Sashe 57
LUu Luu Part 3 Complete Hausa Novel · about 8 min read
Ba wanda bai shigo ya mata sannu ba.......ba wanda bai nuna kulawarsa a kanta ba,amma sai takejin wannan kulawar da komai ma sunyi mata kadan. Abinda take gani saman fuskokinsu ke sake daga hankalinta. Kowaccensu daidai da noorah auta cikin walwalarsu suke,walwalat data tabbatar tana da nasaba da isowar matar captain obbo,ta sake tabbatar da hakan kuma sanda ta fito daukan ruwa mara sanyi babban parlour din,ta samesu dukkansu wasu saman sofas wasu zaune a qasa suna sake tattauna maganarta da gagarumar walimar da zasu shirya ranar data fito daga gidan koyon rayuwa da al'adun masarauta.
Da qyar ta maida kanta daki,bata kuma sake fitowa daukan ruwan ba sai a yanzu. A daddafe take takawa saboda matsanancin ciwon da kanta yake mata,gabanta ya yanke ya fadi sanda hancinta ya fara jiyo mata wannan qamshin.
Shi kadai yake da irin wannan qamshin a duk fadin duniya cikin mutanen data sani......cikin mutanen da take mu'amala dasu. Qamshinsa na dabanne,don haka wanzuwarsa a guri ma ta zama ta daban,kamar yadda koda ya iso guri komai nasa yake banbanta dana kowa. Zataso qafafunta su bata hadin kai tayi gaggawar barin gurin kafin ya iso,amma zuciyarta ta jefawa qafafunta umarnin da har ya iso gurin ta kasa tabuka komai.
Bai lura da ita ba,har sai daya kusa shiga dan walkway din da zai sake sadashi da sassan nanay mafi kusanci.
"Barka da dare" Ta fada a hankali tana fatan idanunsa yakai kanta tana rusunar da qwayar idanunta qasa.
"Yauwa......ya jikin?" Ya fada a tausashe yana dauke idonsa daya sauke a kanta zuwa gabansa.
"Alhamdulillah" Sai ya gyada kansa a nutse ya soma takawa zuwa gaba.
"Allah ya bada lafiya" Ya fadi a nutse yana sake yin nisa da inda take tsaye.
"Ameen" Ta amsa can qasa muryarta tana rawa,tana jin yadda yake qulewa,tana jin yadda yakeyin nisa da inda take tsaye. Duk takunsa saya ruwan hawaye yake saukar mata. Iya abinda zai iyayi kenan?. Me yasa kaman damuwa da lamarinta da kulawar da a baya yake d'an nuna mata sukayi qasa sosai?,me yasa suka ragu fiye da kafin tafiyarsa?.
Me yasa bazai karanci damuwarta ba kaman yadda ya saba karantar damuwar 'yan uwansa dama kowa daya damu dashi?,me yasa bazai kalli cikin idanunta ya karanto abinda ke danqare a kansa a zuciyarta ba?. Zuciyarta tayi wani irin rauni,ruwan gorar data dauko ya fara mata nauyi a hannu,ta riqeshi sosai cikin hannun nata,ta daga qafa zata fara takawa maganansa ya mata bazatar data saki ruwan a qasa.
"Ko akwai wani ciwon da kikeji?,idan akwai ki fadawa nanay,koda asibiti ne sai a sake da tests ko?" Ya fada da kulawa. Qasa tayi da kanta tana kasa hada idanu dashi,sannan ta daga kanta a hankai.
