdusammad ya ƙarasa gabansa muryarsa a dake ya ce
“Ya jikin nata? What happened to her?”
Kallon sa Sultan ya dinga yi, ya kasa cewa komai. Abdusammad ya ɗan kanƙance idanunsa kafin ya ce
“Sultan mene haka? Do i look like ur mate?”
Girgiza masa kai ya yi, Abdusammad ya kalle shi sai kuma ya sanya hannu ya hankaɗeshi daga wajen ya buɗe ƙofar ɗakin ya shige. Zahra na ganin haka tabi bayansa da sauri, Sultan ya sauke wani zazzafan numfashi hawaye na biyo idanun sa.
Kwance Abdusammad ya sameta, Sai dai ya kasa gane dalilin daya sanya suka rufeta har fuska, Ya ƙarasa gaban gadon ya zauna ya buɗeta. Fuskarta fresh kamar wadda ke murmushi, asalin kamarta dashi ya sake bayyana, Ya kai hannunsa ya taɓa ta a sanyaye ya ce
“sorry ƴar gidan Abbie, zaki samu sauƙi.”
Zahra dake tsaye ɗan nesa dashi ta kalleta jin abin da ya ce. Ta sauke ajiyar zuciya tana dafe ƙirjinta, Sultan ne ya shigo ya tsaya a ɗaya side ɗin gadon yana kallon su, Ganin yanda yake ta nanata zata samu sauƙi. Sun daɗe a haka kafin Abdusammad ya mai da bargon ya rufeta amma ban da fuskarta, Ya tashi tsaye yana kallon Sultan ya ce
“Me ya sameta?”
Kallon sa kawai Sultan ya yi idanunsa cike taf da hawaye. Abdusammad ya girgiza kansa rai ɓace ya ce
“Sultan yaushe ne na fara wasa da kai?”
Jiki a sanyaye ya girgiza kansa yana ƙoƙarin ɓoye damuwarsa ya ce
“Yi haƙuri Yaya. But we lost her!”
Tamkar mafarki, ko kuma almara haka Abdusammad yaji kalaman Sultan na ƙarshe. Ya ɗan ware idanun sa yana son fahimtar abin da ya ce, Sultan ya sake Girgiza kansa wannan karon hawaye na zubowa kan fuskarsa ya ce
“Yaya a ina Noor ta samu guba? Wane ya bawa Noor abinci? A ina ta samu guba!"
Wani irin ihu Zahra ta saki sai gata a ƙasa Sumammiya, Abdusammad da ya kasa koda motsi daga inda yake ya sunkuyar da kansa sai sauke ajiyar zuciya yake akai akai. Da sauri Sultan ya nufi inda Zahra take yana kallon ta, Sai kuma ya fice daga ɗakin da sauri, Not too long suka dawo tare da wasu nurses mata guda uku, Akan wheelchair suka ɗorata suka fita daga ɗakin. Har sannan Abdusammad bai motsa daga inda yake ba, Gumi ne kawai ke tsatsafo masa duk da acn dake wajen, Zuciyarsa ta kasa yarda da abin da Sultan yake, Tunanin sa ya tsaya cak, ƙwaƙwalwarsa ta toshe. Yana nan tsaye har after 15mins Sultan ya dawo, Ya dinga kallon sa cike da tausayawa, Ya san ba lallai a fahimci halin da yake ciki ba, domin kuka ko magana baya ɗaya daga cikin abin da yake yi yayin da baƙin ciki ya yi masa yawa. Sultan ya sauke numfashi ya ƙarasa inda Noor take ya rufe mata fuskarta, Yana ƙoƙarin ɗagowa yaji Abdusammad ya riƙe hannunsa gam, Cikin wata irin kakkausar murya ya ce
“Don't ever try that!”
Sultan bai ce komai ba ya janye jikinsa ya bar ɗakin, Abdusammad ya zauna gefen gadon ya ɗaukota ya ɗora a jikinsa, Ya sanya hannunsa ya tallafi fuskarta muryarsa a sanyaye ya fara cewa
“Noorie! Noorien Abbie, Kina jina ko? Kina ji ko? Ai ƙarya suke yi na sani, babu abin da ya same ki, kina nan tare da Abbie, Ba zaki bar ni ba na sani. I know!”
Bata bashi amsa ba, Domin bata jin abin da yake cewa, ruhin ta ya yi ƙaura daga gangar jikinta, Jin bata ce komai ba ya sanya shi girgiza kansa yana ɗan murmushi ya ce
“Fushi ki ke yi da Abbie? Ki yi haƙuri kin ji. Next time zan kawo ki asibiti da wuri, But...!”
Sai ya sami kansa da yin shiru, Ya zubawa kyakkyawar fuskarta ido yana kallon ta, ba zaka taɓa cewa bata raye ba, Kamar bacci take..irin baccin data saba yi da yamma ta tashi bayan magriba, Wani lokacin kuma idan ta yi baccin shikenan sai gobe. Yana nan zaune sama da mintina ashirin bai sani ba, Shi kansa bai san a wane hali yake ba. Idanunsa dai har sannan na kan fuskarta, Buɗe kofar ɗakin aka yi, Ya daga idanunsa yana kallon su. Abba ne ya shigo sai Aliyu a bayansa, Ya yi saurin cewa
“Yauwa Abba zo kaji wai Noor ce taci guba? A ina Noor ta samu guba?”
Girgiza kai Abba ya yi ya janye Noor daga hannunsa ya miƙawa Aliyu, Abdusammad zai yi magana Abba ya kama hannunsa a sanyaye ya ce
“Muje gida tukun”
“But Abba ai bata ji sauki ba, Ya za'a yi mu tafi gida da ita a haka? At least ta samu lafiya”