"Da sauqi.....ina samun sauqi" Kai ya jinjina yana sake komawa hanyar walkway din
"Ma sha Allah,haka akeso". Tana sake jin yana mata nisa....har zuwa sanda qamshin turarensa ne kawai ya rage a gurin banda wannan gangar jikin da wannan kyakkyawan ruhin da take mafarkin mallaka. Tsugunnawa tayi tana laluben ruwanta daya fadi,saboda hawayen da suka cika mata idanu sun hanata ganinsa,ta aza hannunta akai ta dauka ta miqe da sauri sauri tana wucewa ciki.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 52
Kuka sosai ta fashe dashi tana qoqarin boye kukanta don kada Aanaani dake zaune tana amsa waya ta jita. Ta lura daidai da kallo ma ba kai tsaye yake kallonta ba. Haka yake kallonsa akan kowacce diya mace yana qoqarin kauda idanunsa a kanki.....amma me yasa sai a yanzun haka yafi zafafarta?. Ta tabbatar ba irin wannan kallon yakewa matarsa ba......bama irin wannan kallon ya mata ba har yaja ra'ayinsa a kanta ba. Me yasa bazai.kalleta da dukkanin idanunsa ba kamar yadda ya kalli matarsa?. Ta tabbatar tana da dukkan wata siffa hali da dabi'a da yakeso game da d'iya mace......ta tabbatar indai zai kalleta yau gobe zuwa jibi.....lallai wataran zata samu kyakkyawan gurbi da muhalli a ransa. Ta sanshi ta karanci dukkan wata dabi'a tasa,tasan abinda yakeso tun daga kan sutura yanayin turare abinci da yanayi(weather)na gari dana muhalli,tayi kuma amfani da dukkan wannan ta fara samar da magana me dan tsaho a tsakaninsu,koda kuwa akan karatu ne amma taci wannan galabar. Ba irin farkon zuwanta ba.....ba kamar a baya ba da daga nesa kurum take hangensa......me zai sanya ta tsaya a iya haka?.
"Wacece ita?" Ta samu kanta da tambayar kanta bayan dogon tunanin data gama. A kaf dabi'arsa ta gama gane baya wani ra'ayin mu'amala da mata,baya zurfafa kallo a kansu,wannan ya bata relief na cewa itace kawai zatayi nasarar shiga rayuwarsa. Ta yaya wannan din ta shiga rayuwarsa?,wacece ita?,dame ta fita?,dame take taqama?. Wadannan tambayoyin gaba daya suka kwadaita mata son gani da sanin WACECE AKHNAN.
Duk da tana fargaba,zuciyarta kuma tana gaya mata koma wacece zata samu nasarar mallakar sheikh muhammad din tako ina ta cika mace tabbas......to amma kuma tana fata duk cikar da tayi ita ta fita ta kowacce fuska.
Tsam nanay ta miqe sanda yake shigowa dakin,fuskarta shimfide da murmushin nan da yake sake nuna dattakonta da tarin nutsuwar da yaranta suka gada daga gareta.
Shima nasa idanun suna kanta,yana dubanta da wani kalan tarin qauna da soyayya da tausayi na jiran wasu mutane data dinga yi a rayuwarta na tsahon shekaru ba tare da tana da tabbaci akan komai daya shafesu ba. Ya lumshe idanunsa yana kama hannayenta,yana jin wani irin sassauci da sanyi a ransa a duk sanda ya tuna cewa shine zai zama silar yankewar wannan jiran.....shine zai kusantata da nesanta.....shine zai zame mata tsani na sake rayuwa da mutanen da sukafi soyuwa a ranta.
"Zauna nanay" Ya fada yana zaunar da ita saman lallausan tuntum dake zube kan kilishin dake dakin. Bata musa masa ba,ta zauna shima ya dawo gabanta ya zauna saman qafafunsa yana dubanta.
"Na dauka kin gaji da jira kin kwanta". Murmushi tayi ta girgiza kai.
"Nace zan jiraka muhammad,munyi kewarka sosai.....zanso ace a yanzun haka a irin wannan yanayin surukata tana gefena kamar yadda kake zaune a gabana.....amma al'ada tayi mana wannan shamakin" Ta fada tana murmushi. Yau kawai sai yaji kunyar nanay ta kamashi,yadan sauke kansa qasa. Wai shine da mace?,shine ya auri wata macen?.
"Yaya take Muhammad.....gayamin" Da mamaki kadan a fuskarsa ya daga kai yana duban nanay din. Idanunta basu qaryata abinda ya fita yanzu a bakinta ba. Da gaske take tanason ganinta,wacce irin qauna ce wannan?,tun kafin tasan wadda ya kawo mata a matsayin suruka?,tun kafin taga wacece?. Babban abun,a duk lokaci itin wannan da zai dawo daga tafiya ba wanda Nanay takeji ko ta gani saishi,amma a yau maimakon zallar kulawar nan a kansa shi kadai ta soma rabata da wata?. Tun a ranar farko?.
"Lafiya alhamdulillah nanay" Kai ta gyada a hankali.
"Nace da hasnaaa ta bani ita a dazun muyi magana saita manta.....fatana daya ta kasance me fikira kamar yadda mijinta yake,ta kammala karbar horo cikin qananun kwanaki don ta iso cikin ahali" Qasa yayi da kansa kadan yana murmushi,shi duka ba wannan ba.....izzarta Allah yasa ta barta tayi abinda ya dace,yana fatan izzarta ta barta ta ajiye komai na agadez ta shiga practicing al'adu da dabi'un fada da masarautar aba jifar.
"In sha Allah nanay" Ya fada yana zama sosai wannan karon.
Hira suka shiga yi a tsakaninsu,irin hirar yaushe gamo. Hirar da take kama da hirar masoyan da sukayi nesa da juna. Abubuwa masu yawa suka tattauna,basa ma ko kallon abincin da tasa aka shirya kala kala daga nau'ikan abinciccikan alfarma na al'adarsu da tasan yafiso.
Ya bata labarai kala kala na yadda komai yazo masa. Zuciyarta ta karaya,tayi laushi sosai. Aikinsa a kullum rana tsoro yake sanyata na wanne irin qalubale wataran zai hadu dashi?,amma bata taba yarda ta nuna masa ba. Saboda ta sani,daga ranar daya fahimci abinda yake daga mata hankali,tayi imanin ya ajiye aikin kenan bazai sake waiwayarsa ba duk da yadda yakai ga son aikin. Bata burin ta zama sila ko sanadin hanashi wani jin dadi ko cikar buri na rayuwarsa.
Abu daya da take nacewa Allah akai wajen roqa masa shine MACE TA GARI. wadda zata zame masa sanyin idaniya.....wadda zata debe dukkan wani fargaba damuwa da hadari na cikin aikinsa......wadda zata bashi AMINCI ta kuma bashi NUTSUWA. Wadda zata soshi kaman yadda takeson kanta. Wadda zata tare kasa cutarwa.....wadda ba zata bari ya cutu ba tako ina.....uwa uba wadda zata iya dauke dukkan nauyinsa da lalurarsa ta d'a namiji......ta bashi abinda ya kauda kai daga bid'arsa duk da tarin buqatarsa akai.....yayi haquri ya jira halal dinsa.
"Nanay" Ya kirata da girmamawa bayan sun kammala cin abincin da ita ta dinga zuba masa har sai daya qoshi.
"Sheikh muhammad" Ta fadi da murmushi. Yakanyi murmushi a duk sanda ta kirashi irin hakan,sai yaji sunan kaman yafi dadi a bakinta.
"A duniya.....wanne buri ne kike fatan cikarsa kafin ki koma ga mahaliccinki?". Tayi shuru tambayar tana ratsawa cikin kanta. Tana da wasu burika na daban......amma ta sani inde ta riga muhammad rasuwa to zai iya cika mata su,koda bata gani da idanuwanta ba,amma a yanzun burin da take dashi shine taga 'yan uwanta.
"Muhammad......burina bana jin me cika ne" Ta fada a raunane. Matsawa gabanta yayi sosai,ya kama hannuwanta ya riqe cikin nasa.
"Kija numfashi sosai nanay,ki fadi duk wani burinki,a gaban muhammad dinki kike" Murmushi ya subuce mata dake hade da ruwan hawayen da baikai ga zuba mata ba.
"Na sani.....wannan jan gwarzon namijin,zakin d'ana" Maganan ya sashi qaramar dariya,duk da ba yau ya fara jin ta fadi haka a kanshi ba,amma murmushinta kawai ya sanya wani farinciki a zuciyarsa.
"Burina naga safiyya da safeena,duk da nasan zai wahala rayuwa ta bamu wannan damar" Ta fadi cikin alamun karaya da yanke tsammani.
Da qyar ta maida kanta daki,bata kuma sake fitowa daukan ruwan ba sai a yanzu. A daddafe take takawa saboda matsanancin ciwon da kanta yake mata,gabanta ya yanke ya fadi sanda hancinta ya fara jiyo mata wannan qamshin.
Shi kadai yake da irin wannan qamshin a duk fadin duniya cikin mutanen data sani......cikin mutanen da take mu'amala dasu. Qamshinsa na dabanne,don haka wanzuwarsa a guri ma ta zama ta daban,kamar yadda koda ya iso guri komai nasa yake banbanta dana kowa. Zataso qafafunta su bata hadin kai tayi gaggawar barin gurin kafin ya iso,amma zuciyarta ta jefawa qafafunta umarnin da har ya iso gurin ta kasa tabuka komai.
Bai lura da ita ba,har sai daya kusa shiga dan walkway din da zai sake sadashi da sassan nanay mafi kusanci.
"Barka da dare" Ta fada a hankali tana fatan idanunsa yakai kanta tana rusunar da qwayar idanunta qasa.
"Yauwa......ya jikin?" Ya fada a tausashe yana dauke idonsa daya sauke a kanta zuwa gabansa.
"Alhamdulillah" Sai ya gyada kansa a nutse ya soma takawa zuwa gaba.
"Allah ya bada lafiya" Ya fadi a nutse yana sake yin nisa da inda take tsaye.
"Ameen" Ta amsa can qasa muryarta tana rawa,tana jin yadda yake qulewa,tana jin yadda yakeyin nisa da inda take tsaye. Duk takunsa saya ruwan hawaye yake saukar mata. Iya abinda zai iyayi kenan?. Me yasa kaman damuwa da lamarinta da kulawar da a baya yake d'an nuna mata sukayi qasa sosai?,me yasa suka ragu fiye da kafin tafiyarsa?.
Me yasa bazai karanci damuwarta ba kaman yadda ya saba karantar damuwar 'yan uwansa dama kowa daya damu dashi?,me yasa bazai kalli cikin idanunta ya karanto abinda ke danqare a kansa a zuciyarta ba?. Zuciyarta tayi wani irin rauni,ruwan gorar data dauko ya fara mata nauyi a hannu,ta riqeshi sosai cikin hannun nata,ta daga qafa zata fara takawa maganansa ya mata bazatar data saki ruwan a qasa.
"Ko akwai wani ciwon da kikeji?,idan akwai ki fadawa nanay,koda asibiti ne sai a sake da tests ko?" Ya fada da kulawa. Qasa tayi da kanta tana kasa hada idanu dashi,sannan ta daga kanta a hankai.
"Da sauqi.....ina samun sauqi" Kai ya jinjina yana sake komawa hanyar walkway din
"Ma sha Allah,haka akeso". Tana sake jin yana mata nisa....har zuwa sanda qamshin turarensa ne kawai ya rage a gurin banda wannan gangar jikin da wannan kyakkyawan ruhin da take mafarkin mallaka. Tsugunnawa tayi tana laluben ruwanta daya fadi,saboda hawayen da suka cika mata idanu sun hanata ganinsa,ta aza hannunta akai ta dauka ta miqe da sauri sauri tana wucewa ciki.
*zaki samu daman karanta wannan QASAITACCEN LABARIN ta hanyoyin siyan tikitinki kamar haka da naira (1000) kacal*
*Lambar asusu:- 6019473875*
*Safiya musa abdullahi*
*Keystone bank*
*KI TURA SHAIDAR BIYA TA NAN*
08187255862
*Al'ummar qasar nijer 🇳🇪*
*2349166221261*
*Safiya musa abdullahi*
*NITA*
*CFA 1,000*
*SAIKU TURA SHAIDAR BIYA TA LAMBAR DAI*
08187255862
*GA WADANDA ZASU SAKA KATIN WAYA NA MTN SUMA NUMBER DUKA DAYA CE*
*MTN CREDIT 1000 ZUWA GA*
09166221261
*SHAIDAR BIYA*
08187255862
*_TAFIYAR 'YAR GASKE CE........LABARIN QASAITACCIYAR MACE CE KAWAI KE IYA SIYANSA_*
*QASAITA👑*
*HUGUMANKU CE*✍🏽💎 *L U'U L U'U*
*_(The diamond)_*💎
*H U G U M A*
*BOOK 03///PAGE 52
Kuka sosai ta fashe dashi tana qoqarin boye kukanta don kada Aanaani dake zaune tana amsa waya ta jita. Ta lura daidai da kallo ma ba kai tsaye yake kallonta ba. Haka yake kallonsa akan kowacce diya mace yana qoqarin kauda idanunsa a kanki.....amma me yasa sai a yanzun haka yafi zafafarta?. Ta tabbatar ba irin wannan kallon yakewa matarsa ba......bama irin wannan kallon ya mata ba har yaja ra'ayinsa a kanta ba. Me yasa bazai.kalleta da dukkanin idanunsa ba kamar yadda ya kalli matarsa?. Ta tabbatar tana da dukkan wata siffa hali da dabi'a da yakeso game da d'iya mace......ta tabbatar indai zai kalleta yau gobe zuwa jibi.....lallai wataran zata samu kyakkyawan gurbi da muhalli a ransa. Ta sanshi ta karanci dukkan wata dabi'a tasa,tasan abinda yakeso tun daga kan sutura yanayin turare abinci da yanayi(weather)na gari dana muhalli,tayi kuma amfani da dukkan wannan ta fara samar da magana me dan tsaho a tsakaninsu,koda kuwa akan karatu ne amma taci wannan galabar. Ba irin farkon zuwanta ba.....ba kamar a baya ba da daga nesa kurum take hangensa......me zai sanya ta tsaya a iya haka?.
"Wacece ita?" Ta samu kanta da tambayar kanta bayan dogon tunanin data gama. A kaf dabi'arsa ta gama gane baya wani ra'ayin mu'amala da mata,baya zurfafa kallo a kansu,wannan ya bata relief na cewa itace kawai zatayi nasarar shiga rayuwarsa. Ta yaya wannan din ta shiga rayuwarsa?,wacece ita?,dame ta fita?,dame take taqama?. Wadannan tambayoyin gaba daya suka kwadaita mata son gani da sanin WACECE AKHNAN.
Duk da tana fargaba,zuciyarta kuma tana gaya mata koma wacece zata samu nasarar mallakar sheikh muhammad din tako ina ta cika mace tabbas......to amma kuma tana fata duk cikar da tayi ita ta fita ta kowacce fuska.
Tsam nanay ta miqe sanda yake shigowa dakin,fuskarta shimfide da murmushin nan da yake sake nuna dattakonta da tarin nutsuwar da yaranta suka gada daga gareta.
Shima nasa idanun suna kanta,yana dubanta da wani kalan tarin qauna da soyayya da tausayi na jiran wasu mutane data dinga yi a rayuwarta na tsahon shekaru ba tare da tana da tabbaci akan komai daya shafesu ba. Ya lumshe idanunsa yana kama hannayenta,yana jin wani irin sassauci da sanyi a ransa a duk sanda ya tuna cewa shine zai zama silar yankewar wannan jiran.....shine zai kusantata da nesanta.....shine zai zame mata tsani na sake rayuwa da mutanen da sukafi soyuwa a ranta.
"Zauna nanay" Ya fada yana zaunar da ita saman lallausan tuntum dake zube kan kilishin dake dakin. Bata musa masa ba,ta zauna shima ya dawo gabanta ya zauna saman qafafunsa yana dubanta.
"Na dauka kin gaji da jira kin kwanta". Murmushi tayi ta girgiza kai.
"Nace zan jiraka muhammad,munyi kewarka sosai.....zanso ace a yanzun haka a irin wannan yanayin surukata tana gefena kamar yadda kake zaune a gabana.....amma al'ada tayi mana wannan shamakin" Ta fada tana murmushi. Yau kawai sai yaji kunyar nanay ta kamashi,yadan sauke kansa qasa. Wai shine da mace?,shine ya auri wata macen?.
"Yaya take Muhammad.....gayamin" Da mamaki kadan a fuskarsa ya daga kai yana duban nanay din. Idanunta basu qaryata abinda ya fita yanzu a bakinta ba. Da gaske take tanason ganinta,wacce irin qauna ce wannan?,tun kafin tasan wadda ya kawo mata a matsayin suruka?,tun kafin taga wacece?. Babban abun,a duk lokaci itin wannan da zai dawo daga tafiya ba wanda Nanay takeji ko ta gani saishi,amma a yau maimakon zallar kulawar nan a kansa shi kadai ta soma rabata da wata?. Tun a ranar farko?.
"Lafiya alhamdulillah nanay" Kai ta gyada a hankali.
"Nace da hasnaaa ta bani ita a dazun muyi magana saita manta.....fatana daya ta kasance me fikira kamar yadda mijinta yake,ta kammala karbar horo cikin qananun kwanaki don ta iso cikin ahali" Qasa yayi da kansa kadan yana murmushi,shi duka ba wannan ba.....izzarta Allah yasa ta barta tayi abinda ya dace,yana fatan izzarta ta barta ta ajiye komai na agadez ta shiga practicing al'adu da dabi'un fada da masarautar aba jifar.
"In sha Allah nanay" Ya fada yana zama sosai wannan karon.
Hira suka shiga yi a tsakaninsu,irin hirar yaushe gamo. Hirar da take kama da hirar masoyan da sukayi nesa da juna. Abubuwa masu yawa suka tattauna,basa ma ko kallon abincin da tasa aka shirya kala kala daga nau'ikan abinciccikan alfarma na al'adarsu da tasan yafiso.
Ya bata labarai kala kala na yadda komai yazo masa. Zuciyarta ta karaya,tayi laushi sosai. Aikinsa a kullum rana tsoro yake sanyata na wanne irin qalubale wataran zai hadu dashi?,amma bata taba yarda ta nuna masa ba. Saboda ta sani,daga ranar daya fahimci abinda yake daga mata hankali,tayi imanin ya ajiye aikin kenan bazai sake waiwayarsa ba duk da yadda yakai ga son aikin. Bata burin ta zama sila ko sanadin hanashi wani jin dadi ko cikar buri na rayuwarsa.
Abu daya da take nacewa Allah akai wajen roqa masa shine MACE TA GARI. wadda zata zame masa sanyin idaniya.....wadda zata debe dukkan wani fargaba damuwa da hadari na cikin aikinsa......wadda zata bashi AMINCI ta kuma bashi NUTSUWA. Wadda zata soshi kaman yadda takeson kanta. Wadda zata tare kasa cutarwa.....wadda ba zata bari ya cutu ba tako ina.....uwa uba wadda zata iya dauke dukkan nauyinsa da lalurarsa ta d'a namiji......ta bashi abinda ya kauda kai daga bid'arsa duk da tarin buqatarsa akai.....yayi haquri ya jira halal dinsa.
"Nanay" Ya kirata da girmamawa bayan sun kammala cin abincin da ita ta dinga zuba masa har sai daya qoshi.
"Sheikh muhammad" Ta fadi da murmushi. Yakanyi murmushi a duk sanda ta kirashi irin hakan,sai yaji sunan kaman yafi dadi a bakinta.
"A duniya.....wanne buri ne kike fatan cikarsa kafin ki koma ga mahaliccinki?". Tayi shuru tambayar tana ratsawa cikin kanta. Tana da wasu burika na daban......amma ta sani inde ta riga muhammad rasuwa to zai iya cika mata su,koda bata gani da idanuwanta ba,amma a yanzun burin da take dashi shine taga 'yan uwanta.
"Muhammad......burina bana jin me cika ne" Ta fada a raunane. Matsawa gabanta yayi sosai,ya kama hannuwanta ya riqe cikin nasa.
"Kija numfashi sosai nanay,ki fadi duk wani burinki,a gaban muhammad dinki kike" Murmushi ya subuce mata dake hade da ruwan hawayen da baikai ga zuba mata ba.
"Na sani.....wannan jan gwarzon namijin,zakin d'ana" Maganan ya sashi qaramar dariya,duk da ba yau ya fara jin ta fadi haka a kanshi ba,amma murmushinta kawai ya sanya wani farinciki a zuciyarsa.
"Burina naga safiyya da safeena,duk da nasan zai wahala rayuwa ta bamu wannan damar" Ta fadi cikin alamun karaya da yanke tsammani.